Rayuwa Da Gibi – Chapter Ten
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Irin kukan da Iyaa tayi bayan jin tsiyar da Ummi take shukawa dole ya bawa mutum tausayi. Bayan an kai ruwa rana a station ɗin da su ka je Baba Maje ya gane duk inda yake tunanin Ummi ta wuce nan. Fitina da gagara ta ƴan matanci kam tana bugawa a bayan idonsa. Ya sake yarda ba a shaidar ɗan yau. Ba don da bakinta ta amsa laifukanta ba da ya yi rantsuwar sharri ake yi mata. Ummin da ya sani daban. Wadda ya dawo da ita gida daban.
Abin baƙinciki shaiɗanin tsohon najadun da yafi kowa hure mata kunne Uncle B ashe makanike ne. Matansa biyu da ƴaƴa goma sha uku. Sau ɗaya ake ɗora tukunya a gidansa. Irinsu Ummi ke cinye ɗan abin da yake samu. Ita da yake tunanin raba hanya da ita saboda rashin bashi haɗin kai tuntuni ashe silarta asirinsa zai tono. Sai da ya yi sati guda a ƙulle kafin a yarda a bada belinsa. Shi ma kuma an haɗa masa da muguwar tarar da zai ji jiki wajen biya.
Hantara da kyara su suka marabceta daga dawowarta gida. Ta zama mujiyar da bahaushe yake kira mai baƙin jini. Iyayenta ba su dake ta ba don ciwon abin da tayi ya kai maƙura. Yayanta Baballe ne dai ya kasa zama bayan yaji kukan Iyaa yayi yawa a waya da tana labarta masa. Ya niƙi gari ya taho Kano ya sakar mata ƙarfinsa. Zaneta ya yi ciki da bai babu wanda ya hana shi. Sai ma dare da jikinta ya yi mugun tsami ne Iyaa ta tada ta zaune.
“Sau nawa ki ka zubar da ciki Ummi?”
Duk soyewar zuciyarta da ya hanata kukan dukan da ta sha wannan tambaya sai da tayi sanadin zubar hawayenta. Hannu ta ɗora akan bakinta tana danne kukan.
“Iyaa? Ciki kuma?”
“To Ummi meye abin mamaki a ciki? Samarin da su ke kashe miki kuɗi ƙannen uwa ne ko na uba da za a ce zumunci suke yiwa?”
Hawaye take ita ma ga tsoron kada Ummin ta amsa zargin da su ke yi mata ita da Baba Maje.
“Wallahi Iyaa ban taɓa yarda na bada kaina ba.”
“To me ki ke basu ko me su ke samu a madadin kuɗinsu? Don dai bana jin shaiɗancin naki ya yi tsamarin da za ki asircesu su dinga bin umarninki.”
Shiru Ummi tayi. Hankalin Iyaa ya sake tashi ta dinga kai mata duka da hannu ta ko ina.
“Ki faɗa min gaskiya kafin zuciyata ta buga.”
“Iyakarsu tattaɓani amma bana yarda da…”
Da sauri Iyaa ta tashi don bata son kuma jin ƙarshen zancen.
“Ya isa. Kin yiwa kanki.”
Fita tayi ta bar Ummi tana kuka. Kuma duk wannan abu bai zama ishara ya tuna mata yadda ta dinga cin zarafin mutane dole rana irin ta yau ta zo ba. Sunan Hamdi kawai ke yawo a zuciyarta. Ko harararta aka yi laifinta take ƙara gani. Musguna mata da ta dinga yi a makaranta ai bai shafi komai na karatunta ko rayuwarta ba a tunaninta. She was just having fun. Ba ita kaɗai bace senior mai yi wa na ƙasa da ita hawan karkatacciyar kuka, saboda haka bata ga dalilin da zai sa ita kaɗai ce rayuwarta ta kife irin haka ba. Da me ake so ta ji? Sanin waye Uncle B ko fitowar sirrinta? Ko kuwa rabata da makaranta a matakin ƙarshe da iyayenta su ka yi don ta ɗauki bidiyon ɗan daudu?
“Wallahi sai na rama Hamdiyya. Babu wanda ya isa ya saka ni kuka ban saka shi ba.”
Da wannan kalaman ta goge hawayenta a fusace ta kwanta tana shure Siyama da ƙafa don ta ɗan matso ɓangarenta cikin bacci.
***
Kwanaki sun ja inda a farko farkon watan August ɗaliban sakandire su ka kammala jarabawar fita. An yi WAEC har ta fito kafin a gama NECO. Da taimakon Allah da kuma dagewar karatu Hamdi ta sami kyakkyawan sakamako.
Kwana biyu bayan kammala jarabawar makaranta ta shirya gagarumin taron sallamar ɗalibai. Iyaye da ɗaliban suna shiryawa wannan rana wasu tun farkon shiga SS3. Ɗinkin ankon wata shuɗiyar atampa su ka yi mai adon fari da yellow. Tun kafin hutu aka fitar amma lokacin Hamdi bata ƙarɓi ƙyallen ba. Saboda ko kusa bata sa ran zuwa. Sai bayan faruwar lamarin nan taji a jikinta ta daina ɗararewa. Allah Ya taimaketa kafin a gama jarabawar lokacin visiting da Sajida da Zee su ka zo mata ta basu.
“Abba fa ya bar sana’arsa Hamdi. Ki haƙura kawai a kawo miki ko cikin kayan sallarki ne.” Zee ta faɗi bayan ta gama kallon atampar.
Mangareta Sajida tayi “Yaya bata gargaɗeki akan faɗa mata ba?”
“Gaskiya fa na faɗa mata don kada ta sa rai.” Zee ta bata amsa tana ƙunƙuni.
“Ya Sajida me yake faruwa? Ba don saboda ni ya daina ba?” Hamdi ta tambaya hankalinta na tashi.
Bayanin abin da ya faru su ka yi mata. Sannan Sajida ta ce kada ta damu in sha Allahu za a saya a ɗinka kafin ranar.
“Na haƙura.” Hamdi ta ce a sanyaye tana tuhumar kanta a matsayin wadda ta kasa godewa mahaifinta a lokacin da yake yi musu.
“Anti Labiba ce ta bani kuɗi da zan taho. Allah zan iya saya miki.” Sajidan ta bata amsa tana dariya.
Daga nan su ka koma wata caftar mai daɗi. Sajida tayi saurayi a Abuja daga zuwa taya cousin ɗinsu zaman jego. Mutumin da gaske yake. Yana aiki da rufin asirinsa. Ƴan maza zar su ke da mijin Anti Labiban (ƴa a wurin babbar yayar Abbansu Anti Zinatu).
Ƴan matan uku su ka haɗa kai su na ta murna kamar ma anyi auren an gama.
Zee ce ta dakatar da shewar tasu “Kin dai yi masa bayanin Abba ko?”
Fari Sajida tayi da idanu tana faɗaɗa murmushinta “Kada ku damu. Ya ce sai da su ka yi magana da mijin Anti kafin ma ya yi min magana. Yanzu dai ku sa rai da zuwansa nan da wata guda. Lokacin ma kin dawo gida ko?”
“Su Ya Sajida an fara kashe murya a waya kenan.” Hamdi ta tsokaneta.
“Zan ɗauko rahoto kafin ki dawo. Dama bata yi na gani ba don kada na fesawa Yaya.”
“Kin fa raina ni Zee. Ni da na raineki.”
Dariya Zee da Hamdi su ka yi. Ita Zee SS2 take don tsiransu da Hamdi babu yawa.
***
Aikin gini ya soma kankama son Taj ba ɓata lokaci ya zo yi ba. Shawarar Amma ya karɓa ya yi ginin a iya restaurant da shaguna ƙalilan. Wani Architect ya kwatantawa abin da yake so. Nan da nan aka zana masa plans kala uku. A ciki ya zaɓi ɗaya. Shi da Kamal kullum sai dare su ke komawa gida. Shi ya tafi gidan Ahmad, Kamal kuma ya koma don muddin ya kwana zai gamu da fushin Alhaji.
Tsarin da aka ɗauko ya bada ma’ana sosai. Gini ne da aka yi ɓangare uku manne da juna. Na tsakiyar yafi girma da faɗi kuma shi kaɗai ne aka ɗorawa bene. Na hagu anyi kitchen ƙato da komai domin aikin fulawa. Cake, doughnut, meatpie, samosa, pies da dangoginsu. A wadace yake sai dai babu wurin zama a ci a ciki. Idan mutum baya son fita akwai ƙofa da za ta sada shi da tsakiyar wato ainihin restaurant ɗin. Ɓangaren dama wanda shi dama za a fara tararwa shi kuma kana gani za ka san na masu gashin nama da kifi ne. Ko yanzu da ake matakin gini kaɗai kana gani zai burge ka. A tsakiyar sama gabaɗayansa kujeru da teburan zama ne. Sai wasu ɗakuna biyu domin masu gudanar da taron da zai iya cin mutane hamsin. Meeting, seminar, reunion da sauransu amma banda biki. Ɗakunan ɗaya normal ne ɗaya kuma VIP. A ƙasa ma da wurin cin abincin sai ɓangaren masu haɗa natural juice da za ayi bayan kayi order. Saii kuma makeken kitchen ɗin Taj da ma’aikatansa. Har ila yau a farfajiyar wajen an keɓe wani waje da aka soma tayar da garden. Za a ƙawata wajen da liluka da wajen guje guje da wasan yara. Sai kuma cikon alƙawarin da ya yiwa kansa. Zai gina madaidaicin boutique da gininsa zai kallon restaurant ɗin ya bawa Kamal amma bai faɗa masa ba.
Yau sun bar wurin duba aikin da wuri sakamakon zazzaɓi da ya rufarwa Taj gadan gadan. Kamar wasa ya ce kansa na ciwo, sai gashi kafin su isa gidan Ahmad yana rawar sanyi. Ɗauke hanya Kamal ya yi su na cikin tafiya. Taj ya ɗago kansa da ya yi nauyi da ƙyar ya dubi hanya.
“Sayar dani za ka yi don kaganni haka Happiness?”
Kamal ya yi murmushi “kwantar da hankalinka. Ai an taya kuma naji ba tsada za ka yi ba.”
“Ka ci bashi don sai na rama.”
“Allah Ya baka haƙuri. Yadda nake jin yunwa idan kayi fushi dani da alama Salwa ba za ta bani abinci ba yau.”
Wani irin kallo Taj ya yi masa na neman alaƙar fushinsa da cin abincin Kamal amma ya kasa ganewa.
“Wani abu ne ya haɗaka da ita?”
“No” Kamal ya bashi amsa mischieviously.
“Meaning?”
“A bar zancen sai ka warke.”
Taj bai matsa ba. Kansa kuɗa yake kamar zai cire. Asibiti Kamal ya kai shi duk turjiyarsa. Abu ya kai da ƙarin ruwa don likitan ya ce jikinsa babu kuzari. Gashi sakamakon gwaji ya nuna yana da malaria da thypoid duk shi kaɗai. Sun haɗe da rashin hutu sun kayar dashi lokaci guda.
“Amma ba kwana zan yi ba ko?”
Ya tambayi likitan bayan an gama saka masa canula a hannu.
“Ka godewa Allah da ka iya shigowa nan da ƙafafunka. Your temperature is abnormally high.”
Da Kamal ya barshi ya rufe ido don ya gaji sosai. Bayan fitar likitan da Alhaji yaji Kamal ɗin yana waya. Ya sanar dashi halin da yake ciki. Ƙaguwa ya yi yaji me Alhajin zai ce don kamar ya ƙwaci wayar a hannun Kamal. Ya dai daure har su ka gama. Shiru bai ji Kamal ya isar da saƙon Allah Ya ƙara sauƙi ba.
Sai da ya bari ya gama waya da su Inna da Ahmad sannan ya tambaye shi.
“Bai ce komai bane?”
“Yana hanya ne da alama ba ya ji na sosai” Ita ce kalmar da Kamal ya ƙirƙiro ya faɗa masa.
“Hmmm”
Kamal ya dawo kusa da shi “Happy kayi haƙuri sannan mu cigaba da addu’a.”
Abinka da ƴan dangi. Lokaci ƙanƙani asibitin ya fara cika da ƴan uwansu. Kowa ya zo faɗan rashin hutu yake yi masa.
*
Don son tabbatar da zarginsa, Kamal kiran Salwa ya yi ya faɗa mata bayan ya sanar da Ahmad. Tunda yaji ya ce baya gida shi ne ya kirata. Ai kuwa abin da ya yi tsammani yaji. Rikicewa tayi ba tare da ta sani ba.
“Ya Kamal yana iya magana?”
Ya yi murmushi “eh, ko in bashi ne?”
Da sauri ta ce “a’a” kunya na lulluɓeta da ta fahimci za ta bada kanta. Awa guda bayan sun yi wayar ta kasa sukuni. Jira take Zahra matar Ahmad tayi maganar zuwansu dubiya tunda tayi arba’in yanzu amma taji shiru. Bini-bini ta ɗaga waya ta duba lokaci. Da ta kai matakin da ba za ta iya haƙuri ba sai ta tambayi Zahran.
“Anti Zahra na ce ko sai Hayat ya taso in an kai shi islamiyya za mu wuce asibitin?”
Zahra ta zaro idanu tana laluben wayarta “ba ki da lafiya ne Salwa? Ina yake miki ciwo? Bari na faɗawa Daddy.”
“Ƙalau nake Anti. Dama maganar duba Yaya Taj ne.”
Zahra tayi murmushi “lahhh kada ki damu. Daddy ya ce zai biyo muje yanzu. Ke kuma ki zauna saboda Hayat.”
“In zauna?” Salwa ta ce ba shiri.
“Ina jin babu lallai ya kwana tumda yace min suna ta waya da Kamal. Meeting ne ya hana shi fita da wuri.”
Rasa bakin magana tayi ta fita kawai. Zahra ta bita da ido ba tare da kawo komai a ranta ba.
Da Ahmad ya dawo ko shiga gidan bai yi ba ya kira Zahra ya ce ta fito bayan la’asar. Kafin ta gama shirya Aisha Salwa tayi saurin fita wajensa.
“Ya Ahmad kana ganin daga gida ba za su fassara rashin zuwana duba shi ba ace don ba ɗan uwana bane?”
“Ke, gidanmu babu irin wannan kin ji. Bana son Hayat yayi missing islamiyya shi yasa nace ki zauna.”
“Naga kamar zamu iya dawowa kafin ya taso.”
Wani irin kallo mai tattare da tuhuma ya yi mata.
“To ko mu zauna ke ki je?”
Diriricewa tayi don bata tsammaci furucinsa ba. Ta ce “Haba Yaya ba haka nake nufi ba.”
Su na tafiya ta sake kiran Kamal ya ce mata jikin Taj da sauƙi. Don ya ƙara rura wutar da ya fahimci ta soma cinta ya ce
“Yanzu dai ya gama amai wallahi. Ya galabaita sosai don ko zama ya kasa. Amma dai da sauƙi za a ce.”
“Kace ina masa sannu don Allah” ta ce da muryar kuka.
“Ban gane ba. Ba za ki zo ba?”
Da sanyin murya ta ce “Ya Ahmad ya ce na zauna.”
Tausayi ta bashi ya daina ɗorata. Yana ajiye wayar ya yi murmushi “shege Happy. Daga zuwa ya yi ɓarna a zuciyar ƴar mutane.”
Wasa wasa sai da Taj ya yi kwana biyar aka sallamo shi. Kuma tun washegarin kwanciyar tasa kullum sai Salwa ta je. Duk wani motsinta Ahmad ya kafa ya tsare har ya tabbatar da zarginsa. Hankalinsa kuwa ya tashi don yana jiye mata abubuwa da dama.
***
Takarda ce cikin foolscap Hamdi take ta karantawa tun wajen kwana uku tana son haddacewa. Speech ne malamar English ta bata wanda za ta yi ra ranar taron. Cikinta har ƙullewa ya yi yau da aka kira assalatu saboda tana da tsoron yin magana a gaban mutane. Har aka gama yayin monitoci da mataimakansu da ma prefects bata taɓa karɓa ba. Komai na mutane gudu take. Sai gashi wannan karon Principal da kanta ta ce a bata. Wai jawabin godiya ne a matsayinta na overall student ta makaranta. Da shawarwari ga ƴan uwanta ɗalibai akan hanyoyin bi domin samun nasara.
Ga dai takarda ko daga bacci ta farka za ta iya kawota tas da ka, amma da zarar tayi tunanin mutanen da za ta fuskanta sai taji kan ya koma fanko. A haka ta janyo jiki ta zo wajen taron tamkar mara lafiya. Ana tsakar gabatar da shirye shirye ta tashi kafin a zo kanta. Bayan Admin block taje ta sami wuri ta zauna tana ta bita kamar mai zuwa musabaqa.
*
A cikin dandazon mutanen da su ka zo taron harda ƴaƴa da jikokin Alh. Hayatu Sule. Akwai jikarsa Firdaus ƴar wajen babbar ƴarsa Hajiyayye cikin masu fita. Yarinyar mutuniyar Taj ce sannan bata san ya zo gari ba. Rabonta da shi tun tana ƴar ƙarama. Shi yasa da Hajiyayyen ta gayyaci ƴan uwanta zuwa graduation shi ya fara amsawa zai je. A cikin hayaniyar programs ɗin da ake gabatarwa da hirar ƴan uwansa yaji wayarsa tana vibrating. Sunan Amma ya gani ba shiri ya tashi yana neman wurin da zai iya amsa wayar ba tare da hayaniyar ta hana shi jin me take cewa ba. Kamar ance ya kalli damansa ya hango wata yarinya tana tafiya da sauri sauri ta nufi bayan Admin block. Sanye take da ankon ƴan graduation ɗin da gown ɗinsu. Ta riƙe hular a hannu. Ɗaurinta na Maryam Babangida ya zauna đas a kanta. Sai ɗan mayafi da ta yafa a kansa ta rufe wuyanta da shi.
Numfashinsa kusan ɗaukewa ya yi da ganin yarinyar kamar yau ya fara ganin mace. A kallon farko ya iya tantance tsayinta da yake matsakaici. Fatarta da yake iya gani a fuska tayi daidai da wankan tawarɗa da ake kiran masu sirkin fari da baƙi. Fuskar ya sake kallo wadda ta fizgi duk wani rational tunanin dake yawo a kansa. A cike take da duk wani abu da yake muradi a wurin mace. Ga ƙarin kwarjini da nutsuwa da yake da yaƙinin tana da su daga yanayin tafiyarta. Wayar da yake son ɗauka tuni ya manta da ita har ta katse.
Kamar ana ingiza shi ya bi ta. Idanunta a rufe lokacin da ya hangota. Ta sanya hannu ta rufe kunne tana karanto abin da ta haddace.
Sannu a hankali ya dinga takowa gabanta har ya rage babu nisan kirki a tsakaninsu.
Ƙamshin da Hamdi taji yana ta kusanto ta ne ya hanata buɗe ido. A zuciyarta ta gama tsorata don an saba faɗin akwai ƙwanƙwamai a bayan Admin block. Wai ba a ganinsu sai dare. To me ya fito dasu da hantsin nan lokacin da ake ta kai kawo a makarantar?
Taj na jin yadda ta ja numfashi ta kasa saukewa da ya matso. Ya saki murmushi.
“Buɗe idonki.”
Hamdi ta tsuke baki don in ta sami wuri akwai tsiwa. To yau dai aljanu za ta nunawa bata tsoronsu don kada su maketa a banza. Ta sha jin labarin idan baka nuna tsoronsu ba, ba sa yiwa mutum komai.
“Anƙi ɗin. Tsakanina da aljani nan gani nan bari. Na riƙe Ayatul Kursiyyu.”
Dariya Taj ya yi a hankali ya a jin wani irin abu na bin jikinsa.
“Ni ba mai cutarwa bane so you can open your eyes.”
Ido ɗaya ta ɗan buɗe a hankali ta tabbatar mutum ne sannan ta buɗe ɗayan. A lokaci guda idanuwansu su ka sarƙe cikin na juna sai dai Hamdi bata iya zurfafa kallon ba ta kawar da kai. Babu abin da zai sa ta iya jurewa kallon idanun mutumin dake gabanta masu kaifi da su ka tsareta. A zuciyarta kuwa sai da ta kira sunan Allah saboda tunda take bata taɓa ganin wani namiji taji ina ma ace….ba sai a kan wanda yake gabanta.
A daidai lokacin su ka ji sanarwa ta sipika.
“Bayan wannan gajeriyar diramar da za ayi mana mai taken Ilimi a Karkara, za mu saurari speech daga bakin overall student ɗin makarantar nan Hamdiyya Habib.”
Wani haɗaɗɗen ruɗani Taj ya gani a idanun yarinyar gabansa. Da haka ya gane ita ce aka ambaci sunanta.
Takardar hannunta yaga ta kalla kamar za ta yi kuka.
“Kin taɓa ganina?”
“A’a.”
“Good. Ki yi imagining ni ne duka mutanen wurin can sai ki yi speech ɗin naki na ji.”
Kamar ta ce a’a sai dai ta gyara tsayuwarta. Ta rufe ido.
“Open your eyes and think of …” ya kalleta “Wa ki ka fi so a duniya?”
“Iyayena.”
“To ni ne su. Ki sa a ranki su kaɗai ne a wurin.”
Sallama tayi da rawar murya ta soma da gabatar da kanta amma ta kasa faɗin sunanta ma. Sai komawa baya take yi. Taj ya karɓi takardar ya dunƙuleta a cikin hannunsa bayan ya karanta a gurguje.
“Bayan godiya ga school da iyayenki za ki bawa students shawarar karatu. Do you realy need a paper to say all that?”
Hamdi ta ƙifta idanu “no.”
“Then say what you truly want to say from your heart. You will be fine in sha Allah.”
Haka kawai magana da shi ta sanya mata wata irin nutsuwa. Ta tattare doguwar rigarta sama kaɗan ta dube shi da murmushi a fuskarta.
“Thank you.”
Ya so sake cewa wani abu amma tunawa da ya yi tana buƙatar nutsuwa kafin ta iya yin abin da ke gabanta sai ya barta ta tafi. Ya raya a zuciyarsa idan an gama taron zai nemeta.
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
