Rayuwa Da Gibi – Chapter Nine
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Zazzaɓin gaske ne ya kama Ummi tun bayan ta saurari wayar Vice principal da mahaifinta. Aikin gama ya riga ya gama. Bayan ya ajiye wayar wani irin kallo ya yi mata ya jinjina ƙarfin halinta. Sannan ya ƙara tabbatarwa mace abar tsoro ce komai ƙanƙantarta.
“Wannan mutumin shi ne mahaifinki Ummi?”
Kai a ƙasa ta ce “eh.”
“Wanda yake zuwa kuma ya kuke da shi? Kuma me yasa ki ka zaɓi faɗin gaskiya yanzu?”
Shiru tayi babu amsa tunda Hamdi ma taƙi magana me zai sa ta fara?
Rai a ɓace ya ce “To kuwa ki kwana da sanin cewa yau ce ranarki ta ƙarshe a makarantar nan. Don ban ga wani dalili da zai hana a kore ki gobe ba ko da kece mai gaskiya. Sannan dole zan kira shi domin a warware komai gaban mahaifin naki.”
Yanzu ma kasa cewa komai tayi sai faman saƙe-saƙen neman mafita. Sannan a gefe guda babu irin ashar ɗin da bata saukewa Hamdi ba. Da farko ta san kawai jindaɗin samun mai yi mata bauta a makaranta tayi da sanin sirrin Hamdi. Yanzu kuwa wata irin tsana ce da za ka ji komai ma za ka iya yiwa mutum take ji akanta. Har lokacin bata saduda ba don tana jin da Hamdi tayi mata biyayya ta bata ruwan nan da bata ga wannan lokacin ba. Haɗuwarta da Baba Maje gobe ba ƙaramar tarzoma zai tayar ba.
“Ki tashi ki fice min daga office nace.”
Tsawar VP ta dawo da tunaninta inda take. Ta miƙe za ta fita sai kawai wani tunani ya zo mata. Guntun murmushi ta saki wanda har ga Allah sai da ya VP ɗin tsoro da shakku akanta.
Wurin ƙawarta konace babbar ƴar korarta Widad taje da saurinta. Sun gama nasu punishment ɗin na yau sai kuma washegari da ake sa ran samun ruwa. Za su wanke banɗakunan makarantar kaf har na malamai. Ga kuma sharar harabar makaranta da cire ciyayi.
Widad na ganinta ta tashi zaune daga kwanciyar gajiyar da tayi. Ummi ko kallon arziƙi bata yiwa ciwon dake babban yatsan Widad na ƙafa wanda taji a wurin faɗan ɗazu ba. Kuma ta gan shi sarai amma ba shi ne a gabanta ba.
“Bani wayarki in kira Uncle B”
“Kuna can aka zo inspection ɗin bazata tun bayan an nuna wayarki a wajen principal. Yau wayar da aka fitar daga ɗakin nan tafi ashirin.”
Muguwar harara Ummi ta jefeta da ita sannan ta yatsina fuska ta ce mata “banza, me yasa ko a pant baki ɓoye ba?”
“Korarmu aka yi waje bamu san dalili ba. Sannan aka yi searching ɗinmu da ɗai-ɗai.” Widad ta amsa tana mai ɓoye zafin zagin da halin ko in kula da Ummin ta saba nuna mata.
Plan ɗinta na farko ya faɗi tun kafin ta aiwatar. Dama niyarta ta faɗawa sugar daddy ɗin nata da take kira Uncle B idan an nemi numbarsa kada ya yarda ya zo. Shawara ta biyu kawai za ta ɗauka. Idan an zauna gobe kawai ta tada aljanu kuma duk yadda za ayi da ita kar ta yadda ta dawo daidai sai an koma gida. In ya so ko kasheta za ayi gara ayi a can.
***
A hanyarsa ta zuwa tasha cikin adaidaita sahu Abba ya kira ƙaninsa a waya. Hankalinsa ne sam bai kwanta da zuwa makarantarsu Hamdi ba. Yana son kare martabar ƴaƴansa daga dukkan abin da zai iya janyo musu raini daga mutane. Ya tuna wani lokaci da Yaya Hayatu kamar yadda yake kiran Alhaji yayi masa wata magana a baya.
“Habibu gaba nake jiye maka. Lokacin da za ka ji kunyar nuna kanka a wasu wuraren saboda kana ganin kamar darajarka bata kai ba. A lokacin ilimi ko rashinsa, talauci ko arziƙi ba su ne za su zame maka shamaki ba. Wannan mazantakar da kake gudu da Allah Ya karramaka da ita ce za ka so a baka aro ko na awa guda ne.”
Bai manta yadda ya murguɗa baki bayan wucewar Alh. Hayatu ba. Ya doka cinya harda tofar da yawu.
“Aniyarka ta bika. Sa idawa, ana ruwa kuna ƙirgawa.” Ya nuna ƙafarsa “wannan sayyara da Allah Ya bani babu inda ba za ta shiga ba sha Allahu.”
Ga ire iren ranakun sun zo. Ina ma ana mayar da hannun agogo baya. Da ya juya lokaci ya canja komai banda auren Jinjin. Matar da ta rufa masa asiri ta kuma bashi ƴaƴa mafi soyuwa a gare shi.
Gaisawa su ka yi da ƙanin nasa da girmamawa sannan ya faɗa masa halin da yake ciki a kunyace.
“Wallahi Yaya Habibu ka ganni a asibiti wani maƙocina ne babu lafiya. Daga shi sai matarsa ga yara ƙananu ta taho dasu. Basu da kowa a nan sai mu maƙota. Yanzu haka yayansa dake Zaria yana hanya. Tun asuba nake nan.”
“Ahhh, yi zamanka Abdulƙadir. Bari kawai naje.”
“Ka daina ɓoye kanka daga rayuwar yaran nan. Yau in dukkaninmu babu sai kai kaɗai shikenan sai ace zuri’armu basu da uba saboda abin da ya wuce?”
Yayi maganar ne saboda ya saba ji daga yaransa cewa ƴaƴan yayan nasa suna kunyar alaƙarsu da shi. Bai ga laifinsu ba Fisabilillah. Amma kuma Allah da Ya haɗa alaƙar Shi Ya san yadda zai tafiyar da al’amura. Tayasu ɓoye kansa ba dabara bace tunda duk lalacewa da uba ake ado.
Abba bai sake neman kowa ba ya tafi makarantar. Anyi sa’a yau shadda ya sanya ruwan madara, riga da wando harda hula. Da ya shiga makarantar bayan tafiyar minti arba’in tafiyarsa ya fara ƙoƙarin gyarawa. Sannan da zai tambayi masu gadi ofishin principal ya daddage ya kumbura murya. Amma kunne da idanu masu lafiya babu yadda za ayi su kasa fahimtar me ake son ɓoye musu. Basu dai nuna a fuska ba guda ya nuna masa hanyar office ɗin. A can gefe inda ake ajiye motoci ya ga wata kamar ta Baba Maje. Amma da yake baya tare da nutsuwa bai tsaya ƙare mata kallo ba.
***
A rayuwa babu abin da yafi tashin hankali kamar a samu wani ya san sirri a kanka wanda baka so a sani. Kuma in anyi rashin sa’a ya dinga amfani da wannan damar wurin cusgunawa rayuwarka. A shekara shidan da Hamdi tayi a makarantar nan bata taɓa shiga matsanancin hali ba sai da Ummi ta fara blackmailing ɗinta. A jiya da abu ya fito fili waɗanda su ka sami ganin bidiyon nan su ka labartawa waɗanda basu gani ba, sai taji zuciyarta wasai. Abin ya matuƙar bata mamaki. Tayi zaton in an sani an tsokaneta za ta iya yin kuka. Sai gashi babu wanda ya tunkareta tunda aka ga abin da ta yiwa Ummi da kuma maganar da ta yaɓawa wata Metiron bayan ta dawo ɗaki.
Da yake wasu manyan hankalinsu a ƙwauri yake, matar a gaban mutane ta tambayeta.
“Hamdiyya da gaske ne babanki ɗan daudu ne?”
A fusace ta amsa da “Eh, amma yafi uban wasu da yake zaman prison.”
Matar tayi matuƙar mamaki domin kuwa ba kowa ne ma ya san cewa mijinta yana prison ba saboda sata. Laƙwas tayi don babu halin sake magana saboda ƴan kallo sun sami sabon abin tattaunawa.
Ƙarfe goma aka aiko kiransu. Tana zuwa ta sami Ummi tayi kneel down a gaban teburin Principal. Ga Baba Maje zaune akan kujera. Yana ganinta ya saki fuska sosai yana magana da Principal ɗin.
“Yauwa ita ce kuwa.”
Principal ta dube shi da ɗan sakin fuska don taga sam bai fahimci zancen ba ta ce “Nima ita nake nufi Alh. Maje. Wannan Hamdiyyan ce dai su ka yi faɗa da Ummi jiya su ka yi sanadin hargitsa makarantar nan.”
“Na gane bayanin naki Hajiya. Dama abin da nake son fahimtar dake shi ne ina ganin ɗaya daga cikinsu ce ta shigar wa ƴar uwarta. Ba wai a junansu su ka yi faɗan ba.” Ya yi mata bayani dalla dalla a ƙoƙarinsa na son ta gane.
Murmushi tayi masa don yanzu bata jin za su fahimci komai sai yaran sun yi magana.
“Ko me yasa ka yi wannan tunanin?”
Ƴar dariya ya yi gami da gyara hannun rigarsa “mahaifin Hamdiyya abokina ne tun kafin a haifesu kin gansu nan. Shi yasa nake tunanin ko karewa juna suka yi. Ba kuma wai goyon bayansu nake ba. In sun yiwa makaranta laifi zan bada goyon baya ɗari bisa ɗari a hukunta su.”
Abin da ya fađa ya bawa Principal ɗin mamaki sai dai bata ce komai ba sakamakon sallamar sakatarenta da mutane biyu. Ɗaya wani ƙosasshen Alhaji ne ya sha babbar riga yana fama da kayan tumbi. Ɗayan kuwa Abban Hamdi ne. Su na shigowa VP da wasu manya cikin malaman su ka shigo su ma.
Abba na ganin Baba Maje ya ce “da na san za ka zo ai da nayi zamana a gida.”
“Ko kuma da ni na zauna ba.”
Dariya su ka yi sannan aka yi musabaha tsakanin duka mazan wajen.
Murya da yanayin mahaifin Hamdi kaɗai yasa malaman kallon kallo a junansu. Principal ta buƙaci a buɗe zaman da addu’a sannan ta ɗauko wayar Ummi ta miƙa mata.
“Buɗe min wayar nan don na sami labarin ita ta fara janyo rigimar.”
Kai Alhaji mai ɗan tumbi wato Uncle B da baka gane Baba Maje ba tunda Ummin bata kama dashi sai ya kama faɗan bogi.
“Ban hanaki zuwa da waya makaranta ba? Ke kenan kullum rigima ta tashi sunanki ne a sahun gaba.”
Baba Maje buɗe baki yayi don maganar ba tsoro ta bashi ba illa ruɗa masa tunani. VP na ganin haka sai ya taso har inda yake ya ja shi waje.
“Duk abin da za ka ji ko ka gani kada kace komai don Allah har ka gama fahimtar inda zancen ya dosa.”
“To amma…”
“Mu koma ciki. Komai zai warware kansa.”
Haƙuri ya bawa Principal na katse su sannan su ka jira Ummi ta buɗe wayar da rawar hannu. Jikinta babu inda baya ɓari. So take tayi aljanun ƙaryan tun yanzu amma bata da ƙwarin gwiwar pretending. Hamdi da bata san badaƙalar dake kwance ba kuwa ko a jikinta. Jikin kujerar da Abba ke zaune ta raɓa tayi kneel down abinta.
“Kunna min abin da ki ka kunnawa ɗalibai a jiya.”
Nan fa ɗaya. Kasa kunnawa tayi. Displine master ya daka mata tsawa amma ko gezau.
“Kin cika umarnin da aka baki ko sai na tashi?”
Muryar Baba Maje ta fito da kaushi. Uncle B duk ya zata malami ne da ake tsoro shi yasa bai ji komai ba da yaga ta cika umarni da rawar jiki.
Ofishin karaɗewa yayi da muryar Abba. Kunya tayi masifar kama shi. Idanunsa su ka yi jawur lokaci guda. Hamdi taji wani irin tausayinsa wanda yasa ta kuka. Baba Maje ya rasa me yake yi masa daɗi.
Principal ta miƙawa kowa wayar ya gani da idonsa sannan ta umarci Hamdi da tayi magana. Ba tare da coge ba ta faɗi abin da ya faru tun ranar da su Baba Maje su ka zo gidansu har abin da ya faru jiyan. Irin cin zarafin da Ummi ke yi mata da takura kawai don ta mallaki sirrin mahaifinta. Kallon takaici kala kala ya dinga sauka akan Ummin bayan ra gama magana.
“Ummi haka aka yi? A ina ki ka sami bidiyon?” Uncle B ya tambayeta har yana kai hannu zai ɗaga haɓarta domin kanta a ƙasa yake tana zubar da zafafan ƙwallar tsanar Hamdi.
“Wai kai ɗin uban waye a makarantar nan da za ka taɓa baligar mace?” Baba Maje ya tambaye shi a harzuƙe bayan ya doke masa hannu.
“Kai zan yi wa wannan tambayar.” Ya kalli Principal ɗin “ya kamata malamanki su san aikinsu in ba haka ba zan cireta daga makarantar nan.”
Baba Maje ya ce “Kai a wa?”
“Ni a mariƙinta” Uncle B ya bada amsa kai tsaye.
VP gaban kujera ya dawo don yaga an zo inda yake jira. Cikin zafin rai kuwa Baba Maje ya ɗago Ummi tsaye ya dubeta.
“Kalli ƙwayar idona ki faɗa min waye wannan.”
Numfashi ta fara ja tana shirin yin suman ƙarya taji Baban nata ya yi mata wata irin wawiyar jijjiga. Muryarsa tana rawa har wajen office ɗin kuma ana ji ya ce,
“Idan ki ka ce za ki yi min ƙaryarku ta ɗalibai zan sabauta miki halitta a wajen nan. Ki faɗa min waye shi.”
“Saurayi na ne.”
Tasss, tass, tas ya ɗauketa da wasu gigitattun maruka. Abba ya yi saurin finciketa daga hannunsa ya tsaya a tsakani.
“Haba Maje…”
“Matsa min Habibu.” Ya furta yana huci.
Uncle B na ganin haka ya tashi zai sulale ya gudu sai dai babu dama. VP ya sanya securities ɗin makaranta a bakin ƙofa. Hasashen haka zai iya faruwa tun a jiya yasa ya ɗauki matakin da ya dace.
Da ƙyar da suɗin goshi aka samu Baba Maje ya zauna. Abba ya dubi Principal ɗin ya yi magana.
“Da farko zan fara da baku haƙuri akan ɓarnar da yaran nan su ka janyo muku. Ummi tayi kuskure sannan ita ma Hamdi tayi na ɗaukar doka a hannunta. Amma fa duka abin da ya faru laifina ne…” ya sunkuyar da kansa.
Principal ta kalle shi da tausayawa “bari na ɗan ce wani abu a nan.” Ta kalli Hamdi “mu iyayenku da ku ke gani muma haifarmu aka yi ba da wayo muka zo duniya ba. Shekarunmu na hawa ne muna daɗa hankali. Duk wani kuskure da kuke yi a yanzu muma mun yi ƙila ma fiye da haka a lokacin tamu ƙuruciyar. Yanzu mun girma mun san illar abin shi ne dalilin da yake sa muke muku faɗa ma idan kun yi. Abin nufi a nan shi ne ƙuruciya da raunin hankali a baya yasa mahaifinki yin kuskuren bin rayuwar da kowa yake ƙyama. Gashi ita aba ce da ko ka daina da wahala đabi’unta su barka ɗari bisa ɗari. Amma tunda Allah Ya baki shi a uba ki rungume kayanki da godiya. Da baki ji kunya kin ɓoye shi ba, babu wanda ya isa ya ɗaga miki hankali akan shi. Ki nuna godiyarki ga Allah ta hanyar appreciating ɗin duk abin da Ya baki.”
Gyaɗa kai tayi tana goge hawaye “Abba don Allah ka yafe min.”
Da ƴar muryarsa ya ce “Allah Ya yi miki albarka Hamdiyya. Ki bawa iyayenki na makaranta haƙuri su ma.”
Ta kuwa bi umarninsa ta bawa kowa haƙurin abin da su ka yi jiya. Cike da kunya da jin nauyi Baba Maje ya bawa Abba haƙuri.
Abba ya yi murmushi “Don Allah ka bar wannan zance.”
“Ta yaya zan bari? Bayan shekara sama da ashirin da rabuwarmu ace ƴar cikina ce tayi maka irin wannan tozarcin?”
“Magana ni dai ta wuce don Allah.” Abba ya sake maimaitawa.
VP ya ce “yallaɓai ina ganin sanin alaƙar Ummi da mutumin nan shi ne abu mafi mahimmanci yanzu tunda an kashe wancan case ɗin.”
A lokacin aka fito da file na fitinannun makaranta inda sunan Ummi ya bayyana a kowanne term tun zuwanta a JS3. Bata fara laifin da ta cancanci a kira iyaye ba sai a SS2 da ta zama cikakkiyar senior. Kuma a lokacin ne duk sanda aka buƙaci iyayenta sai wannan mutumi dake zazzare idanu ya zo a matsayin kawunta. Ita ma aka bata dama ta faɗi yadda suke biyan maigadi su haura katanga ita da wasu. Samarinsu su kai su gari a shaƙata a sha ice cream da su shawarma a dawo. A rantsuwarta dai ta ce babu abin da ya taɓa haɗasu na fasiƙanci. Baba Maje kasa jurar jin maganganun ya yi ya finciki bulalar hannun wani malami ya shiga lafta mata. Da taron dangi aka raba shi da bulalar
“Kanki ki ka cuta Ummi. Nan duka ɗaliban da ki ka zalinta in basu yafe ba sai kin gani a ƙwaryarki.”
Fuskarta yaɓe yaɓe da majina da hawaye ta ce “Baba ka yafe min.”
“Ba dole na ba? Idan nayi miki baki rayuwarki ai sai tafi haka lalacewa. Ki tashi ki haɗo kayanki don kin gama karatu kenan.”
“Alhaji ba ayi haka ba.” Principal ta sa baki “ka bari mu ɗauki matakin da ya dace.”
“Maje kada ka ɗauki hukunci cikin fushi.”
“Kun san Allah ɗaya ne ko? To wallahi yarinyar nan ta gama karatu a ƙarƙashin ikona.”
Ya kalli Uncle B ya yi wani irin murmushi mai ciwo sannan ya ɗaga waya ya kira ɗan yayarsa police. Makarantar ya kwatanta masa.
“Ku taho yanzu don Allah.”
“Yallaɓai da ka bari an kira masa ƴan sandan dake kusa da nan. Ka san kowanne laifi ana shigar dashi a unguwar da ya faru.”
“A kira su. Shi wannan ɗana ne saboda haka ina jiran zuwansa saboda ina son komai ya tafi da jagorancin wani nawa.”
Suna wannan zance Uncle B ya matsa gefe yana ta bige bigen waya da hargagin iska. Bayan ya gama ya cigaba da masifa yana doka teburin Principal.
“Baki san ko ni waye ba a garin nan wallahi. Ina da damar sanyawa a rufe makarantar nan baki ɗaya a yau idan na so.”
“Ka daɗe baka aiwatar ba. Mutumin banza. Girma da matsayinka basu ƙara maka komai ba sai sanya hannu wajen ɓata tarbiyar yaran mutane.”
A cikin minti talatin motar ƴan sandan da VP ya kira ta iso makarantar aka yi awon gaba da Uncle B. Baba Maje da Ummi da VP ɗin su ka tafi tare dasu. Principal ta sanar da malamanta wajibcin neman iyayen yara a kurkusa domin tattaunawa da gujewa maimaicin abin da ya faru.
Hamdi da Abbanta su ka fito tare fuskokinsu babu walwala sosai. Shi yana cikin damuwar halin da abokinsa ya sami iyalinsa, ita kuma tana cike da kunyar ya san irin matsayin da ta ajiye shi a matsayinsa na uba. Hannunsa ta riƙe ganin yana raɓewa gefe guda.
“Abba in kai ka ka ga ajujuwanmu?”
“A’a Hamdi.” Ya zame hannunsa.
“Ba ka yafe min ba ko?” Idanunta su ka kawo ruwa.
“Ban taɓa fushi dake ba. Ba dai na son sake bar miki abin faɗi a cikin abokan karatunki.” Ya ce a sanyaye.
Wannan furuci nasa ya sanyata kuka sosai. Ta roƙe shi da ya jirata a nan inda yake za ta dawo bayan ya hanata kukan. Tana tafiya ta samu ɗalibai na dinning hall ana cin abincin rana. Duk da yadda take wasiwasi amma da ta tuno da maganar da Principal tayi mata sai taji zuciyarta ta daina tsoron komai.
“SS3 A” ta ƙwala kira da ƙarfi.
Tashi su ka yi wasu kuma su ka amsa da baki.
“Ku zo ku gaisa da Abbana.”
Ai kusan rabin hall ɗin ne su ka fita a guje. Aka kasa controlling ɗin su. Tana gaba har inda ta barshi tsaye. Kawar da kai taga ya yi tayi murmushi ta zaga gabansa.
“Abba an zo gaishe ka.”
Tunda yake kullum yaransa su ka zo gida da ƙawa basa taɓa cewa a gaisa da shi. Ƙawayen ma bai san kowa ba sai na dangi ƴaƴan ƴan uwa.
Ya juya suna ta ina wuni shi kuwa ya kasa amsawa saboda kada jin muryarsa yasa a yiwa ƴarsa dariya.
“Abba ka amsa mana” Hamdi ta ce tana dariya kamar ba ita ba. Yarinyar da kullum take cikin ƙunci da damuwa.
Ya buɗe baki ya dinga amsa musu. Ƴan matan nan maimakon nuna ƙyama sai yake ganin kamar ya burgesu. Wasu basu taɓa ganin ɗan daudu a kusa haka ba. Kamar wani abin sha’awa su ka dinga girmama shi. Kan Hamdi ya kumbura suntum saboda daɗi. Ranar da taimakon malamai aka ƙora su duka har ita cikin makaranta sannan ya samu ya tafi wajen Baba Maje.
***
Ganin su Inna ya yi saurin ɗaukewa Taj damuwar da ya shiga. Sai gashi ya zage yana ta hira kamar ba shi ba. A cikin hirar ne ya tambaye su ko akwai wani abu a tattare dashi da zai sa ayi masa kallon namijin da bai cika ba.
Ya naɗe hannun rigarsa har saman kafaɗa irin yadda yara su ke yi.
“Saboda son burge Alhaji har gym nake zuwa ina motsa jiki. Yanzu wannan…” ya nuna dantsensa “bai isa a kirani namiji ba?”
Kamal kula ya yi da Salwa da ta shigo ɗauke da tray ɗin abinci da yadda tayi saurin ɗauke ido daga kallon hannun Taj. Shi kuma gwanin ya kama ƙasan riga zai ɗaga wai ya nuna musu packs ɗin ƙirjinsa. Gudun kada ɗan uwansa ya kunyata shi ne ya kai masa duka a hannun.
“Dalla malam rufe wannan sandar raken.”
Taj da yaji zafi ya rama dukan “ɗan baƙinciki in ka isa ka buɗe naka mai kama da taliya.”
“Mama kina dai jin abin da yake faɗa min ko?” Kamal ya faɗi yana miƙewa tsaye.
“Laifinka ne fa Kamal. Kai ka fara dukansa” Mama ta goyi bayan Taj.
“Saboda ya dawo daga America za ki nuna min wariya? Ke fa ki ka hana raini tsakaninmu.”
Su Hajiya sai dariya su ke yi. Taj ya sami goyon baya ya cigaba da tsokanarsa.
“Ka ci sa’a ban auro baturiya ba da kaga asalin wariya. In taho da ƴan ƴaƴana farare su na Mom…Dad…who is this black man” ya nuna Kamal aka sake tuntsirewa da dariya. Ya cigaba da tsokanarsa “Duk ƴan uwa su taru a kansu ana son burgesu. Kai kuwa naka sai dai kaji ana cewa ‘Sule maza tafi wurin babarka ta goge maka majina’ “
“Banza ƙazami. Wai majina kamar tashin Soron ɗinki. Kuma don wulaƙanci ba ma Sulaiman ba Sule zan haifa?” Kamal ya faɗi yana shure shi da ƙafa.
Taj dariyar da ya san za ta ƙular dashi ya cigaba da yi.
“Sule Kamalu Hayatu Sule. Irin ƴan chubby yaran nan masu ɗan ƙaton ciki ba.”
Ba ka jin komai a falon sai dariyar iyalin ta farinciki. Salwa da take ganin duk motsin Taj wani salo ne daban mai tafiya da zuciyarta ce kaɗai ta ƙare da murmushi.
Kamal da Taj su ka gaji da wasansu na dambe da girma bai hanasu yi ba su ka koma cin abinci daga plate ɗaya su na hirar da babu mai ji.
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
