Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
    Ummi dai baje kolin rashin mutumcinta tayi akan Hamdi har ya kasance sauran ɗalibai suna samun sararawa. Kowanne aiki Hamdi, kowacce bola da shara ma ita ɗin dai take nema. Wanki harda na su pant ita take mata. Su ɗebo ruwa da kwafar note dama tuni ta daina saka wasu. Kuma ko da wasa Hamdi bata taɓa faɗin wata kalmar neman sauƙi ba. Komai Ummi ta ce ‘to’ ce amsar. Ita dai burinta ta bar makarantar ba tare da kowa ya san ko waye mahaifinta ba.

    Da yake a cikin hutun da su ka aka yi jarabawar JAMB, yanzu ƴan kwanaki su ka rage kafin a fara WAEC. Kowa ya duƙufa da karatu ba ji ba gani. Waɗanda basu ɗauki karatun a bakin komai ba irinsu Ummi kuwa shagalinsu suke yi.

    Ranar wata laraba da safe aka tashi makarantar babu ruwa. Abin ka da lokacin zafi. Tsakanin April da May a garin Kano dama ba a cewa komai. Rijiyar makarantar mai dama dama ba a samun komai sai wani ruwan dauɗa wanda zai iya sati bai kwanta ba. Kowa ya shiga damuwa don ko darussan aji ba a shiga ba. Ga ɗan karen zafi ana ta zufa. Principal tun safe ta fice sai wajajen shabiyu ta dawo da tankokin ruwa har bakwai a bayanta. Yara sai murna. Aka umarci malamai da su kula da ɗaliban wajen bin layi ta yadda kowa zai samu. Sannan an ja musu kunne babu mai ƙarɓar ruwa sau biyu. Kuma bokiti biyu kaɗai za a cika wa kowa saboda kada wasu su rasa.

    Layi layi aka jera ɗaliban na ajujuwansu. A sammakon Hamdi ita ce ta talatin da huɗu a layinsu. Kafin a zo kanta rana ta gama dafa ta. Ana zuba mata taji wani sanyi ya ratsata. Ta ɗauki bokatan hagu da dama ta wuce ɗaki. Tun kafin ta isa bakin matattakalar hostel ɗin ta hango Ummi da ƙawayenta a zaune kan dandamalin wurin suna ta hayaniya ana dariya. Fuska a haɗe Ummin ta tarbeta da ta ƙarasa.

    “Kin daɗe a layi gaskiya. Ke ko irin turereniyar nan baki iya bane?”

    Take takenta Hamdi ta gane sai dai ta riga ta yiwa kanta alƙawarin ko me zai faru ba za ta bata ruwan da ta wahala wurin samu ba. Jikinta gabaɗaya ƙaiƙayi yake yi mata. Ga ƙishi ga yunwa.

    “Ban iya ba.”

    “Mtswww, wuce ki kai min ruwan in samu nayi wanka kafin a gama abinci.”

    Wata zaƙaƙura ta ce “Ummi kin ce fa nima za ki sa ta ɗebo min.”

    “Ki bari ta juye min mana.” Ta cewa wadda tayi maganar a wulaƙance.

    Juyawa Ummi tayi taga Hamdi ta ajiye bokatan ta sarƙe hannu a ƙirji.

    Rai a ɓace ta ce mata “Ɗauki mu tafi mana.”

    “Ki je ki bi layi don babu wanda za a zubawa sau biyu. Har ticking suna ake yi.”

    “To sai ki san yadda za ki yi. Ni ki wuce ki zuba min zafi nake ji.”

    Hamdi ta rasa daga ina take jin wani ƙwarin gwiwa kawai ta ce “naga kamar baki gane ba. Wannan ruwana ne. Ki je ki ɗebo naki.”

    Wata uwar shewa Ummi tayi tana dafa ƙirji “dani kike? Har kin manta abin da zan iya yi miki idan ki ka ɓata min rai?”

    Tunawa da alamun mutumcin su Iyaa tayi sai take ganin kamar duk haukan Ummi ba za ta fitar da bidiyo ɗin ba.

    “Kin daɗe baki nunawa duk makarantar nan waye ubana ba.”

    “Kanbu, dani kike?” Ummi ta faɗi cike da mamaki. Sai kuma ta fasa faɗan ta ce ƙawayenta su ɗauko bokitin.

    Suna kai hannu Hamdi ta tare kayanta ta hanyar durƙusawa a gaban bokatan ta tarosu da hannuwanta.

    “Wallahi ba zan baki ruwan nan ba.”

    Mamakin me Hamdi ta taka a yau ne ya kama Ummi. Taga gara ta nuna mata idan tace za ta yi abu lallai babu fashi. Waya ta ɗauko daga aljihun wandonta na kayan prep. Gaban Hamdi na faɗuwa amma idonta yau ya ƙeƙashe. Tana ji kamar kowa muryar Abbanta ta ƙarade wurin. Kan kace meye wannan ɗalibai sun taru suna jin bayanin Ummi na cewa wannan zuƙeƙiyar muryar fa ta mahaifin Hamdiyya Habib ne wanda ya kasance ɗan daudu. Aka dinga tururuwar leƙa bidiyon ana cewa ga kama nan.

    Kallon Hamdi aka fara ana zunɗe tayi kamar bata jinsu duk yadda ranta ke suya ta duƙa za ta ɗauke ruwan sai taji Ummi tayi wata maganar da ranta ba zai iya ɗauka ba.

    “Mamanta kuwa cangal ce mai ƙafa ɗaya da kwata” ta cilla ƙafa ɗaya ta banƙaro ƙirji ɓari ɗaya “idan tana tafiya sai ka rantse Awilo ne zai yi rawar waƙarsa.”

    Innalillahi wa inna ilaihi raji’un. Hamdi ta iya faɗi don dariyar da aka tuntsire da ita a yayinda Ummi ke kwatanta tafiyar Yaya ta mugun baƙanta mata rai. Sakin bokiti guda tayi ta ɗaga ɗayan da hannu biyu ta juye shi tas akan Ummi. Kowa kuma sai ya bar abin da yake yi aka tsaya kallo.

    Ummi bata gama dawowa hayyacinta ba Hamdi ta cakumi wuyanta ta soma kai mata duka. Dambe sosai ya ɓarke a tsakaninsu inda Hamdi ta dinga tumurmusata da ƙasa. Tunda kayanta a jiƙe suke sai jikin ya yi futu-futu kamar an tonota daga rami. Ƙawayen Ummi da suka ji ta fara neman ceto ne su ka ƙwaceta sannan su ka yiwa Hamdi taron dangi. Mutum uku ne su ka danneta a ƙasa suna duka. Ƴan hostel ɗinsu na ganin haka su ma suka saka hannu wurin kai mata ɗauki. Wurin ya hargitse aka dinga ɓarin ruwa ana doke doke.

    Prefects ma basu iya yin komai ba sai malamai da aka kira. Duk wadda take waje a lokacin da ƴan kallo da ƴan dambe aka tasa ƙeyarsu sai ofishin Principal.

    Baiwar Allah ji tayi kamar ta fasa ihu da taga yadda yaran nan su ka ɓannatar da ruwan da ta wahala wurin nemowa. Ba’asi guda ta nema shi ne su waye su ka fara faɗan. Aka nuna Hamdi da Ummi. Ta karɓi bulala kuwa ta zane musu jiki ta zauna tana haki. Mataimakinta ne ya karɓi shari’ar saboda abin mamaki yau Hamdi yake gani kuma wai ita ta fara faɗan. Duk yadda aka yi a sanin da ya yiwa shaiɗanci na Ummi ya san laifin ba zai wuce nata ba.

    Masu tarar aradu da ka ya haɗa da displine master sannan ya zauna sauraron abin da ya haɗa yan matan. Ummi ta kitsa ƙarya da gsskiyarta ita kuwa Hamdi ko tari bata yi ba. Mutumin nan ya kaɗa ya raya amma ƙememe taƙi magana. Sai ajiyar zuciya kawai take saukewa. Waje ya tura su ya tattauna da malamai. Kowa ya riga ya san halin Ummi da Hamdi. Duk da haka tunda Principal tayi rantsuwa ya ce a dubo lambobin iyayensu a sanar dasu ana nemansu washegari Juma’a. Duk wanda bai zo ba ƴarsa ba za ta yi jarabawar da za a fara ranar litinin ba.

    Hamdi a yau ko a jikinta. Ta riga ta sanyawa zuciyarta ɓoyon uba bashi da wata fa’ida. Da tun farko ma an san shi Ummi bata isa tayi amfani da wannan damar akanta ba.

    A ɓangaren Ummi ne dai hankalinta ya nemi gushewa. Ƙaryarta ce za ta ƙare nannda ƴan awanni. Kiran iyayenta ba baƙon abu bane ko kaɗan. Inda gizo ke saƙar dai shi ne wani Sugar Daddy ɗinta ne yake zuwa a matsayin kawunta. Wai ita marainiya ce. Baba Maje da ke kawota kuma yaron kawun nata ne. Har ila yau baban nata yana karɓar wayarta duk ranar komawa makaranta tun da aka bata wayar. Wadda take amfani da ita ba tare da sanin hukumar makarantar ba wata ƙawarta take bawa ajiya. Babbar waya ce da wani saurayin daban ya saya mata. Tun kafin a dawo taje gidansu yarinyar ta tura wannan bidiyo ɗin da ta yiwa Abban Hamdi. Idan ta kuskura ta bari aka kira wani ba mahaifinta ba Hamdi za ta sami damar da ta zarce wadda ta samu ta cusguna mata. Gumin da ya tsatstsafo mata ta yarfe kafin ta tashi da rawar jiki taje ta sanar da Vice Principal numbar da zai kira a madadin wadda su ke da ita.

    ***

    Ɗokin da ya kama shi tunda aka yi sanarwar jirgi zai sauka nan da mintuna kaɗan ya bashi mamaki. Belt ɗin da aka ce fasinjoji su ɗaura ya gyara gami da leƙa tagar jirgin. Garin Kano yake gani da tsakar rana ƙarfe biyu da rabi. Tsirarun bishiyoyi da yalwar ciyayin damina sai gine gine marasa tsayi ba kamar inda ya baro ba. Tayoyin jirgin na dira ƙasa sabon yanayi ya baƙunce shi na farinciki da tarin fargaba. Uwayensa da ƴan uwa tun a waya su ke nuna farincikinsu. Alhaji ne damuwarsa. Zai karɓe shi ko kuwa yanzu ma zai cigaba da nuna masa ƙyama kamar wanda yake aikin saɓon Allah?

    *

    Kafin kowa ya kula wata matashiya dake tsaye tare da iyalan Alh. Hayatu Sule ta hango Taj ta cikin ƙofar gilas. Kyakkyawan saurayi ne wanda duk hangen mace indai ta same shi ta sake ɗaga ido neman wani dole a sanyata a sahun marasa wadatar zuci. Yana kama da ƴan uwansa amma akwai wani abu dake tattare dashi wanda ya bambanta shi dasu da take iya gani. Ba hasken fata bane domin wasu cikin ƴan uwan nasa sun fi shi haske. Haiba da cikar halittarsa su ne suka fi komai ɗaukar hankalinta. Tana can duniyar saƙe saƙe bata kula da yadda ƴan uwan nasa da ƴaƴansu su ka bar wurin ba domin tararsa sai daga baya.

    Idanu kansu su ka dawo ganin yadda ake pasin-pasin wajen rungumar Taj. Gashi taron mata don Ahmad da Kamal ne kaɗai maza in ka cire jikokin gidan da ba wani sabo suka yi dashi sama da waya ba. Bishir da Abba su na makaranta.

    “Aunty Salwa mu je mana.”

    Wani yaro ne ya yi maganar yana jan hannun matashiyar budurwar da Taj ya sacewa zuciya farat ɗaya. Murmushin jin kunyar kanta tayi ta kama hannun yaron su ka matsa kusa dasu. Yaron ya saki hannunta ya koma wajen Ahmad yana cewa ya ɗaga shi zai ga Uncle Taj.

    “Daddy ni bai ganni ba. Ɗaga ni sama.”

    Kamal ne ya ɗaga yaron ya miƙawa Taj. Ya karɓe shi ya rungume yana sumbatar kumatunsa.

    “Babana da kansa.”

    Yaron ya girgiza kai “Uncle Taj sunana Hayat.”

    “Ba Hayatu ba?” Taj ya ce da alamun mamakin da yasa yaron saurin cewa “Hayat yafi daɗi.”

    Dariya kowa yayi sannan Ahmad ya ɗan turo budurwar nan gaba.

    “Ga Salwa ku gaisa.”

    Taj ya sakar mata murmushi domin kuwa ƙanwar yayansa Ahmad ce da su ka haɗa uwa. A yanzu haka sakamakon karatu da ya kawota Kano daga Bauchi garin da mahaifiyar tasa ta sake aure shi ne take zaune a gidansa. Shekararta ta biyu kenan a Kano kuma iyalin Alh. Hayatu har matansa basu nuna mata wani abu da zai sosa zuciyarta ba. Ƙanwar ɗansu ita ma ƴarsu ce.

    Shi Ahmad matarsa ɗaya da yara biyu. Hayat da ake kira da sunansa bisa umarnin Alhaji sai jaririyar da ko arba’in ɗinta ba ayi ba mai sunan Mama wato Aisha.

    Ɗunguma su ka yi a motoci huɗu su ka nufi gida. Mazan motarsu ɗaya su kaɗai. Kamal ya yiwa Taj bayanin cewa sun canja shawara zai zauna a gidan Ahmad har lokacin komawarsa.

    Jikinsa a sanyaye ya tambaye su “Alhaji ya ce kada na zauna masa a gida ne?”

    “A’a” Ahmad ya faɗi da sauri.

    “Yaya ka faɗa masa gaskiya mana.” Cewar Kamal dake tuƙi “ɓoyewar bata da wani amfani.”

    “Faɗa min me ya ce Happiness.”

    Tiryan tiryan kuwa Kamal ya faɗa masa yadda Alhaji yaje ɓangarensu har ɗaki ya ce yaga saƙon Taj na tahowa buɗe gidan abinci. Ba zai hanasu mu’amala da ɗan uwansu ba amma indai da niyyar cigaba da saɓa masa ya dawo ya nemi wurin kwana.

    “Amma ya amince ka shiga gidan ka gaishe da su Hajiya. Kawai dai kada ka bari ku haɗu.”

    “Zan zauna a hotel.”

    Dukkaninsu kallonsa su ka yi. Ba kuma don abin da ya ce ba, yadda muryarsa ta fito kai ka san ba ƙaramar dauriya ya yi ba. A shaƙe take da wani irin rauni daga zuciyarsa.

    “A gidana za ka zauna. Tun jiya nasa Salwa ta gyara maka ɗaki.” Ahmad dake baya ya zura hannu gaban motar ya ɗan bubbuga masa kafaɗa.

    “Ba zan zauna na takura iyalinka ba. Infact mutumcina ma zai zube. Kawai bamu taɓa haɗuwa ba sai da aka koreni daga gida for the second time.”

    Dariya Kamal ya yi “zaman hotel ɗin ba matsala bane amma ba mutumcin aljihunka bane gaskiya a garin da kake da gidan ƴan uwa sama da hamsin da za su so zamanka tare dasu.”

    Kamar shi ya kar zomon, Taj ya ɗaure fuska ya ce masa “kawai ka faɗi abin da yake ranka. Kana tsoron kada naje ace na fara bin mata ko?”

    “Ba a ji mutuwar sarki a bakina ba, amma dai kai da kake kan tsini idan ka ƙara da kwanan hotel ban san yaya za ku kwashe da Alhaji ba.”

    “Allah ni ba ɗan isk* bane. Saboda tsoron kada Alhaji ya yi min baki watarana na lalace ko girlfriend na kasa yi.” Taj ya amsa defensively.

    “Daga budurwa sai lalacewa Taj?” Cewar Ahmad, shi da Kamal su na dariya.

    Shi kuma Kamal ya ce “dama me za kayi da busassun turawan nan da ba su da gaba da baya?”

    Haɓa Taj ya riƙe yana kallonsa kafin ya ce “Yaya kaji irin zancen banzan da Happiness yake yi ko? He is long overdue for marriage.”

    “Da za ku yi auren maybe da ka samu daidaitawa da Alhaji.”

    Hirar tasu sai ta koma ta dacewar Kamal da Taj su nemi mata su yi aure haka nan. Da haka su ka isa gida. Sai dai kafin maigadi ya buɗe musu gate motar Alhaji ta tsaya a bayan tasu.

    “Alhaji ne” Ahmad ya faɗawa Taj.

    Zuciyarsa ya ƙarfafa ya fita daga motar duk da tunin da yayunsa ke yi masa akan gargaɗin Alhajin na baya son ganinsa. Da sassarfa ya isa bakin motar da gilasanta duka baƙaƙe ne. Ba a sauke ko ɗaya ba a ciki amma ya tabbatar daga cikin ana ganinsa. Direba ke tuƙin motar amma da dishi-dishi yana iya hango Alhaji zaune a baya. Ya taka har bakin tagar ɓangaren nasa ya durƙusa cike da girmamawa.

    “Sannu da zuwa Alhaji.”

    Tun a hanya jikinsa dama ya bashi zai ga ɗan nasa. Tunaninsa ne ma ya hana shi gama uzurin da ya fitar dashi. Yanzu da yake ganinsa kewar Taj ɗin ta mamaye zuciyarsa. Idanunsa su ka tara ƙwallar da yake jin abin kunya ne a ganshi da ita. Saboda haka bai ɓata lokaci ba wurin umartar direbansa da ya yi ribas su bar wurin.

    “Alhaji ka daure ka saurari yaron nan don Allah.”

    “Koma na ce!”

    Direba ya so yin musu Alhajin ya manta da dattijantakar mutumin ya daka masa tsawa. Wannan yasa shi danna accelerator bayan yasa giya a ribas da ƙarfi. Ƙura kuwa ta tashi ta baɗe Taj da yake durƙushe har lokacin bai motsa ba.

    Ba shi ya tashi ba duk da magiyar su Kamal da wasu cikin matan da su ka riga su dawowa daga airport. Anyi a idonsu ne saboda an buɗe gate. Kuma dama Kamal na yin horn su ka firfito tare da iyayensu.

    Ahmad ne ya ɗaga shi zai shiga dashi gidan ya cije ƙafarsa.

    “Mu je gidan naka.”

    “Kaga su Umma fa a tsaye. Mu ƙarasa ku gaisa sai mu tafi.”

    Kai a sunkuye Taj ya girgiza kai.

    “Wallahi ba zan shiga gidan nan ba sai ranar da mai shi ya kirani ciki da kansa.”

    Motar ya kama zai buɗe Kamal yayi saurin danna lock da muƙullin hannunsa.

    “Kada kayi taurin kai. Don Allah ka shiga ciki.”

    Kai Taj ya ɗaga ya hango Salwa a tsaye tare da sauran. Bai yarda ya haɗa ido da kowa cikin matan gidan ba ya ƙwala mata kira.

    “Salwa…”

    Gabanta ya faɗi, zuciyarta tayi wani irin bugu. Sai kuma wani irin ɗumi mai daɗi ya lulluɓe mata jiki da ta tuna sunanta kaɗai Taj ya ambata a wannan yanayin da yake ciki. Ƙafafunta kusan da ikon kansu su ka ƙaraso da ita gabansa.

    “Kai ni gidan Yaya a rickshaw (haka ake kiran adaidaita sahu a India).”

    Alamun rashin fahimta ya gani a tare da ita ya nuno mata guda da ya shigo layin nasu.

    Kai Ahmad ya girgiza domin hanata sannan ya umarci Kamal da buɗe motar. Da kansa ya tura Taj baya ganin ƙanin nasa ƙiris yake jira ya saki ƙwallar da ta rufe masa idanu.

    “Kai shi gida zan taho.”

    Haka kawai ya ce da Kamal ya buɗe gaba ya ce da Salwa ta ɗauki Hayat su bi shi. Suna tafiya shi da sauran suka koma ciki.

    “Korarsa ya sake yi?” Umma ta tambaya da kukanta.

    “A’a. Ku shirya mu je gidana ku gan shi.”

    “Me ya faru Ahmad?”

    Mama da Hajiya duka kuka su ke yi. Inna kuwa jingina tayi da ƙofar shiga gidan ta runtse idanunta. Da yake duk da mayafi su ka fito Ahmad buɗe motarsa da ya bari a gidan ya yi ya ce su shiga.

    “Alhaji zai yi faɗa Ahmad.”

    Da mamaki mai haɗe da ɗimbin takaici Mama ta kalli Inna da tayi maganar baki buɗe.

    “Sau tari damuwar uwa da jajircewarta na taimakawa wurin ragewa ƴaƴa raɗaɗin hukuncin uba. Kina tsammanin akwai riba idan duka ku biyun kun juya masa baya? Ko kuwa kina ganin yin hakan wata gwaninta ce da Alhaji zai yaba?”

    Umma dama tafi kowa zafi kuma maganarta indai akan gaskiya ne ba kasafai take taunata ba.

    Jiki ba ƙwari Inna ta ce “ba haka bane.”

    Umma ta ce “to yaya ne? Sama da shekara goma rabon da ɗanki ya sanya ki a ido zahiri. Banda ma Allah Yasa Takwara (da yake haka su ke kiran juna da Amma) jajirtacciya ce da tuni ɗannan ya bi duniya. Uwa da uba a raye amma kun bar masa wawakeken giɓi mai wuyar cikewa. Baku san ku yabi ƙoƙarinsa ko kuyi masa faɗan kuskure ba.”

    “Kiyi haƙuri don Allah” Inna ta ce tana kuka sosai.

    “Magana ce ta gaskiya. Kin goyi bayan miji kun mayar da yaro marayan ƙarfi da yaji. Yau ko ɗan kafin Fatiha ya kawo muku gida wannan hukuncin ya yi tsauri, balle girki. Mene ne aibun girkin nan ne? Har mamakin ki nake yi idan kina sha’anin gidan nan kamar babu abin da yake faruwa.”

    “Jamila ya isa haka don Allah. Na tabbata tana da dalilinta na yin duk abin da tayi tunda ita tayi naƙudar Taj. Ta fi mu son sa.” Hajiya ma ta gwaɓa tata maganar.

    Kukan Inna ya sake tsananta da wannan rashin fahimta da abokan zamanta su ka yi mata. Ita fa tun lokacin da taga auren Mama yana girgiɗi a dalilin Taj hankalinta ya yi mugun tashi. Balle da aka zo sulhun nan ta fahimci ashe su Hajiya ma dake gidan sun daina girki. Wannan dalilin yasa ta sauke dukkanin tijarar da ta tanadarwa Alhaji. Domin tana da tabbacin muddin ya sallameta akan Taj su ma za su gwada masa rashin goyon baya. Ƙarshenta cikin fushi aurensu ya sami matsala. Indai ba butulci ba kuwa irin zaman da su ke yi a gidan bata jin ya kamata ta yi musu sakayya irin wannan.

    Zafin da taga sun ɗauka ne ya bats damar yi musu wancan bayani yadda za su fahimceta.

    “Kuna ganin rayuwar Taj za ta yi albarka idan sanadinsa gidan nan ya wargaje? Fushi irin na Alhaji nayi imanin sallamarmu duka lokaci guda ba zai yi masa wahala ba. Sai dai ya yi nadama daga baya. Sannan gabaɗaya yaran gidan nan da wuya su sake yiwa ɗan uwansu kallon mutumci. Da farin gashinmu a ka ace muna zawarci.”

    Allah Sarki. Tana rufe baki Umma ta rungumota.

    “Ki yi haƙuri Abullen Alh. Hayatu. Shaiɗan yaso amfani da ɓacin raina ya haddasa mana fitina.”

    “Sunan da ki ka kira ni dashi na mene ne kuma?”

    “Na ƙaunar rigimammen tsohon nan mana.”

    Dariya su ka ji an kwashe da ita. Shaf sun manta da ƴaƴansu dake wajen a tsaye. Kowa da jan ido an sha kuka suke dariyar daidaitawar iyayen nasu. Da wannan kuma babbar ƴar gidan Yaya Bintu ta sanar da ƴan uwanta cewa babu masifa da za su bari ta shiga gidan sama da rabuwar kawunansu. Don haka kowa ya shirya abin da zai iya domin taimakawa Taj. Haɗin kansu kaɗai zai iya sassautawa mahaifinsu haƙƙin ɗansa da yake ɗauka.

    Zaman lafiya aka ce yafi zama ɗan sarki. Alhaji bai san cewa duk cikim alkhairansa na duniya yadda ya gina gidansa shi ne mafi girman arziƙinsa ba. Gashi yana neman ɓata abin sa da hannunsa.

    Motar Ahmad su ka shiga ya kaisu gidansa. Sai ga Taj ya manta da dukkanin damuwarsa da ya ganshi tsakanin uwayensa.

    ***

    Abba ya maimaita zancen da yaji daga Vice Principal yafi a ƙirga a zuciyarsa bayan sun gama waya. Abin ne bambarakwai wai namiji da suna Hajara. Ta yaya ma za a ce Hamdi tayi dambe har ta kai rashin zuwansa akan matsalar zai iya jawo mata kora? Hamdi ce fa. Yarinyar da ko a cikin ƴan uwanta lokacin ƙuruciya da wuya a kawo ƙararta.

    Damuwar da su ke ciki shi da Yaya akan matsalar tashinsa da aka yi daga wurin sana’a sai ta zama ba komai ba. Fatan wayewar gari kawai yake domin yaje ya ji me yake faruwa. Sai dai kuma hantsi na soma leƙowa yaji wani irin tashin hankali. Da hankalinsa ya riga ya san yadda yaran ke kunyar nuna shi musamman ita Hamdi. Shin za ta yi maraba da amsa kiran nasa ko kuwa?
    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!