Rayuwa Da Gibi – Chapter Four
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Auren Habibu da Jinjin ba na son zuciya bane kamar yadda ƴaƴansu suke hasashe. Yar mahaifinsu da suka fi ɗorawa alhakin saboda sunanta da Zee tace wato Anti Zinatu ma ba laifinta bane. Abu ne na karamci da sanin darajar wanda ya kiyaye taka darajar.
Aure ne na zumunci domin kuwa kamar yadda Iyaa da Baba Maje suka fito daga zuri’a ɗaya su ma iyayensu mata shaƙiƙan juna ne. Mahaifiyar Habibu ita ce babba. Tayi aure a Kano da ƴaƴanta maza uku da mata biyu. Shi ne na biyu. Ita kuwa mahaifiyar Jinjin a garinsu Ɓatagarawa dake Katsina tayi aure. Bata sami haihuwar ba da wuri sai akanta. Ta haifota kyakkawa mai kama da dangin mahaifiyar. Idan ka ganta da ƴaƴan Inna Batulu za ka rantse ita ta haife su duka. Sunanta Khadija amma ake kirantan Jinjin (jinjinniya don ƙauna). Soyayya da gata gwargwadon hali ta taso tana gani wurin uwa da uba kafin Allah Ya jarabceta da cutar shan inna tana da shekara biyu da rabi. Lokacin da iyayen su ka farga ƙafar ta mutu ba ƙaramar damuwa su ka shiga ba. Idan tana tafiya kafaɗa da ɓangaren ƙirjinta na dama sai ya ballaƙo waje. Wannan abu ya tsayawa uban a rai. Har ta kai indai yana wajen da ta miƙe zai ce,
“Don ubanki koma ki zauna. Kina faman tafiya kamar wata tsuntsuwa babu kyan gani.”
Ko ya ce “wannan da ma ciwon tafiya ya yi dake kika huta. Meye haka don Allah?”
Da bata da wayo uwar ke kuka idan yana wannan rashin albarkar. Ƙarshe ma yayi aure shi da matar da lafiyayyun ƴaƴan da su ka haifa su ka taru su ka mayar da rayuwar Jinjin ƙuntatacciya. Yanzu ita ke kukan uwar na rarrashi. Watarana Inna Batulu ta kawo musu ziyara ta tarar da ƴaƴan kishiyar ƙanwarta suna dukan Jinjin. Abin takaici uwarsu da ƙanwar na kusa amma wai kawaici ya hana ta ƙwaci ƴarta. Garin cangala ƙafa ta kifar da garin masarar tuwon dare. Kuma gudu ma take saboda an biyota za a ci zali.
Inna Batulu na gani tayi kukan kura ta damƙo yaran nan su uku ta bi kowa ta feffela musu mari. Ta ƙare musu zagi irin nasu na Katsinawa.
“Banda raini ba yayarku bace?” Ta juya ga ƙanwarta “shiga ki haɗo min kayanta yanzu zan wuce da ita tunda ba kya so.”
“Ba haka bane Yaya.”
Da takaici takalleta “kunyar marasa kunya asara ce Luba. Gidan nan kaf har mijin naki ban ga wanda ya dace ki ragawa akan kyautar da Allah Ya yi miki ba.”
Jijjiga Jinjin tayi a gabanta ta ƙara da cewa “don bala’in gidan nan ƴar shekara goma sha uku ji ƙirjinta kamar anyi daɓen siminti.”
“Kai Yaya Talatu?”
“Allah kuwa. Zuwa yanzu ai yaci ace an fara ganin…”
Da ɗan gudunta Jinjin ta bar wajen don bata son ƙarasa jin hirar iyayen.
Kamar wasa maigidan na dawowa Inna Batulu ta sauke masa nashi kwandon masifar ta ce kuma jiransa take a bata ƴa.
“Gata nan har abada da gaban abada na bar miki.” Ya furta ko ajikinsa.
Luba sam bata ji daɗi ba amma haka ta shirya mata kaya su ka tafi. Bata da wani farinciki ko nishaɗi a gidan idan ba Jinjin take gani ba. Da ita take hira tunda miji ya juya mata baya. Sauƙinta ɗaya ta san cewa yanzu za ta sami ƴanci ta wataya kamar sauran yara.
A Kano tabbas taga gata da soyayyar da tasa har take manta da nakasar dake tare da ita. Inna Batulu da maigidanta harma da yaransu sun mayar da ita ƴar gata. Matsala guda ta kula akwai a gidan ita ce ta yayanta Habibu. Lokacin yarintarsu tana iya tuna shi da yawan wasa da dariya. Yanzu kuwa kullum iyayensa cikin kukan sabuwar ɗabi’arsa suke yi.
Shi ne tafiya yana rangwaɗa da karairaya jiki kamar mata. Ga uwa uba muryarsa da bata san ya aka yi ta motse ba. Idan ya yi magana sai ka rantse wata budurwar ce. Duk wasu take taken daudanci yake nunawa. Indai zai yi sallama a gidan daga su Inna Batulu har ƴan uwansa basu da nutsuwa.
A yau da take da kusan wata biyu a gidan sallamar wata matashi suka ji a gaggauce. Babu kowa a gidan sai Jinjin da ta dawo daga makarantar islamiyya. Fita tayi ko kaya bata cire ba ta sami wani mutum da bata sani ba. Da gani magidanci ne ya sha shadda wagambari da ɓakar ɗara a ka.
“Inna Batulu ko Baba nake nema” ya ce kafin ta gaishe shi.
“Duk basa nan.”
Kallonta ya sake yi ya tuna sun taba shiga gidansu wurin iyayensa da Inna Batulu tace ƴarta ce daga Ɓatagarawa. Shi yasa kawai ya faɗa mata abin da ya kawo shi.
“Ki ce musu Habibu na gani a gidan abincin wasu ƴan daudu yana girki a kasuwa.”
Rasa abin cewa tayi don fuskar mutumin tayi nuni da matsanancin ɓacin ran da ganin hakan ya janyo masa.
“Kin fahimci abin da nace kuwa?”
“Eh, zan faɗa musu in sha Allahu.”
Juyawa ya yi babu sallama zai tafi ta tambaye shi wa za ta ce musu.
“Hayatun gidan Alh. Sule.”
Sunan da taji bayan tafiyarsa ya dawo mata da hirar da ta taɓa tsinkaya daga mutan gidan. Akwai gidan wani mai kuɗi nan kusa dasu wanda aka ce ɗansu Hayatu ya ɗauki Habibu tamkar cikinsu ɗaya. Saboda ladabi da ƙoƙarinsa a shekarun baya ya kasance duk wata lalurar karatunsa Hayatu ya ɗaukarwa kansa. Irin abin nan na maikuɗi ya cicciɓi talaka domin inganta masa rayuwa. Ance da Habibun ya fara canja akalar rayuwa Hayatu ya shiga ɓacin rai sosai. A son sa yaron ya ginu ya zama mutum amma kullum ana yi masa faɗa yana daɗa kangarewa. Me za ayi da namiji mai girki a ƙasar hausa? Har dukansa taji ya taɓa yi watarana da ya ganshi da ɗaurin zani a ƙirji ya fita. A ƙarshe ya ce masa zai iya tsaya masa ya koyi girkin harma ya mayar dashi sana’a amma sai ya ajiye duk wani abu da yake kamanceceniya da mata. To Habibu dai ana faɗa ta kunnen dama zancen na ficewa ta hagu.
Da Inna Batulu ta dawo ta sanar da ita sai da tayi kuka. Shi yasa ba a son zama unguwa ɗaya da wanda ake ganin zai iya jan ra’ayin yaran unguwa. Daga yawan aikensa siyan abinci a wurin wasu ƴan daudu dake bakin titi ita dai bata san yadda aka yi ya dinga rikiɗewa ya koma wannan Habibun na gabansu ba.
Ranar anyi masa faɗa sosai. Baba ya zage ya yi masa dukan mutuwa. Garin Allah na wayewa aka neme shi aka rasa. Wurin wata uku ana nema kafin daga bisani su sami labarin ya tafi Saudiya da wani ubangidansa. Sana’ar abinci su ke yi a can ɗin.
Akwai abubuwa da kan sami bawa ya rasa silarsu. Ka haifi ɗa kayi masa duk iyakar ƙoƙari amma idan ƙaddara ta faɗa masa kana ji kana gani zai zaɓi hanyar ta bata ɓullewa. Irin haka ta sami Habibun Inna Batulu. Dangi su ka sanyo su a gaba da yawan magana da famin ciwo. Wasu in sun sami zuwa ƙasa mai tsarki a unguwar su yi ta kawo labaran yadda aka ganshi ya ɗashe saboda shafe shafe. Zantuka barkatai harda wanda ya ce wai an faɗa masa ya yi aure da wani ɗan daudu irinsa.
Zancen da ya tayar da hankalin Baba fiye da kowanne kenan. Ya sayar da gonarsa da wani gidan haya ya haɗa kuɗi a shekarar ya tafi Hajji. Bai wani sha wahala ba aka sada shi da gidan da Simagade yake haya da abokan sana’arsa. Lokacin shekararsa tara baya gida. Jinjin ta gama sakandire har ta fara sana’ar kitso a gida tunda aure ya gagara. Ta kai matakin da kowane iri tana son samu saboda yadda mahaifinta ke jifanta da maganganu idan taje gida.
Baba fashewa yayi da kuka da yaga ɗan nasa sanye da jallabiya ya ɗora zani da ɗankwali. Ga haƙoran Makka har biyu. Tamkar ba a Jidda ba suna ta ƙazaman zage zage shi da wani da suke faɗa. Ganin mahaifinsa ne ya sagar masa da gwiwa ya yi shiru. Sai hankalin kowa ya kai kan tsohon dake zubar da hawaye.
“Shiga ka sako kaya ka zo ka rakani masallaci.”
Ba Habibu ba hatta abokan zamansa duk jikkuna sun yi sanyi. Ya shiga ciki ya samo aron wasu pakistan na maza ya saka. Ya fito tafiyar nan babu dama ne. Masallaci mafi kusa Baba ya shiga dashi. Ya umarce shi da yin sallah raka’a biyu sannan ya fuskance shi bayan sun idar.
“Saboda ka taka dokar Allah Habibu yau alwala da sallarka ma in ni nake karɓa ba za su bar rufin masallacin nan ba zan jeho maka kayarka.”
Kai ya sunkuyar cike da kunyar kansa.
“Daga wannan rana ba zan sake yi maka faɗa ko nasiha ba. Zan kuma roƙi Batulu da kada mu sake zubar da hawaye a kanka. Na barka da duniyar da ka zaɓa wadda nan da kwanaki kaɗan za ta daina yayinka. Idan tayi maka rawar ƴan mata ina jin za ka yi hankali har ma kayi tunanin dawowa gida. In na mutu tun yanzu ka sani na yafe maka. In kana da rabon shiriya ka zo gida kafin baƙincikinka yayi ajalin mahaifiyarka.”
Yana gama faɗin haka ya tashi. Habibu zai bi shi ya ce baya so. Haka ya koma ya gama kwanakin da su ka rage ya dawo gida. Habibu kuwa komai ya daina yi masa daɗi. Nadama mai raɗaɗi ta shiga ɗawainiya dashi. Ana gama kwaso mahajjata ya tattara komatsansa ya dawo gida.
Bai fi wata biyu ba Baba ya kama cuta har ya cika. Yayi kuka kuwa kamar ba gobe. A gefe guda yana godiya ga Allah da Ys bashi damar dawowa. Tun daga lokacin ya soma neman gyara rayuwarsa. Sai dai kuma jama’a da dama suna gagarar yiwa mai laifi uzuri ko ya tuba. Da yake har yanzu in ba jallabiyar nan ya saka ba sai yaji kamar yayi tsirara, amma yana bakin ƙoƙarinsa wurin yin abin maza. Matsalar dai an bar kari tun ran tubani. Murya ta gama shaƙewa. Karairaya ta zame masa jiki duk da ya rage. Ya yi ta neman aikin yi ya rasa. In ya kasa kayan sayarwa irinsu kayan miya babu mai saye. Har wurin Hayatu yaje amma yaƙi taimaka masa ya zama yaron shago kamar yadda ya nema. Allah Ya ɗora masa ƙyamar ƴan daudu sosai.
Da ya rasa yadda zai yi ne ya roƙi Inna Batulu ta yarje masa tafiya Lagos sayar da abinci. Ya tabbata a can da babu wanda ya san shi kuma girki ba a ɗauke shi sana’ar mata kaɗai ba zai sami sauƙi.
“Idan ka tafi Habibu ina jin tsoron kada ka koma ruwa. Gashi nayi imanin babu mai baka mata ka aura a halin da kake ciki.” Ta goge hawaye.
“Ki yafe min Inna. Na san na cuci kaina amma nayi miki alƙawarin ba zan komawa waccan rayuwa ba.”
Duk zancensu a kunnen Jinjin. Kafin tafiyarsu ta sake jin maganar ana yi tsakaninsa da ƴan uwansu. Ta kula Inna tana cikin damuwa. Barinsa babu abin yi matsala ne. Sannan zuwansa shi kaɗai akwai haɗari. Bayan dogon nazari irin na yarinta ta nemi izinin zuwa gida ta shawarta da mahaifiyarta. Luba ƴar halak ko mijinta bata bi ta kansa ba ta sako ƴarta a gaba su ka taho Kano. A gaban ƴaƴan gidan da mahaifiyarsu ta ce ga amana ta sake damƙa musu.
“Jinjin miskiniya ce na sani. Ban sani ba ko bawa Habibu ita zai zama gwaninta ko abin ɓacin rai a gareku.”
“Allah Ya kiyaye Gwaggo Luba” cewar yayar Habibu tana taya Inna Batulu kuka don ta kasa magana.
Sun yiwa uwa da ƴar godiya kamar su ari baki. A wata guda aka yi komai aka gama su ka koma Lagos da zama. Rayuwar ta fara daɗi Allah Ya karɓi ran Innarsa. Shi ne dalilin dawowarsu kuma ya kasa komawa.
Habibu yana ƙaunar ƴaƴansa kamar rai. Yafi kowa sanin akwai lokutan da basa son nuna shi. Shiyasa ya kan kame daga zaƙe musu don kada ya ɓata rawarsa da tsalle. Matarsa Jinjin kuwa duk duniya baya haɗata da komai. Shi ya sani cewa tayi masa alfarmar da da ace ana auren ƙanwa ko ya nasa ba za su taɓa aurensa yana ɗan daudu ba.
**
Alh. Hayatu Sule Maitakalmi mashahurin ɗan kasuwa ne a Kantin Kwari. Takalma dai na mata da maza daga shagunansa an gama magana. Karansa ya kai tsaiko a kasuwanci. Sunansa ya zaga duk inda ya dace a dama da shi. Mutumin cikin ƙwaryar Kano ne daga unguwar Soron ɗinki. Yana da kirki da ƙoƙarin cicciɓa na ƙasa da shi sai dai akwai tsatstsauran ra’ayi kuma baya tanƙwaruwa. Duk wanda ya san shi ya san kaifi ɗaya ne kamar bakin wuƙa.
Matansa huɗu kuma duk a gida ɗaya suke. Ƙaton gini ne na masu kuɗin da wanda yake yawan shan gyara domin ya tadda zamani. Ainihin gidan akwai ƙaton falo wanda in an shiga da ƙofofi huɗu a jere a ɓangaren dama. Kowacce in ka shiga falo ne babba da banɗaki da kuma ɗakuna biyu. Nan me ɗakunan matansa. Bangon dake kallon ɗakunan kuwa kitchen ne makeke da store sai ɗakin masu aiki dake haɗe da banɗaki. A jikin bangon tsakiya ne da matattakalar bene inda ɗakin maigidan yake da falonsa. Sai kuma ɗakuna biyu na ƴan mata suma kowanne da banɗaki duk a saman. Sai an fita daga bayan ainihin ginin ne kuma za a tarar da ɓangaren samari. Ta gaba kuma aka jona ginin falo da banɗaki inda yake ganawa da baƙinsa. Duka gidan ƴaƴa ashirin da takwas ne kuma a ciki biyar ne kaɗai maza. Sai ƴaƴan ƴan uwa da yake riƙo da ƙannensa. Shi yasa kullum gidan yake a cike.
Uwargidansa ta lalle Haj. Gambo da ake kira Hajiya kaɗai tana da goma. Ta biyun Mama A’i tana da uku. Sai Umma Jamila mai takwas. Sannan amarya Inna Abu mai shida. Ya taɓa sakin mace ɗaya wadda ta kasance ta uku a jerin aurensa. Ɗa ɗaya ta haifa kuma shi ne babban namiji a gidan mai suna Ahmad. Da fitina ta zo shi kuma ba zai lamunta ba. Tun yana lallaɓawa da yaga za ta wargaza masa tsari ya sallameta ya bawa Mama ɗan. Tun daga lokacin babu wadda ta sake gigin tayar masa da hankali. Zaman lafiya ake da ƙullewar zumunci. Har ta kai idan mace ta haihu wani zubin ɗan cikinta ma sai ya yi mata ƙyuya saboda kulawar da yake samu a wajen yayyensa da sauran matan. Irin rayuwar nan ta daga ni sai ƴaƴana bata da muhalli kwatakwata a gidan Alh. Hayatu.
Bayan Ahmad an ɗauki lokaci kafin a sake samun ɗa namiji. Don a haihuwa ta tara Hajiya ta haifi Kamaluddin. Yana da wata biyar Inna ta haifi Tajuddin. Bayansa tayi mata biyu sannan ta ƙara da maza biyu Sulaiman (Abba) da Bishir sai ta rufe da mace kuma autar gidan. Wannan yasa mazan su ka tashi a ƙarƙashin yayunsu mata tunda sun zo a sahun ƙarshe ƙarshe.
Kamal da Taj sun tashi tamkar ƴan biyu sakamakon rashin tazarar haihuwarsu. Wasu har basa gane su don hatta pant duk mai sayawa ɗaya za ta sai wa ɗayan. Bambancinsu da aka fi ganewa shi ne doguwar fuskar Taj da gashin fulanin Kamal wanda su ka gado daga uwayensu. Da yake jinin Alhajin akwai ƙarfi duk inda ƴaƴansa su ke basa ɓoyuwa. Musamman da cikakkiyar girarsu da ta zama wani sirri na ƙarin kyawunsu. Mama uwar riƙon Ahmad ita ce maman mazan gidan. Duk abin da ya shafesu ita ce a kai tun ana goyonsu. Ita take yayesu shikenan yaro ya koma ɗakinta.
Za a iya cewa Taj da Kamal wasu manyan jigo ne na farincikin gidan Alhaji. Indai suna gida to in sha Allahu dariya da nishaɗi baya yankewa. Zolaya da wasa duk halinsu ne. Har suna su ka sanyawa juna. Kamal ya kira Taj Happy, shi kuma Taj ya kira shi Happiness. Irin faɗan nan na sakonni da wuya kaga sun yi. Sannan daga yayyensu har ƙanne ba za ka ji wanda ya kai ƙararsu akan sun masa ba daidai ba. Duk kuwa da kasancewar Taj mai tsokana lamba ɗaya. To amma yana da tsoron yin laifin da za a hukunta shi. Shi kuwa Kamal dama green snake ne. Sai ya yi abu ya koma gefe kamar ba shi ba.
Tun tasowarsu akwai wata irin shaƙuwa ta musamman tsakanin Alhaji da Taj. Shi dai da zarar mahaifinsu ya dawo to ya gama wasu wasanni. Yana daga cikin lokutan da akan gansu wuri daban daban shi da Kamal. A gefensa yake zama yana yi masa tambayoyi musamman akan kasuwanci. Nan da nan ya zama sunansa abokan harkokin Alhajin su ka fi sani. Kowa ya buɗe baki sai ya ce Taj. Har dai aka fara hannunka mai sanda a gidan ana cewa da alama shi zai gaji Alhajin. Yawan maganar yasa Inna ta fara jin abin yana damunta. Bata son rigima ta ɓullo daga ɓangarenta. Shi yasa wata rana su na zaune su biyu da Alhajin ta tayar masa da zancen.
“To ke banda abin ki mene ne a ciki? Duk uba ai yana son magaji a fannin da ya yi zarra musamman idan halattacce ne.”
Wasa taga ya mayar da zancen ta girgiza kai.
“Kaga yana da yayye. Idan ana cewa magajinka wani zai yi zaton irin abin nan ne na son ture wasu don wata manufa.”
Kallonta ya yi yaga sosai ta shiga damuwa.
“Ku mata sai a barku. Tunaninku kullum babu nisa. Musulunci dai ya riga ya gama mana komai. Yau ko dama na kwanta yadda shari’a ta tsara haka za a raba abin da na bari a bawa ƴaƴana. Babu wani fifiko.”
“Na sani”
“Amma duk da haka kina damuwa saboda kada a ce Hayatu ya fifita ɗanki akan na sauran. Ƙila ma kina ƙarawa da cewa za a zargi ko don mahaifiyarki ƙanwar mahaifina ce.”
“A’a wallahi” ta ce da sauri.
Ya sake yin murmushi sannan ya ɗan tuna mata baya. A gidansu cikin maza su goma sha uku shi kaɗai ne ɗan kasuwa kamar baban su. Sauran duk aikin gwamnati su ke yi. Shi kuwa ya ajiye kwalin tun daga degree na farko ya rungumi sana’ar gidan ba tare da an tauye ƴan uwansa da komai ba. Duk abin da ya tara yanzu arziƙinsa ne na guminsa. Ya ma zamana duka ƴan uwan nasa duk wanda ɗansa namiji ya gama sakandire sai ya tura masa shi kasuwa na shekara ɗaya. A haka yanzu akwai mutum bakwai cikin ƴaƴansu da su ke jikinsa.
“Zan yi maganin damuwar nan anjima idan an zo cin abincin dare.”
Bai manta ba kuwa. Dama al’adar gidan idan ba baƙi gare shi ba duka tare ake cin abinci a babban falo. Ƴan shekaru kusa da juna ake haɗawa a kwano guda. Matansa ma yawanci tare su ke ci. Ana gamawa yaran za su nufe shi da buƙatunsu. Ko fensir ne ya karye sun fi gane su sanar dashi. Yana daga zaune zai sa a bashi reza don yafi gane mata ya fiƙe. Wasu ya koya musu homework. Masu buƙatar kuɗi ko wani abu makamancin haka duk a wannan zaman ake yi. Ana gamawa zai ja su sallar Isha sannan ya tashi. Su kuma daga nan za su ɓalle da hira. Ƙananun da duk mai ra’ayi su tarkata su koma wurin Hajiya indai ba girkinta bane domin jin daɗaɗan tatsuniyoyi.
“Mal. Bishir wai me ka ke son zama ne idan ka girma?”
Bishir ya ɗago kai daga rubutun da yake yi na homework ya kalli baban nasu.
“Shoe shiner.”
Falon gabaɗaya aka bushe da dariya harda Alhajin. Shekarar Bishir bakwai a lokacin.
Kuka ya soma yi yana cewa “Alhaji kaga suna yi min dariya ko?”
“Rabu dasu. Tambayar ma ta saraya a kanka sai ka ƙara girma. Duk wanda ya sake dariya kuma bana bashi da takalmin sallah. Dama kai zan bawa ka raba.”
Da haka ya kawo ƙarshen kukan nasa. Ya mayar da tambayar ka ga Abba.
“Babana fa?”
Murmushi ya yi “Alhaji ni police zan zama.”
“Ni dai bana son khaki Abba. Don Allah ka zaɓi aikin da ba zai dinga hana ni bacci mai daɗi ba” cewar Mama.
Alh. Hayatu ya ce a ƙyale yara a bisu da addu’a.
“Taj kuma fa?”
Abin nema ya samu. Kowa ya zuba masa ido ana jiran a ji ya ce kasuwanci irin na baban nasa sai ya basu mugun mamaki.
“Chef! Mai girki.” Ya ce hankali kwance yana murmushi.
Da yake yafi kusa da Umma a inda yake zaune bata san ma lokacin da ta buge bakinsa ba saboda wani hargitsatsen kallo da Alhaji ya watsa masa.
“Bar dukansa Jamila. Barshi ya maimaita.”
Ko ɗar bai ji ba ya sake faɗin abin da ya ce da ƙwarin gwiwa.
“Chef. Mai dafa abinci a restau…”
“TAJUDDIN!!!”
Tsawar ta gigita kowa. Ƴar autarsu ma kuka ta saka harda zubar da abincin da aka ajiye a gabanta tana ci da kanta.
“Ku tashi ku bani wuri.” Ya faɗa a fusace.
Da yake a lokacin sun kai shekara sha huɗu shi da Kamal duk da hankalinsu. Shi yasa Taj ya gane abin da ya faɗa bai sami karɓuwa ba. Bin sahun ƴan uwansa ya yi ya tashi.
“Ina za ka? Zama zaka yi ka faɗa min me ya burge ka da daudanci har kake tunanin kawo min wannan shaiɗancin cikin gida.”
A tsorace ya zauna yana kallo kowa ya tashi har iyayensu mata. Alhaji ya ɗan sausauta murya don ji yake kamar ya fara duka akan ɗan da yake matuƙar danne soyayyarsa. Ya tambaye shi ko ya taɓa yin girki a rayuwarsa.
“Abincin da aka gama ci yanzu ma ni nayi miya. Wallahi Alhaji na iya girki sosai. Indai babu islamiyya ni nake na dare.”
Sai da ya cije leɓe don wani irin sarawa kansa ya yi sannan ya ce “kirawo min uwayenka ka ce su same ni a ɗaki.”
***
A ɗakin Hajiya su ka tare su huɗu ashe suna ta caccakar Mama. Musamman Umma wadda ta jima da hango ɓacin rana a dalilin wannan abu.
“Na sha faɗa miki ki hana yaron nan shiga kitchen ki ka ƙi. Tun ana ɓare maggi har ta kai yana ɗora sanwar gidan nan.”
Mama da karayar murya ta ce “saboda Allah yanzu a ce mutum yana da yaro amma ba zai koya masa ayyukan cikin gida ba? Girki ai ba lallai sai mace ba. Kuma ra’ayinsa ne tunda duk yadda su ke da Kamal shi ko magin baya ɓarewa.”
Hajiya ta ce “Amma tun farko kin san Alhaji yaƙi jinin ganin mazan gidan nan da tsintsiya ma balle girki. Yana gani yake cewa a daina saka su kada su zama ƴan daudu. Ko kin manta tashin hankalin da aka taɓa yi akan gugar kuɓewa?”
Wata rana ne kusan shekara uku da su ka wuce mai aikinsu ta fita bata dawo da wuri ba. Girkin Hajiya ne ita ma sun fita dubiya dukkansu. Suna dawowa taga ba’ayi tuwon dare ba. Shi ne ta rabawa Ahmad, Kamal da Taj gugar kuɓewa ita kuma da taimakon yan matan gidan ta ɗora tuwo. Alhaji da ya shigo yaga suna aikin nan a falo ya dinga faɗa ba ji ba gani. Sai da ya yi sati baya cin abincin gidan yana kuma gargadi da tuna musu aikin namiji da mace a gida ba ɗaya bane.
Mama ta ɗan kalli Inna da tayi shiru kawai tana kallonsu.
“Ki ce wani abu mana. Ko kema laifina kike gani?”
“Laifi kamar yaya? Neman mafita kawai zamu yi kafin ya tasa mu a gaba don na san…”
Laluben ɗakin da Taj ya ɗaga da sallama ya katse mata magana.
“Alhaji yana kiranku a samansa.”
Hajiya kiransa tayi ganin jikinsa duk ya yi sanyi.
“Girki ko a gidanka kana da damar yi Taj amma kada ka sake cewa za ka zama mai abinci ko daɗin ji babu. Duk wani namiji mai sana’ar abinci ɗan daudu ne. Su kuwa Allah baya son su tunda sun zaɓi jinsi kishiyar wanda ya basu.”
Kai ya gyaɗa kawai ya fice. Sanin cewa zai haɗu da Ahmad da Kamal kuma lallai ba za su goyi bayansa ba sai ya gudu ɗakin Inna. Wuri ya samu ya kwanta ya rufe idanunsa yana tunani.
Kasuwanci da yake nacin koyo a wurin Alhaji ba don komai bane sai don yana da muradin buɗe gidan abincin da yake son ya yi suna. A rayuwarsa babu inda yake shiga yaji kamar an sabunta masa duniya kamar kitchen. Kuma a iya saninsa maza da yawa su na girki. Suna da shekara goma Alhaji ke kai yara Umra. Idan mutum ya yi shabiyar a kai shi Hajji. A Saudiyya in ka cire Takaru babu inda ya ga mata suna sayar da wani abu na ci. Maza ke girkawa su sayar. Maza musulmai magidanta waɗanda basu da wata siffa da duk hangen mutum zai danganta su da mata. Idan sana’ar haramtacciya ce ga namiji da waɗannan basu kai labari ba. Shi kam yana son girki kuma in Allah Ya so ita ce sana’ar da zai yi.
A ɗakin Alhaji kuwa faɗansa har falon ƙasa. Don ma ƴaƴan kowa ya shige ɗaki. Manyan sun haɗe kawunansu da ƙananan a ɗakunan iyayensu a ƙasa.
Ya fusata sosai don ko da su ka shiga ɗakin maganinsa na hawan jini yake sha.
“Ni za ku ha’inta? Girkin nan ba yau ya fara ba tunda ya ce shi ya yi miyar dare. Ace ko sau ɗaya idanuna basu taɓa gani ba. Abin da mamaki.”
Mama ce ta fara bada haƙuri “na bari ne kawai saboda ganin yawanci gidajen da su ke da yara maza duk ana koya musu girki. Hakan bai sa sun yi koyi da ɗabi’un mata ba.”
Cikin faɗa ya ce mata gidansa babu maza da yawa. A cikin mata ashirin da uku a rasa me yin girki sai maza? Shi yasa yake sanya ido sosai saboda idan ya yi sake tabbas mazan za su iya jin cewa kwaikwayon yayyensu mata ba laifi bane. Ko ɗankwali ya gani a hannun ɗansa ya dinga faɗa kenan.
“Da irin wannan sakacin wani yaro a unguwarmu ana ji ana gani wallahi ya zama cikakken ɗan daudu. Gidansu akwai mazan ma amma daga sai ga Habibu ya koma Simagade a unguwa.”
Gashi dai faɗa yake yi amma faɗin wannan suna sai da ya sanya Hajiya da Mama yin ƴar dariya. Umma da Inna dai a murmushi su ka tsaya. Ai kuwa sun janyowa kawunansu sabon faɗa. Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Musamman Mama da a yau tayi nadamar amsa sunan uwar maza a gidan.
“Dole ki yi dariya mana tunda ba ɗanki bane. Da alamu da gangan ma ki ka nemi ɓata min rayuwar yaro saboda baki san daɗin haihuwar namiji ba.”
Ba ita da ya yiwa gori ba, dukkaninsu hankulansu tashi su ka yi. Mama ta saka kuka, Umma da Inna su na taya ta. Hajiya kuwa fiƙe idanu tayi ta ɗauki ragamar girmanta.
“A’a fa Alhaji. Akan ƴaƴanka ba za mu lamunci irin wannan ba. Kai ka koya mana zama da juna. Tunda mu ka kai yanzu kuwa wallahi ba za mu yarda ka haddasa mana rigimar da bamu yi da ƙuruciya ba.”
“Ba akan ƴaƴana za ki ce ba. Ki fito fili ki faɗa min cewa akan Taj ba za ku yi min biyayya ba.” Ya dubi Inna ya cigaba da sababi “wato sai da ki ka ga lamari ya lalace sannan ki ka ankarar dani riƙon sakainar kashin da ake yiwa ɗana don kawai ana ƙyashin kusanci na da shi.”
“Na shiga uku. Alhaji yaushe mu ka yi haka?” Ta faɗi a ɗimauce ganin ƴan uwanta sun zuba mata ido.
Shi a ganinsa babu dalilin da zai sa taji wani ɗar a zuciyarta. Ya riga ya santa da kawaici saboda haka don ana yabon ɗanta a tunaninsa bai isa dalilin maganarsu ta ɗazu ba. Tabbas ganin rayuwarsa ta ɗauko hanyar gurɓacewa a hannun uwar riƙonsa shi yasa tayi magana.
Su Hajiya ficewa su ka yi aka rasa mai tambayarta abin da ya faru ma. Tana kuka ta tashi za ta bisu domin kwance wannan ɗauri da maigidan ya yi mata ya hanata fita. Dama girkinta ne. Sai kawai ya ce idan ta fita daga ɗakin ba da yawunsa ba.
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
