Mayraah Part Complete
Cigaba From Part 54
Karanta Mayraah Daga part 1 zuwa Part 53 anan
Buy Cheap Data and Cables subscription from our platform just click here
Washegari da safe Mayraah na zaune dakin da aka bata bayan tayi wanka amma ko leka parlorn gidan ta kasa yi, tun da Dr Khalil yace mata gidansu matarsa ne ya kawota jikinta yayi sanyi ta kasa samun nutsuwa har gari ya waye, Karime ce ta shigo dakin da sallama, Mayraah ta gaisheta Karime ta amsa da fara’a tace “Hajiya na kiran ki a parlor” Mayraah ta mike sanye da hijab dinta ta fita parlor, da ladabi ta gaida Ummi, Ummi ta amsa tace “Baza ki je aikin bane naga baki fito ba har takwas yanzu” Mayraah ta sunkuyar da kai tace “Zan je” Ummi tace “To ki shirya ki fito kiyi breakfast kafin nan driver ya dawo daga ajiye yara makaranta sai ya sauke ki asibitin” Mayraah tace “Toh Nagode” Daga haka ta mike ta koma dakin da ta fito, karfe takwas da rabi Mayraah ta sake fitowa parlor bayan ta shirya cikin uniform, tana fitowa Karime kadai ta tarar tana ta aikace aikace a parlon, Karime ta nuna mata dinning area tace “Ga kumallon naki can na kai maki” Mayraah ta mata godiya sannan ta karasa ta zauna, shayin ta hada, ta debi irish da kwai ta fara ci, ko bayan da ta gama breakfast din tana ta zaune parlor sai ga driver yana sallama bakin kofar parlor, Karime tace “Yauwa ga Dreban ya dawo, Hajiya ta shiga ciki ta kwanta tace ince maki Allah ya tsare” Mayraah ta mike tace “Toh nagode” Daki ta koma ta dauko handbag dinta da wayarta sai ledan scrub din ta sannan ta fito ta kara yi ma Karime sallama ta fita. Driver na ajiyeta bakin gate din asibitin ta sauka tace masa “Nagode” Yace “Allah ya tsare Hajiya” Daga haka ta shiga gate din asibitin. Kamar jiya yau ma haka Mayraah ta jigata a asibitin don daga shigowarta da safe wani Dr Balogun ya aika a kira ta zuwa theatre, ba kuma wani aiki tayi ba kawai surgical equipments suke kira by their names ita kuma babu bata lokaci take mika masu Instruments din, kuma ko sau daya bata yi mistake din ko daya ba, wani ma bata jira a tambaya take mika wa sanin function dinsa, 2 other senior nurses ne tare da likitoci biyu a theatre din giving them assistant, ba su suka fito theatre din ba sai bayan azahar, Dr Balogun na kallon Mayraah yace “Ur alma mater Madam?” Sosai gabanta ya fadi, sai ga wani Dr ya zo yana ma Dr Balogun din magana, sum sum ta bar wajen da sauri ta koma reception tana zare ido, Nurse Hafsat tace “Sai yanzu, sannun ku da aiki” Dai dai nan Wata nurse ta ajiye telephone din hannunta saman desk tana kallon Nurse Hafsat tace “Who is Nurse Ilham?” Nurse Hafsat ta nuna mata Mayraah, Nurse din ta kalli Mayraah ta sanar mata Dr Khalil na nemanta a office dinsa, Tun da Mayraah ta shigo asibitin basu hadu ba bata ma san ko ya zo ba ko bai zo ba, sai da tayi sallan azahar sannan ta tafi sama zuwa office dinsa, bayan ta shiga ta kulle masa kofa ta karasa har bakin table dinsa ta gaishesa, ya ajiye aikin da yake yi a laptop yayi mata izinin zama sannan ta zauna ta sake gaishesa ya amsa yace “You looked stressed, ai tunda kika bari Dr Balogun ya gano ki sai kinyi hakuri da shi, haka yake in dai ya lura nurse bata basa problem wajen aiki and she is composed kuma ta san abinda take shkkn duk zai yi aiki sai ya sa an nemo masa ita sai dai in bata duty ranan” Mayraah dai bata ce komai ba sai murmushi da tayi, yace “Nasan baki ci abinci ba ko?” Bai jira cewarta ba ya dau ledan takeaway ya mika mata, ganin bata amsa ba yace “Karbi mana” Ta sunkuyar da kanta tace “Bana son ina daura maka burden dina, i am suppose to get food my self ba wai ka siya min ba” Yace “Ki tambayi Nurse Hafsat in dai ban siya mata lunch ba to probably ban zo asibitin ba ko kuma bana duty ranan, i do this for most of the nurses, it’s nothing a wajena” Mayraah ta amsa a hankali tace “To Nagode Allah ya saka da Alkhairi” Yace “Ameen, ya kika baro su Ummi” Mayraah ta kallesa da sauri, sai kuma tayi kasa da murya tace “Amma me yasa zaka kai ni gidan in-law dinka?” Yace “Bayan in-law nima mamata ce ai, bani da kamar ta a duniya….” Kallonsa kawai Mayraah take, yace “Ina da shekara biyar Mom dita ta rasu ta bar ni gun stepmom dina, i still remember vividly the maltreatment from my stepmom, yes it is still in my memory, duk abinda tace shi Dad dina yake yi ba shi da wani say may his soul rest in peace, dangin Mom dina sun so daukana a lkcn stepmom ta saka dad dina yaki amincewa su tafi dani, to cut everything short, Ummi that was our neighbor then ita ta daukeni ta kawo ni cikin nata yaran bayan tayi threatening stepmom dita zata kai ta kara kotu cause barrister ce, Babansu zainab ma haka, kowa na shakkar shiga sabgarsu a layin, even my dad couldn’t confront her duk da gidan su Ummi was opposite to ours, few years later dad din nawa shi ma Allah ya masa rasuwa, Ummi and her husband are the reason i am who i am today, and after everything they gave me der daughters hand in marriage… though Zainab father is also late bayan aurenmu da shekara biyu…” A hankali Mayraah tace “Allah ya ji kansa, Allah ya ji kan iyayenka kai ma” Yace “Shi yasa naji tausayinki da kika ce min ur parent were late” Nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah, yace “Ya ku ka yi da aunt dinki about inda zaki zauna saboda aikin?” A hankali Mayraah tace “Dama tace kayi min recommending area da zan iya samun wajen zama a nan since mu bamu san Abuja ba kai kuma a nan kake” Dr Khalil na kallonta yace “Ohk akwai kudin kama wajen da zaki zauna din kenan?” Ta gyada masa kai, yace “Meye Budget din ku?” Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace “Ai ban san nawa bane ake renting waje a nan” Yace “Nasan baki sani ba, amma nawa ku ke da shi a kasa don in san irin wajen da za a samar maki gidan” Tace “Like 300k yayi?” Khalil ya gyara zama yana kallonta da kyau yace “Yanzu akwai 300k din a kasa?” Ta gyada masa kai, kallonta yake ko kiftawa babu, hakan yasa ta sunkuyar da kanta, Yace “Ilham” Ta daga kai ta kallesa yace “Kuna da 300k din kama gida me yasa baki yi registration din admission da kika ce an baki ba?” Ta hade rai tace “I told u sai da aka tara kudin na taho, kuma da na zo naga an riga ma an rufe portal na registration har ma sun kusa fara exams, kaga ai dole za a soke admission dina” Dr Khalil yace “Wani makaranta ne? And where is the admission list?” Mayraah taji wani zufa na keto mata amma ta wani daure fuska, dai dai nan aka kwankwasa kofar office din ta mike da sauri kamar jira take tace “Kilan patient ne….” Yayi izinin shigowa sai ga wata patient da yake da appointment da ita ta shigo office din, tuni Mayraah ta fice daga office din nasa, gaba daya ta kasa samun nutsuwa a asibitin har aka yi la’asar, Dr Khalil na shigowa daga masallaci Mayraah ta ki barin su hada ido a reception din sai duba file din wata mata take a shelf, ya wuce sama, komawa tayi ta zauna a hankali tana Allah Allah karfe shidda lokacin da yan evening za su amshi duty yayi ta kama hanyar suleja komin dare kuwa, 6 nayi dot Dr Khalil ya sauko ita ko har ta fito daga changing room rike da jakarta, tana ganinsa ta wani hade rai taki yarda su sake hada ido, duk yana kallonta, makullin office dinsa ya mika mata yace “Get me my laptop and bring it to the parking space Nurse Ilham” Ta amshi makullin ya fita daga reception din, ko da ta iso parking space bayan ta mika masa laptop din yace “Ina za ki yanzu?” A takaice tace “Gida” yace “It’s late ki ce zaki kama hanyar suleja yanzu, so kawai gidan Ummi…..” Katse sa tayi da sauri tace “Aa ni bazan je ba gaskkya” yace “Saboda me?” Tace “Gidansu matarka ce fa” Yace “It’s nothing, nace maki nima gidanmu ne, matata tasan wanene ni, ko dazu da muka yi waya da Ummi ta tambayeni ke, i told her anjima zaki je can cause nasan baki da inda zaki zauna nan Abuja yau din ma” it took more than 10 minutes kafin Dr Khalil yayi convincing Mayraah ya kai ta gidan surkarsa, duk jikinta a sanyaye ta shiga gidan kamar munafuka shi ko dama yana ajiyeta ya juya, Ummi na parlor da sister dinta Rabi’ah warce ita ma ranan ta zo, Mayraah ta zauna kasa ta gaida Ummi, Ummi ta amsa da fara’a tace “Ya aikin?” Mayraah tace “Alhamdulillah” Ummi tace “To maa sha Allah, yace min har yanzu baki samu wajen ba ko?” Mayraah ta gyada mata kai, Ummi tace “To in kin ga babu damuwa kiyi zamanki a nan mana sai ki dinga komawa gida weekend, ni dama da yace wai gida kike nema ki zauna hakan bai min ba kina ‘ya mace, dama hostel ne cikin makaranta da sauki wannan, amma gida kam bai kamace ki ba” Mayraah dai kanta na kasa, Ummi tace “Sai ki ma iyayen naki bayani in sun gamsu ba wani takura sai ki zauna nan abun ki kina zuwa aikin ki, abinda in kin fita tun safe sai karfe shidda, weekend kuma sai ki je masu gida tun da naga Auxiliary nurses basu fiye aiki weekends a asibitin ba” Mayraah ta daga kai tace “Toh Nagode sosai, Allah ya saka da Alkhairi” Ummi tace “Ameen sai ki shiga kitchen ki debi abinci” Mayraah tace “Toh, nagode” Mikewa tayi ta nufi dakin da aka sauketa, Rabi’ah da ta bi ta da kallo tace “Ummi wacece?” Ummi tace “Bakuwa ce” Daga haka ta mike tace “Bari in je lokacin sallah yayi” Mayraah ta kai minti sha biyar tana nazarin zaman gidan da Ummi tace tayi, anya zata iya kuwa, though taga matar is very kind amma ita sai abun yayi mata wani iri a kai, shi ko tsoro baya jin kar su zargi wani abu ko ayi tunanin budurwarsa ce ita, kauda zancen tayi kawai a ranta daga karshe ta mike ta shiga bandaki. Da daddare Mayraah na daki Ummi ta shigo dakin tace “Ilham zo ki duba magungunan nan da Khalil ya bada aka kawo dazu bai bada prescription ba” Mayraah tace “Toh” Mikewa tayi ta bi bayanta suka fita zuwa wani daki, Wata tsohuwa ce zaune dakin kana ganinta kasan bata da lafiya, Mayraah ta zauna tana kallonta tace “Ina wuni kaka” Tsohuwar bata amsa ba, Ummi tace “Hajiya ba lafiya Ilham, duba magungunan ki ga” Da kyar tsohuwar ta bude baki tace “Kar ki sake sa ni a bakin duniya kice bani da lafiya Zuwaira, na kuma samu lafiyata babu abinda yake damuna yanzu, aniyar kowa ta bi shi” Ummi na kallon Mayraah tace “Ilham in kin bude maganin sai ki bata” Daga haka ta fita daga dakin, Tsohuwar na kallon Mayraah cikin rawan murya tace “Ke kiji rainin wayo, ita da ‘ya yanta fa suka sa min guba yau sati uku kenan ina fama jiki yaki dadi, amma duk wanda ya zo sai tace masa Hajiya ba lafiyaa, sai terere take min” Tana kai wa nan ta fashe da kuka, Mayraah dai sai kallonta take ta ma kasa cewa komai, ta karasa buda mata maganin ta mike mata, hannu na rawa ta amsa ta dau cup din ruwa, Mayraah tace “Sannu, amma jikin da sauki ko?” Tsohuwar tace “Ke ba wani sauki, yanzu haka duk jikina ciwo yake er nan, banda yaron nan Halilu ɗan albarka ai da na mutu mushe a dakin nan, wai fa a haka an sa min gubar ban mutu ba sai ki ga ita wannan er figigiyar macen da suke ce ma Mimi tana lekoni tana raye raye da tafe tafe, su kuma yan biyun maza sai su zaga baya suyi ta buga kwallo kan windown dakin wai duk don kar in yi bacci, ke bari kawai abinda suke min a gidan nan wallahi kare bazai ci ba, Allah ya isa kawai, banda mutuwa me tonan asiri” Mayraah dai ta ma rasa me zata ce, Tsohuwar na matse kwallan idonta tace “Ga flask can ki tafi da shi ki dafo min wani ruwan zafin a kitchen ban yarda da wanda ke ciki ba tun dazu nake jiran shigowan Halilu ya dafo min wani ruwan shima shiru shiru gantalallen bai shigo ba yunwa nake ji kamar zan suma, ita ma munafukar me aikin gidan na daina yarda da ita duk bakinsu daya da yan gidan” Mayraah ta mike tace “Toh bari in dafo maki Kaka” Daga haka ta fita daga dakin, Tsohuwar tace “Gwara na kama bare kawai, in ma ta cuceni bazai min ciwo ba kamar na jikina” Mayraah na fitowa Ummi dake parlor da karime tace “Ikon Allah….” Karime ta kyalkyale da dariya tace “Ai kuma shikenan kun ƙulla da Inna tunda har ta yarda ki dafo mata ruwan shayi” Ummi tayi murmushi tace “To Allah shi kyauta, sai ki je ki dafo mata”
Hajja na kishingide bayan isha a parlor tana kallon Badiyyah dake kwance ko sallan la’asar bata yi ba balle Magariba ga isha har anyi, daga gefenta kuma plate din abinci ne da Hajjan ta ajiye mata har ta cinye ta bar mata plate din a wajen, Hajja tace “Ke yanzu fisabilillahi Badiyyah ina ta magana tun dazu kin ki tashi daga kan kujeran nan, ga salloli a kanki, kima je kiyi sallan mana sai ki dawo ki ci gaba da latse latsen wayar Badiyyah” Badiyyah tace “Kai na shiga uku, ke Hajja nace maki bazan yi sallan nan bane da kika dameni haka, ina fa sane, ki bari in gama abinda nake a wayar mana tukun” Hajja tace “Kina jin ai gorin da suka maki ranan babu dadin ji, amma ni ko a jikina tunda nasan ba su suke bada mijin auren ba, ita Ladi dama makwadaiciya duk inda galmi galmi yake nan take makalewa, cabdi ta zo nan tayi min me tasan ni ba me kudi ba, ai in ma ta zo wallahi koran kare zan ma er iskar makwadaiciya, tunda bata da zuciya tayi ta zama gidan Mamudan….” Ko rufe baki Hajja bata yi ba aka tura kofar parlon duk suka daga kai, wasu maza ne su hudu suka shigo parlon, Hajja ta mike zaune a firgice tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’una me zan gani haka, daga ina ni Sadiya??” Badiyyah da ta gigice ta mike tsaye ita ma gashi babu daman gudu duk sun zagaye Parlon, Daya daga cikinsu ya sanar da cewa su yan sanda ne ya ciro ID card dinsa yana nuna masu sannan yace “Wata waya muka yi tracking muka gano tana cikin gidan nan” Badiyyah jiki na rawa tana nuna masa wayarta tace “Wallahi waya ta ce wannan ku duba ku ga” Wani ɗan sanda ya daka mata tsawa yace “Kar ki rena mana hankali ke, bayan wayar taki wani wayar ce a gidan nan kuma?” Badiyyah tana zare ido tace “Waya kuma? Sai ɗan karamin wayar kakata fa wllhi” Hajja dai salati kawai take ta kasa zaune ta kasa tsaye ko ina na jikinta na bari, Wani firgitattcen tsawa da police man din yayi ma Badiyyah sai da ta kusa sakin fitsari yace “Idan kika bari muka shiga muka dauko wayar da kan mu to baza ki ji da dadi ba” Nan suka sanar mata sunan wayar har da color din wayar Badiyyah ta hadiye wani abu da kyar ganin babu wasa fuskarsu ga wani har yana kokarin kai mata mari tace “Yana daki bari in dauko maku” Bin ta suka yi har zuwa cikin dakin ta dauko wayar wanda farashinta zai yi miliyan daya da rabi suka amsa a hannunta suka kado ta parlor, Hajja salati take har a sannan tana zaga Parlon babu wanda ya bi ta kanta aka saka Badiyyah dake rusa kuka a gaba suka bar gidan. Abba na zaune parlor tare da Mama Ladi dake cewa “Ni kaina Mamuda wallahi na gaji da koke koken nan da Ammi take ba dare ba rana kan yarinyar nan Mera, ka tambayi su Mashir babu abinda bana gaya mata don dai ta kwantar da hankalinta amma duk a banza, zuwa yanzu ya ci ace ko mutuwa Mera tayi Ammi ta sa ma ranta dangana kuma haka balle er banzan na can in an bibibiya hankalinta kwance tana sabgogin gabanta mu kuma ta bar zuciyoyinmu cikin walagigi, ni da ba don ma kar ku kullaceni ba da sai ince dama ance tsintattciyar mage bata mage, Mera ta nuna cewar lallai da gaske mu ba danginta bane shi yasa ta shiga duniya kanta tsaye ko duba irin kyakkyawan rikon da aka mata na shekara 23 bata yi ba duk ta mance wannan halaccin, to ni ko Allah ya isa na mata sai ya bi ta duk inda take wllhi, kuma haƙƙin Ammi bazai bar ta ba a dubi mugun damuwar da ta jefata ciki fisabilillah, to shine nake son baka shawara Mamuda anya baza ka dau Ammin nan ko Saudia ne ku je ku kwana biyu ba ko Allah zai sa ta samu salama a zuciyarta, ni wallahi tsoro nake kada ciwon zuciya ya kamata tunda dama tana da hawan jininta duk mun sani, kaga ban ma san zaka kawo min maganar ba ina ta son in samu lokaci in zaunar da kai ince maka gaskiya a duba lamarin Ammi ashe kai ma hakan na damunka bawan Allah” Abba ya sauke ajiyar zuciya yace “Shikenan Mama, shawaran da kika kawo ma yayi gaskiya, in sha Allah zuwa nan da sati daya sai mu tafi Saudi Arabia kawai” Mama Ladi tace “Yauwaaa Allah maka albarka Mamuda, daga nan sai ku saka er banzan yarinyar a addu’a Allah ya karkato da hankalinta gida, ai gantalin ya isa haka kuma, ni dai kafin ku tafi dama kar ka manta kajin firiji sun kare, er mantinar ma duk Ammi nake juye ma a kofi in zuba mata madaran gwangwani duk sun kare su ma, kasan kuma babu dadi a tafi a bar gida babu isasshen kayan abinci” Bude kofar Parlon aka yi duk suka juya, Hajja ta shigo tana rusa kuka tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Mama Ladi ta mike tace “Mun shiga uku mutuwa Badiyyar tayi??” Cikin kuka Hajja tace “Yan sanda ne suka zo suka tafi da ita muna zaune parlor ba laifi ba komai, yaushe rabon ma da ta fita ko nan da gate Marainiyar” Abba da ya mike shi ma yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un”

Mama Ladi dake zaune Parlon Ammi ta maida cup din shayin gabanta gefe da sauran bread din da ya rage tana kallon Hajja da ta kasa daina kuka kamar ranta zai fita, ta marairaice tace “Yaya ki sa ma ranki salama don girman Allah, wallahi kukan nan naki ya sa na kasa nutsuwa in ci abinci in koshi duk hankalina ya rabu, tunda Mamuda ya ce zai yi duk iya bakin kokarinsa don ganin an sakota ai kema kinsan zai yi hakan, kwanaki da suka tafi dake ba waya kawai yayi aka sako ki ba ko kin manta ne….” A fusace Hajja tace “Ladi ki shiga hankalinki ki fita harkata kar ki sake cewa za ki min wata magana, ai da er ki ko jikarki aka shigo har gida aka dauke baza ki samu damar hada katon kopin shayi da bredi ki sa a gaba kina ci ba, rayuwa ce fa Ladi, kuma kowa yayi da kyau zai ga da kyau” Mama Ladi ta saki baki tana kallon Hajja da mamaki, can tace “Ka ji yaya da wata magana dai, sai in ki cin abinci ina jin yunwa saboda yan sanda sun tafi da Badiyyah?? ayi magana fa ta gaskiya domin Allah? Shi ciki ina ruwansa da abinda ke faruwa shi dai ba kawai a fita hakkinsa a sallamesa ba, ita kanta Badiyyar yan sandan baza su bar ta haka ba sai sun bata abinci a celf balle ni da nake gida, kaji fa yaya da wata magana jama’a, shi ciki meye nasa a wannan lamari da za a tauyesa?” Ammi dai dake Parlon zaune sai kallonsu kawai take bata ce komai ba, a fusace Hajja tace “Ga ki ga abinci Ladi… Kiyi ta ci ba komai rayuwa ce” Mama Ladi ta mike ta dauke shayinta da sauran bredi ta nufi dakin Ammi tana cewa “Ji min dai fadan rashin gaskiya kiri kiri wai kar in ba cikina haƙkinsa don an tafi da Badiyyah, a ina aka taɓa haka, ba sai mutum ya ci ya koshi zai samu karfin jajanta lamarin ba, ni dai ba ruwana” Daki ta shige don har Hajja ta bata mata rai, murya can kasa tace “Ina ruwana da wata Badiyyah ma dai tukun, ban da dai neman magana irin na Hajja, Mera ma da bamu san inda take ba bai sa mun hana cikinmu abinci ba balle wata Badiyyah da muka san inda aka kai ta” Ammi na kallon Hajja cikin sanyin murya tace “Kiyi hakuri Hajja, tun da yace zai yi duk yanda zai yi in sha Allah a daren nan za a gama komai ta dawo gida, ki kwantar da hankalinki don Allah” Hajja na kuka tace “Toh Allah ya sa Ammi, Allah ya dubi maraicin yarinyar” Abba na zaune parlonsa Maheer ya shigo ta dalilin kiransa da Abban yayi, ya zauna kan kujera Abba na kallonsa yace “Wayar wani babban mutum fa yarinyar nan taje ta dauka babu batun bail yanzu haka, anya kuwa yarinyar nan kanta daya bata da wani mental problem?” Maheer yayi shiru yana kallon Abba yana jinjina abinda Badiyyah tayi a ransa, Abba ya sauke ajiyar zuciya yace “Gaskiya an ɓata rayuwar yarinyar nan kawai, abun nata sai gaba yake, ya kai har da dauke dauke yanzu take, ko kwana goma ba ayi ba taje gidan matarka tayi mata sata wanda ya kai su ga fada har ta fasa mata kai, yanzu kuma wayar mutane taje ta dauko me tsada aka yi tracking, wannan wace irin rayuwa ce?” a ran Maheer tunani ya shiga yi don ma Abba bai san duk adadin gurmin da ta hada a yan watannin nan ba, iya wanda kawai ake gaya masa ya sani, wanda da zai san har da sa hannunta wajen barin Mayraah gida da ma fasa auren Mayraah da ko bin ta kan case din nan bazai yi ba, dama shi tun da yaji an zo an tafi da ita ko bin ta kan issue din bai yi ba don abinda ya damesa ma ya ishesa, duk inda ma za a kai ta a kaita for all he cares ba kuma abinda zai tofa a lamarin, Abba ya kara sauke ajiyar zuciya yace “Sai dai zuwa gobe da safe kuma mu ga abinda hali zai yi, amma wannan ba karamin case bane gaskiya, don sun ce sai me wayan ya zo yana Abuja, to wa yasan sanda zai zo” Maheer yace “Allah ya kyauta” Abba yace “Ameen” Wayarsa dake ring ya dauka ya ga Hajiya Amina ke kiransa, Maheer ya mike ya fita daga Parlon, this past days kawai karfin hali yake yi, rashin Mayraah ba karamin taɓa sa yake ba, it’s weighing him down sosai ba kadan ba, dare daddaya ne baya mafarkinta idan ya kwanta, downstairs ya dawo ya zauna ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido missing his lil sis, he misses her so badly, ya fi minti sha biyar zaune parlon ya ji muryar Mama Ladi ya bude ido yana kallonta, Mama Ladi tayi kasa da murya tace “Ya ake ciki, inji dai Mamuda bai samesu a wayar ba su yan sandan” Maheer ya gyara zama a hankali yace “Wayar wani babban mutum ta dauke, ba ma batun bail yanzu maganar da ake” Mama Ladi ta gwalo ido tace “Wayar babban mutum? Eh lallai Badiyyah ta shahara sauran kawai ta fara yawo da makamai, nan ko kakar tun dazu ta ishi kunnemu da kuka wai da kyar ba sharri aka laka ma Marainiyar ba ni ko a raina ina ta tunanin anya Hajja ba bakinsu daya da Badiyyah ba kuwa? Da kyar fa in ba ita take kai ma kayan satan ta ajiye mata ba, sannan don girman Allah kai dai ka ja bakinka kayi shiru kar ka wani ce ma kowa ance babu beli wllh hanamu bacci tsohuwar nan zata yi daren yau don gaskiya yanzu haka ma bacci nake ji kada a shiga hakkina akan abinda bai shafeni ba, yanzu haka ina komawa sama shimfida zan yi in kwanta ince mata Mamudan bai dawo daga caji opis din ba” Daga haka tayi wucewarta kitchen zata kai cup din shayi…. Still wajen karfe sha daya Maheer na parlor Ammi ta sauko downstairs zata shiga kitchen ta hado ma Abba shayi, Ammi na kallonsa a hankali tace “Ita waccen dake asibitin an sallameta ne da na ganka a nan” Maheer ya girgiza kai yace “Sai gobe za a sallameta yan uwanta na asibitin, amma Ammi na so kawai taje gidansu daga asibitin don ina bukatar space, but Abba ya hana hakan ni kuma gaskiya i can’t stand the sight of her a yanzu” Ammi dai tayi shiru bata ce komai ba, can ta wuce kitchen kawai. Kamar kullum yau ma karfe bakwai na safe Mayraah ta fito daga daki bayan tayi shirin tafiya aiki, kitchen ta tafi ta dafo ma inna ruwan zafi don for 5 days now ita ke kai mata ruwan zafi da breakfast kafin ta fita aiki, Mayraah na shiga dakin ta ajiye mata ta gaisheta, Inna da bakinta ya bude ras tace “Lafiya lau, kin ga yau fes na tashi bana jin ciwo a ko ina alamar guban ya sakeni” Mayraah tayi murmushi tace “Haka ake so dama inna Allah ya kara maki lafiya” Inna tace “Ameen, ai da so suka yi ace na mutu su hade har gadona, ni da nasan komai” Mayraah dai murmushi kawai take tana hada mata shayin, Inna tace “Allah maki albarka ke dai, naji wai aiki kema kike a asibitin su Halilu ko?” Mayraah tace “Eh” Inna tace “Toh Allah ya baki sa’a, kuma Kinga yaran gidan nan ki bar sake masu fuska kar su raina ki yanda suka raina ni basu da mutunci kwata kwata ya yan jaraba ne ga uwar bata kwabarsu” Mayraah dai sai murmushi take tace “Bari inje kar inyi latti Inna” Inna tace “Toh maza ki tafi Allah ya tsare” Mikewa tayi ta fita, bata tsaya tayi wani breakfast din kirki ba don ka’idar asibitin karfe takwas ne, sallama tayi ma Ummi ta fita gidan, kwana biyar yau basu hadu da Dr Khalil ba sun je wani workshop Lagos, Ta fito daga wani ward downstairs wajen karfe sha daya Dr Balogun ya shigo Reception, tare da shi aka tafi workshop din, nurses dake reception suka hau gaishesa suna masa sannu da zuwa yace “The MD is around, so u have to compose ur selves….” Daga haka ya wuce sama, Smartly dressed in black suit with white shirt ya shigo Reception din hannunsa rike da laptop dinsa, Mayraah ta bi sa da ido, gaba daya nurses din suka dinga gaishesa da ladabi kamar sun ga wani prominent person, yayi wucewarsa sama bayan ya amsa a takaice without looking at any of them, Dr Khalil dai na biye da shi a baya holding on to his laptop too ya daga ma nurses din hannu, Hafsat ta kalli Mayraah dake kokarin ajiye file din hannunta ta dawo ta zauna tayi kasa da murya tace “Wai shi ne me asibitin?” Hafsat ta buda ido sosai tace “He is the managing director” Mayraah bata sake cewa komai ba, bayan few seconds ta sake kallon Hafsat tace “But he is a foreigner?” Hafsat tace “Wallahi ban dai sani ba, amma ya cika jaraba mutumin, and he is a no nonsense, kowa shakkarsa yake” Da sauri Mayraah ta mike bayan ta tuna akwai wata patient da Dr Hamid yayi assigning dinta ta sa ma ido, ward din ta nufa to check on the patient, bayan azahar Mayraah ta tafi office din Dr Khalil zata kai masa wani file, gaishesa tayi ya amsa yace “Ya kwana biyu, ya aiki?” Tace “Alhamdulillah, how was the trip?” Yace “So stressful, nan da wata daya za mu koma in sha Allah” Mayraah tace “To Allah ya kai mu” Yace “Ameen, just that you have to be very careful cause or Director will be around har zuwa next workshop kafin ya koma, don haka ki zama diligence kan aikinki kar ki bari encounter mara dadi ya hada ku it wont be funny, though bana wani jin ki tunda har Balogun yayi commending dinki” Mayraah ta zauna bata dai ce komai ba, yace “Ya su Ummi?” Tace “Suna lafiya lau” Yace “Ummi ta ban labari kun kulla kawance da Inna yanzu” Dariya Mayraah tayi, yace “To ki dai dinga bin a hankali kar ya kwabe maku” Murmushi kawai Mayraah tayi tana gyada masa kai, yace “Kin je weekend gida kuwa?” Tace “Na je” wayar kan desk dinsa ne ya fara ring, ya kalleta yace “MD na kirana, make sure kar ki tafi gida ki jirani i will drop you don nima zan je gidan” Tace “Toh” Mikewa yayi ita ma ta tashi suka fita office din tare, shi ya tafi last flour zuwa office din MD din, ita kuma ta sauka downstairs ta dau allurai a tray zuwa wani ward zata yi ma wata yarinya da aka yi admitting da safe, tana shiga ward din ta tarar Maman yarinyar na bata abincin da aka kawo masu na asibitin, sai da ta zauna ta jira ta gama bata abinci sannan ta mike ta fara hada alluran, bude kofar ward din aka yi Mayraah ta juya, sai kuma ta koma gefe tana kallonsu, MD din ne da Dr Khalil dake biye da shi a baya, Matar ta gaishesu MD din na kallonta yace “Hello Ma, is there any improvement?” Da turanci Matar tace har yanzu jikin yarinyar na zafi, sai zazzabin ya sauka sai ya sake dawowa, sannan yarinyar na zabura, MD ya kalli Mayraah dake tsaye gefe yace “Diagnostic procedure?” Haka kawai taji gabanta ya fadi ta dau file din yarinyar da ta shigo da shi ta fara budewa da sauri, lkci daya duk sai ta daburce, Dr Khalil ya amsa file din a hannunta yana dubawa ya sanar masa diagnosis din, Gyara tsayuwa yayi yace “Ita bazata iya dubawa ba sai kai” Dr Khalil yace “We have 19 more wards ahead Doctor” MD din yace “Therapeutic procedure?” Nan ma Dr khalil ya karanto masa within few seconds, MD din yace “Any medical History?” khalil ya sanar masa yana duban file din still, karasawa MD din yayi feeling the girls temperature ya duba ta da stethoscope din wuyansa, bayan few seconds ya kalli Mayraah a takaice yace “Give her the injections” Daukan alluran tayi ta nufi kusa da yarinyar zata yi mata amma sai abun yayi mata kamar bata taɓa yi ma kowa allura ba kamar ranan zata fara ga kuma kukan da yarinyar take ya gigitata, MD din ya kalli Dr Khalil a bit pissed off yace “Why is she so sluggish? Wannan ta san aikinta kuwa?” Dr Khalil zai amshi alluran ya dakatar da shi furiously yace “What for?” Mayraah ta masa wani kallon gefen ido bayan ta ɗan daure fuska, nan dai ta tsaida hankalinta waje daya tayi ma yarinyar alluran, ficewa yayi daga ward din Dr Khalil ya bi bayansa. Karfe biyar wata senior nurse ta sanar ma nurses dake reception da za su yi ma yan evening handing over cewar su jira akwai meeting, yan evening na zuwa to su yan morning za su shiga meeting din da director a meeting room dake cikin asibitin, the next day kuma kafin yan evening su tafi za su yi nasu meeting din. Mayraah ta fito daga wani ward Dr Khalil ya nufota yana kallonta yace “Kiyi tafiyarki gida kawai ba sai kin yi attending meeting din ba Ilham, beside he doesn’t even have ur data for now sai na basa, after the meeting i will be coming back home too” Mayraah taji hankalinta ya kwanta don dama tun da Matron ta sanar masu da batun meeting ta rasa sukuni, ita in son samu ne ma bata son ko wani irin encounter ya hadata da wnn MD din har sanda zai koma, kawai taji kwata kwata bai mata ba she don’t like him, he is rude and arrogant sannan ta ga alamar ya iya disgi, Ta langwabar da kai tana kallon Dr Khalil tace “Toh shikenan, sai ka dawo” Yace “Hope kina da cash dai?” Tace “Ehh ina da, thank you” Ko minti goma bata kara a asibitin ba ta dau jakarta ta tafi bayan taje tayi ma Nurse Hafsat sallama a injection room, tana fita nurses din reception suka fara kus kus a tsakaninsu ganin ta tafi bayan ance akwai all staff meeting, dama tun da aka lura da yanda wasu daga likitocin asibitin ke yaba mata shkkn aka fara mata hassada kiri kiri don wasu ko magana basa mata a asibitin ita kuwa ko sanin suna yi ma bata yi ba tunda ba wani surutu take ba ko hira, tsakaninta da su gaisuwa shi ma wasun su sai suyi kamar basu ji ba, asibitin da ko kwana goma bata yi cikakke da fara zuwa ba, hatta yanda Dr Khalil ke kiranta office da kuma yanda Dr Balogun ke interacting da ita ya tsaya ma da yawansu a wuya, wata nurse fa’iza tana kallon colleague dinta murya can kasa tace “Wato ita shafaffiya da mai bazata tsaya meeting din ba kin ga ta dau jakarta ta tafi, tabdi bata san MD bane, ta zata irinsu Dr Khalil da Dr Balogun ne ko Dr Hamid dake shining mata hakora, muna nan dake wallahi sai MD ya gane bata shiga meeting din ba, sai in dai basu hadu a asibitin ba wannan mayen, zan ga ko shi ma kwarkwasan zata dinga masa yanda take ma sauran likitocin, Allah Ubangiji ya sa ya disgata gaban kowa da kowa mu ga iskanci, ko su Dr Khalil din da Dr Balogun babu abinda za su iya yi in ba haka ba ya hada da su” Nurse Victoria tace “The thing tire me my sister, ke daga zuwanki sai wani feeling kanki kike kin zo kin samu mutane a waje ki dinga wani ciccin magani kina daga masu kai wai ke me kokari, who does that?” Nurse Bola dake jin su tace “Fatana kawai yana ganinta after all the meetings ya gane bata shiga ba, a nan zata ga ikon Allah” Suna hango Nurse Hafsat duk suka yi shiru. Mayraah na isa gida ta tadda Ummi zaune parlor tare da Zainab matar Khalil da kanwar Ummi warce ake ce ma Aunty Rabi’ah, tun zuwan ta gidan sai ranan taga Zainab ta zo, ta karaso ta zauna ta gaida Ummi da Aunty Rabi’ah sannan ta gaida Zainab din ma, kallo daya Zainab tayi mata ta kauda kai ta amsa, Mayraah ta mike ta shiga dakin da take, Sai da Ummi ta ji ta kulle kofa sannan ta kalli Zainab tace “Wannan wani irin amsawar walakanci ne Zainab?” Zainab tace “Walakanci kuma Ummi, ta gaisheni kuma ai na amsa” Aunty Rabi’ah tace “Wai Ummi har yanzu bata samu gidan bane, last week da na zo ce min kika yi gida take nema fa, wannan ko sabon gidan da aka gama ginawa take so ya ci ace ta samu yanzu dai” Ummi tace “Bata samu ba, kuma baza a samun ba ma” Aunty Rabi’ah ta kyabe baki tace “To Allah ya kyauta” Har bayan magrib Mayraah bata fito daga daki ba, cause impression din Zainab duk sai yayi weaken dinta gaba daya, Mimi ce ta shigo dakin tana kallon Mayraah tace “Aunty Ummi tace in kira ki” Mayraah tace “Toh” Mikewa tayi daga kan darduma ta fita zuwa parlor, Ummi kadai ce zaune parlon, Mayraah tace “Ga ni Ummi” Ummi tace “Naga baki debi abinci ba” Mayraah tace “Ina jiran ayi isha ne” Ummi tace “To ai lokacin ma ya gabato, Inna na tambayarki nace kin dawo kina hutawa ne a daki” Mayraah tayi murmushi dai dai nan aka yi sallama kofar parlon, Ummi ta daga kai tana kallonsa da mamaki tace “Aa… kai kuma daga ina haka? 5 weeks din kenan?” Juyawa Mayraah tayi gabanta ya fadi lokaci daya ta dauke kanta da sauri.
Karasowa cikin parlon yayi yace “Ina wuni Ummi” Ummi tace “Lafiya lau, ko dai dama baka tafi ba?” Ya ɗan yi murmushi yace “Ban tafi ba kuma? Bayan har vid call mun yi 2 days back Ummi” Ummi tace “To na gan ka ne kamar an jefo ka ai” Sai a sannan ya ga Mayraah da kanta ke sunkuye kamar munafuka, lkci daya murmushin dake fuskarsa yayi fading, kallon Ummi yayi ya sake kallon Mayraah, kamar tasan kallon nata yake ta daga kai da sauri tace “Ina yini” Still looking at her yace “Lafiya lau” Ummi na kallonsa tace “Bakuwa ce” Yace “Oh ohk” Barin parlon yayi zuwa dakin sa, yana shiga ya ciro waya yayi dialing number Ahmad. Gaba daya Mayraah ta kasa cin abincin da ta debo a kitchen, duk ta rasa wani tunani zata yi, shi ma wannan mutumin gidansu ne nan kenan? She still vividly remember his face, Maida abincin gefe tayi ta jinginar da kanta da gado tsabar yanda ta zama confuse. Ana idar da isha mai aikin gidan ta zo tace mata Inna na kiran ta, ta mike ta saka hijab dinta ta fita, babu kowa parlor ta shiga dakin Inna da sallama murya can kasa, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab, Dr Khalil da shi mutumin da ko sunansa bata sani ba su ma suna dakin inna, ta karasa ta zauna kasa tana kallon Inna tace “Inna ina yini?” Inna tace “Lafiya lau, naji shiru shiru baki shigo kin zubo min sabon ruwa a flask ba shine nace ko kema kin fara canza hali ne, ko kuma yan gidan sun fara canza maki ra’ayi” mikewa mutumin yayi ya fita daga dakin, Mayraah tayi murmushin karfin hali tana kallon Inna tace “Bari in kawo maki” Zainab dai sai danna wayarta take, Mayraah ta dau flask din ta fita daga dakin, Dr Khalil ya mike ya fita Zainab ta bi sa da kallon gefen ido. Mayraah na kitchen bayan ta kunna gas zata daura ruwan flask din aka bude kofa, ta juya da sauri ya shigo yana kallonta yace “U told me admission kika samu a Abuja? Aikin me kuma kike yi a asibiti yanzu?” Kallo daya tayi masa ta dauke kai ta ci gaba da abinda take tace “Admission din bai yiwu ba” yace “Why did u change ur name from the Mayraah u said at the hospital to Ilham?” Ta kallesa tace “Kaga kai ma ba dai dai ka fada sunan ba yanzu haka, so sbda irin wannan issues din yasa ake kirana Ilham most of the time” Yace “Really?” Tace “Yeah” Yace “Ohk, welcome to our home Ilham” yana fadin haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo, wani boyayyen ajiyar zuciya ta sauke ta ci gaba da abinda take, ko da ta je kai ma Inna ruwan zafin ta tarar har Zainab da Dr Khalil sun tafi gida, ita ta ga kamar ma shakkar matar tasa yake wai ko magana bai mata ba saboda Zainab din na wajen, Inna na kallonta bayan ta ajiye flask din tace “Kin ga jikana Ahmad ya dawo daga kasar turawa ko, to shi ne babba a gidan kuma sa’annin juna ne da Halilu, shima kuma Halilun ɗan gida ne duk da ba jininmu bane shi amma ya zama ɗan gida, sai wannan mata da ta bari tayi kiba dazu da kika shigo tana zaune can tana latse latsan waya sunanta Zainab yanzu haka tana da yan biyu mata, saboda yabawa da kyawawan dabi’un Halilu, marigayi ubanta ya ba Halilun auren Zainab, kinsan ni na haifi uban nata, Allah dai ya ji kansa, Bayan Zainab sai yan biyu maza Hassan da Hussaini kullum sai su zagaya bayan windan nan su isheni da buga kwallo wai kar in huta, sai figgiyar yarinyar nan Fatima bata da aiki sai raye raye, duk Zuwaira ce ta haifesu, in ma kika ce ba ita ta haifi Halilu ba to ranta baci yake” Mayraah dai sai kirkiran murmushi take don ta kagu ta bar dakin, daga karshe ta samu ta sulale tace mata zata je tayi wanka.
Musharraf na kwance dakinsa da safe Mami ta shigo, yayi mata kallo daya ya kauda kai, mancewa ma yayi bai kulle kofar ba bayan ya dawo masallaci, ta karaso cikin dakin ta zauna gefen gado tana kallonsa tace “Musharraf” Ya kalleta bai dai ce komai ba, ta kai hannu forehead dinsa tayi kasa da murya tace “Yanzu baza ka cire ma kanka damuwar nan ba Musharraf kayi facing reality” Ya ki kallonta balle yace komai, ta sauke ajiyar zuciya tace “Ta shi mu je kayi breakfast” Mikewa zaune yayi ya matsa daga kusa da ita yace “Mami duk ke kika ja wannan abun, u caused everything, da kin bari mun yi aure tun wancan lokacin she wouldn’t have gone missing now, yanzu wa yasan halin da take ciki a inda take” Mami tace “Musharraf ita ‘ya mace komin rintsi ban ga dalilin da zata bar gidansu ba ko ince gidan da ta taso, bata da wani hujjan da zata ce ta bar gida, ni fa tunda yarinyar nan ta iya tsallaka kafa tayi tafiyarta har aka zo ana zargin ka akayi arresting dinka naji ta fita a raina bazan boye maka ba, who knows the life she’s living now tunda ta gwammaci ta shiga duniya tayi rayuwarta…” Musharraf da yaji haushin furucin Mami har ransa yace “Mami kika san wani pressure yasa ta tafi? She is so young for all this that is happening to her, she can’t think straight, so ake yarinyar ta kamu da depression, she is just 22 fa Mami” Mami tace “Ni dai in za ma ka cire ta a rai ka ci gaba da harkokin gaban ka is better u do so, don babu aure tsakanin ka da wannan yarinyar just put that in mind, in kuma har ka mance abinda guardian dinta suka mana a police station sai in ji, it’s simple idan har zaman kasar ma baka so to ka tafi Canada ka samu Daddy….” Musharraf ya katse ta yace “Waye Daddy? Mami pls ki daina hadani da gayen nan, i have no business with him” Mami tace “Shi ɗan uwan naka zan daina hadaka da?” Musharraf ya sauka daga kan gadon yace “Ɗan uwana that is happy with what i am going through, he is happy with my downfall, ko sau daya bai taɓa kirana duk wannan abubuwan dake faruwa ba” Mami tace “To saboda me zai kiraka, kai kiransa kake Musharraf?” Bai sake sauraronta ba ya fice daga dakin. Maheer na zaune parlon Ammi yayi kasa da murya yace “Ammi yau za a sallami Haseenah daga asibiti, so Abba insisted in kawota gidan nan har ta karasa samun sauki” Hajja da ke zaune parlon hannunta rike da carbi ta dago da sauri tana kallonsa jin abinda yace, Aunty Mariya ma da ta zo jiya da mai gidanta da ya zo yi ma Hajja jaje ta kalli Maheer da mamaki, Hajja tace “Wani gidan? Wai ci gaba da zama da matsiyaciyar nan zaka yi kake nufi Maheer? Ko dai baka da kai ne? Ita Hasinar kake mararin dawowa da ita har zaka kawota gidan nan?” Ammi dai bata ce komai ba, Hajja ta kalleta ta hade rai tace “Ya kika yi shiru Ammi? Kema kin goyi bayan ta dawo ya zauna da er matsiyatan kenan tunda har kika yi shiru” Ammi ta kalli Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace “Hajja ba daga ni bane, nima na so nuna ma Alhajin hakan amma yace lallai Maheer bazai rabu da ita ba saboda ɗan matsalar nan da aka samu, shi yasa kawai na hakura na ja bakina nayi shiru” Hajja na gyada kai tace “Eh lallai, dole kice ɗan matsala tunda ba ke aka kai Caji opis ba aka ci ma mutunci aka walakanta ba ko shi Mamudan, ae ni aka taɓa dama ba ku ba, karshen biyayyar da kike ma Mamuda naga sakayya ya maki da kishiya ai, ke uwar yan bin miji, wato baza ki iya nuna masa ke baki yarda ba an ci mutuncin uwarki shine kika yi shiru kika kyale hukuncin da ya yanke, to ba komai ai rayuwa ce” ita dai Ammi kanta na kasa, mikewa Hajja tayi tana kallon Aunty Mariya tace “Ni ai sai in bar gidan, dama banda lalura da damuwar da yayi min yawa ban san halin da yarinyar mutane ke ciki ba ga dangin ubanta sai zarya suke mana me zai zaunar da ni a gidan surki har zuwa yau, ai an san ba halina bane wannan, ki tashi mu je Mariya dama zuwanki kawai nake jira kuma jiyan baku iso da wuri ba” a hankali Ammi tace “Aa kiyi hakuri Hajja yanxu haka fa Alhajin suna hanya da Badiyyar mun yi waya da shi yace an gama komai in Allah ya yarda yau zata dawo gida an rufe case din” Ko rufe baki Ammi bata yi ba Badiyyah ta shigo parlon, Hajja ta saki salati ta fashe da kuka ta tafi da gudu ta rungumeta tana kiran sunanta, Ammi dai sai kallon Badiyyah take ganin yanda ta rame tayi bakikirin kamar ba ita ba, ita kanta Aunty Mariya sake baki tayi tana kallon Badiyyah, Hajja na kallonta daga sama har kasa cikin kuka tace “Sannu Badiyyah, sannu, Allah Ubangiji ya saka maki wannan abu da aka maki, Allah ya saka maki” Aunty Mariya tace “Allah ya saka mata fa kika ce Hajja? Yarinyar da ta dauke wayar mutane me tsada ne zaki dinga yi ma wannan addu’ar? Maganar da sai da na kai zuciyata nesa na iya sanar ma mai gidana saboda kunya, kuma ke nan har kullatata kika yi ban zo ba, sata fa Hajja? Gaskiya wannan ba karamin abun kunya Badiyyah ta ja mana ba ta ja ma kanta, me ta rasa da zata jefa kanta cikin wannan mummunan hali na satan kayan mutane?” A mugun fusace Hajja ta juyo zata yi magana sai ga Abba ya shigo da sallama, Hajja ta koma ta zauna tayi kasa da kai don dama da hijab dinta a jiki, Abba ya zauna ya gaida Hajja, Hajja ta amsa tana masa sannu da kokari, Aunty Mariya ta gaida Abba ya amsa, sannan yana kallon Badiyyah on a serious note yace “Ke bude kunnuwanki ki saurareni” Badiyya dake rakube jikin Hajja ta daga kai tana kallonsa yace “Kin ga sati dayan nan da kika yi hannun hukuma? To ya kamata ya zame maki darasi a rayuwarki, in har baki yi hankali ba a sati dayan nan to ko baza ki taɓa yi ba, da girmanki da hankalinki ban ga dalilin da zaki dau wayar mutane da sunan sata ba, me kika rasa da har kika ji sha’awar yin sata Badiyyah?” Hajja tayi kasa da murya tace “Mamuda kilan dai akasi aka samu, amma ni nasan halin Badiyyah wallahi sata ba halinta bane bata taɓa daukar min ko kwandala ba tun da ta taso” Tana fadin haka Badiyyah ta fashe da matsanancin kuka tace “Abba kawata ce fa ta bani ajiyar wayar ban san sato shi tayi ba” Abba ya daka mata tsawa yace “Wato bakin ki bazai mutu ba, da aka ce ki fadi inda kawar take kin fada a gaban yan sandan? Maganar banza maganar hofi, ke kika saci wayar ba kawarki ba” Aunty Mariya tace “Ai mara kunya ce, sam bata da kunya, don in har tana da kunya ma bazata bude baki tayi magana ba a nan, kuma dama duk inda makaryaci munafuki yake za a samesa da daukar abinda ba nasa ba, to kanki kika ja ma abun kunya wallahi ba mu ba, sannan ga record dinki na sata can wajen yan sanda” Hajja dai ta kalli Aunty Mariya ta gefen ido bata ce komai ba, Abba ya mike kawai ya fita daga parlon don shi case din ma kunya kawai ya basa kawai babu yanda ya iya ne yayi involving manyan mutane masu ganin girmansa, ace wai er kanwar matarsa ce tayi satar waya, satar ma a hotel kawai dai bai son bude zancen ne gaba daya sai dai yayi da Ammi but he is highly disappointed don a hotel Badiyyah tayi satar wayar, ga Maheer da Usman suka ki shiga case din suka bar sa shi kadai yana ta fama for one week, Aunty Mariya na ganin fitar Abba kafin Hajja ta samu damar ce mata komai ita ma ta mike ta fice daga parlon zuciyarta na tafarfasa, Hajja na kallon Badiyyah ta mike ta dagota tace “Tashi mu je gida kiyi wanka in samar maki abinda za ki ci, ba komai rayuwa ce, wanda bai zo ba ma jiransa yake” Ammi dai sai kallonsu take cike da takaici wai er late sister dinta ce haka, yanzu da Rukayyah na da rai Badiyyah ai bazata zama haka ba, Allah ya gani tayi bakin kokarin ganin ta ba Badiyyah tarbiyar da ta ba nata ‘ya yan, tarbiyar da ta ba Mayraah ta so yi ma Badiyyah amma Hajja tayi ta intruding saboda son duniya da ta dauka ta dora ma Badiyyah don maraici, haka yasa Badiyyah ta daina tsoron kowa ta daina ganin kowa da gashi tunda tasan Hajja zata tsaya mata, ko kallon banza su Maheer suka ma Badiyyah sai Hajja ta ɓata rai, wani lokacin har Ammi hakan ke shafa don sai ta fita harkanta na sati da satittika duk don kan Badiyyah, wannan dalili yasa Badiyyah na cewa tana son Musharraf Ammi tace a hakura a bar mata tunda ita tasan wacece Hajjar, amma at the end duk da hakan bata fita ba, ta dalilin Badiyyah yau gashi babu Mayraah, tunanin hakan yasa hawaye ya kawo idon Ammi, shi dai Maheer ido kawai yake bin su da shi, Hajja na kallon Badiyyah tace “Baki da lafiya ne, naga kina layi? Ko dukanki suka yi a can?” Badiyyah ta marairaice tace “Jiri nake gani, kuma….” Da sauri ta rufe baki tana tsaye inda take kamar wata er yarinya ta fara kwararo amai Hajja ta gigice tana rike da ita tana salati, Ammi ta taso ta nufo su, Maheer dai sai kallonta yake babu ko kiftawa. Mayraah na zaune ita da Hafsat wajen karfe tara da rabi sauran nurses din na ta harkar gabansu attending to patients da suka zo allura, Hafsat tace “Ko energy drink ne ki amso Ilham don kar ki zama weak anjima, naga jinin naki ya ɗan sauka kadan da na duba, kuma akwai operation har biyar yau…” Mayraah tace “Ai ba da ni za a shiga theatre din ba…” Bata rufe baki ba Dr khalil ya shigo Reception din daga meeting room, tun safe da suka shiga meeting sai yanzu suka fito, MD ma ya shigo reception din ya wuce Dr Khalil dake gaisawa da patients, a takaice ya amsa gaisuwar nurses din zai wuce sai kuma ya juya kallon Mayraah, keenly yace “Hey, i didn’t see u in any of the 2 meeting, are you a staff in here?” Nan duk nurses din suka maida hankalinsu kan Mayraah, wasu farin ciki fal cikinsu suna jiran jin me zata ce, Dr Khalil ya karaso yana kallon MD yace “Wannan satin ta fara aiki, kuma….” MD ya daga masa hannu yace “She should speak for her self pls” Yana fadin haka ya maida dubansa kan Mayraah a takaice yace “Madam me ya hanaki shiga meeting?” Mayraah ta nuna masa Dr Khalil a takaice ita ma tace “He have said it all” Ba MD ba, hatta Khalil was shock at her reply, Duk nurses din ma suka saki baki suna kallonta da mugun mamaki, Khalil ya dafa shoulder din MD yayi kasa da murya yace “I spoke to you about….” MD ya dakatar da shi yace “Meet me in my office” Daga haka ya wuce sama kamar zai tashi, Mayraah dai ko a jikinta don ko daga kai ta kallesa bata sake yi ba, Dr Khalil ya juya ya bi bayan MD din, Hafsat ta dawo gefen Mayraah tana zaro ido tayi kasa da murya tace “Ke Ilham why did u speak to him that way? Baya son raini fa? He is our boss Ilham” Mayraah ta kalleta tace “How did i speak to him, tambayata fa yayi kuma an riga an basa amsan tambayar da yayi min and he is still repeating the question” Wata nurse na hararanta tace “Kina wasa da aikin ki kenan yarinya, ko baki san shine MD din duk asibitin nan gaba daya ba, ke haka aka koya maki tarbiya a gidanku, kina ganin ya fara maki magana za ki mike tsaye da sauri ba wai ki zauna kina basa amsa ba cikin isa da gadara, who are you? Ke kamar kanki na hayaki daga fara aiki last week ko, to ina me tabbatar maki idan baki yi hankali ba yau shine karshen aikinki a asibiti nan ba dai MD kika ma rashin kunya ba, kin zata su Dr Hamid da Dr Balogun ne masu fasa maki kai wai kin iya aiki ko, to MD no go area ne, da kyar idan bazai yi firing dinki yau ba” Wata nurse din ta amshe tace “Ki kyale ta mana, yara duk sun je private University sun karbi Degree sun zo nan suna raina mana hankali suna maida mu bamu san me muke ba, to wa zata nuna ma iya aiki in ba karya ba” Mayraah dai bata ko kallesu ba balle ta basu amsa, infact kamar ma ba da ita suke ba, kai ita fa ba dole sai ta bar asibitin ta kama gabanta bata son isa da izza ga nurses ma sai raina mata hankali suke, abeg she can’t, Can dai ta kalli Hafsat warce da alama duk jikinta yayi sanyi don a kaf asibitin hatta likitocin kaffa kaffa suke da MD har ma fararen fatan, Mayraah ta kalleta as if whispering tace “Wai shine me asibitin ne wannan jaraba haka?” Hafsat tace “Aa, but he is in charge of everything” Mayraah tace “To su waye masu asibitin?” Hafsat tace “Ceo din ba musulmai bane kamar ma ba yan kasar nan bane, but MD is the Managing Director cause he is good at what he does, kowa shi ya sani” Hafsat ta marairaice tace “Ni tsorona kar yace zai yi firing dinki kin ga ko tanka ki bai yi ba ya wuce sama yace Dr Khalil ya bi sa” Mayraah ta kyabe baki ta dauke kanta tana wasa da farcenta, iyaka ta koma Suleja abun ta tayi ta bacci ba shikenan ba. Dr Khalil ya zauna kan kujera bayan ya gama sauraron MD yayi kasa da murya yace “Look Dr, yarinyar bata san ka bane, and satin ta daya kenan da fara aiki a nan, pls pls consider…” MD ya dakatar da shi sounding so pissed off yace “Plss I don’t want to see her in this hospital nace maka Khalil, bana son in sake sauka downstairs for any reason in ganta a asibitin nan seriously, banda kai waye kaga yake kawo health worker just like that inyi employing din sa ba tare da an bin proper procedure for the employment ba, ban ga CV ba, babu interview babu komai, infact ita ban ma kai ga ce maka komai kan employment din nata da ka min magana ba kawai ka sa ta fara xuwa aiki without my consent har ka bata uniform Dr, sannan yanzu from all indications naga rude workers ka fara kawo mana asibitin, so she should leave immediately pls, bamu da vacancy” Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace “Kai matsalata da kai saurin hawa, ka ma ki tsayawa ka saurareni” MD ya mike ya buga table dinsa yana kallonsa da kyau yace “Bazan saurareka ba Khalil, she have to leave this hospital immediately ko in kira security yanzu su fidda ta” Murmushi khalil yayi yace “Kasan er wacece?” MD ya koma ya zauna calmly as if counting his words yace “I don’t care” Khalil ya mike yace “Kayi hakuri ka bata second chance pls, ni kaina nasan bata kyauta ba but she seriously needs this job, nasan kai me hakuri ne don Allah ka janye batun bazata sake aiki ba, idan ya so i can tell her idan ta tafi yau she should stay back home har sai ka bata employment din fully kafin tayi resuming” MD ya mike yace “She should stay back home, i am not employing her at all, i mean my words” Dr Khalil ya juya ya fita daga office din ya sauka floor din da office dinsa yake, yana zaune office ya kira downstairs yace a turo masa Mayraah, ba a dau lokaci ba ta shigo office din nasa tana kallonsa, sai da ya mata izinin zama sannan ta zauna, a hankali yace “Ilham me yasa kika yi ma MD magana rudely?” Mayraah tace “Did my words sound rude? Ni wallahi ban sani ba” Kallonta kawai yake, ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds Khalil ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yace “Yanzu ki tashi ki je office dinsa ki basa hakuri politely, and be careful with ur words pls Ilham, speak to him politely kice yayi hakuri kinyi kuskure baxa ki sake ba, talk to him remorsefully” Mayraah ta zaro ido tace “Office dinsa kuma?” Khalil yace “You have to Ilham, office dinsa na last floor”
mikewa mayraah tayi ta fita daga office din dr khalil bayan ya bata direction din zuwa office din md, jingina tayi da bango tana tunanin yanda zata fara zuwa office din nasa, in taje sai tace masa me? bayan few seconds ta fara tafiya zuwa last floor walking slowly, with direction din dr khalil ta isa har door din office din wanda bayan shi babu wani office a wajen, tana ta tsaye bakin kofar ta kasa knocking taji an bude kofar ta koma baya da sauri, wani dr ne ya fito ta gaishesa ya amsa da murmushi ya bar mata door din a bude ya wuce, a hankali ta saka kai ta shiga office din that was extra large, it was damn chill ga kamshin freshner da ya hadu da sanyin office din, everywhere was so organize and tidy, ya daga kai yana kallonta don bai san ta shigo ba, sosai gabanta ke faduwa ta kulle masa kofar kafin ta karaso cikin office din a takaice yace “get out and shut d door behind you…..” mayraah ta daga kai ta kallesa, lkci daya ta ɗan hade rai ta juya ta fice daga office din ta kulle masa kofar. ko office din dr khalil bata koma ba balle ta gaya masa yanda suka yi, ta sauka downstairs kawai intention dinta tayi wucewarta gida a lkcn don ta riga tayi making din mind dinta bazata sake barin komai ya dameta a rai ba, gwara ta ci gaba da lallaba low bp din da ta samu all of a sudden, she will never allow anything weigh her down cause babu kuma abinda ya rage mata bata gani ba a rayuwar nan, zata tafi inda zata dau jakarta kenan wani dr ya ganta ya kirata zuwa theatre room, duk nurses din reception suka bi ta da kallo wasun su na kyabe baki, mayraah na shiga theatre din taga 2 nurses already a ciki, the theatre is already set for the surgery that was going to start soon, ta saka surgeon gown da hula tayi decontaminating hands dinta ta saka gloves with nosemask, bata dai san surgery din da za ayi ba, but she will just be assisting with surgical instruments don abinda likitan ya nuna mata kenan tun shigowar ta, after few more minutes tana juyawa taga md ya shigo theatre din gabanta yayi mugun faduwa ta dauke kai da sauri don ma dai fuskarta da nosemask, wani dr that will not be part of d surgery yayi assisting dinsa wajen saka protective wears sannan ya fita, md ya wanke hannuwan sa, ita dai bata yarda ta sake dago kai ba tayi facing din instruments dake gabanta. mayraah wished dr salim zata dinga mika ma instruments din gabanta not md, babu yanda ta iya don shine kan surgery din, though su ma da nasu part din da za su yi playing, fatan ta dai bazai gane ita bace duk da bata barin su hada ido take mika amsa duk abinda ya bukata babu ɓata lokaci, after working for long, tsabar yanda ta fara gajiya taje zata maida wani instrument ta dau wani kawai ya fadi a hannunta, da sauri ta durkusa ta dauka ta mayar cikin sauran yan uwansa, ba shi md ba har su kansu doctors dake wajen where took aback da abinda tayi, nan da nan tayi realizing mistake din gabanta ya fadi, maimakon tayi sterilizing wanda ya fadi sai kawai ta hada da sauran equipment din, contaminating them also, dole aka dauko wasu instruments din nan take don ta yi contaminating dinsu kenan, at last dai suka gama operation din successfully aka fitar da patient din zuwa ward, tana ta allah allah ta fita bayan ta cire gown din jikinta da gloves taji husky voice din md dake facing dinta yace “where is ur theatre hygiene?” wani dr ya mata alamar ta sauke nosemask dinta, tayi yanda yace a hankali tana kallon md din ba tare da tace masa komai ba, sai a sannan md yasan ita ce a theatre din, after looking at her from head to toes kawai ya fice daga theatre din zuwa office din dr khalil. maheer ya fito daga office din likita da takarda a hannunsa yana kallon ammi dake zaune da hajja a reception, ga badiyyah rungume jikin hajja tana ta mata sannu, hajja tace “wai ba gado za su bata bane maheer? tana jin jiki fa, nasan ba komai bane illa cizon sauron inda marasu tsoron allah nan suka kai ta” maheer yace “sun ce ba sai an kwantar da ita ba ya rubuta magunguna za a siya” hajja tace “to allurai fa” badiyyah ta marairaice da kyar tace “ni bana son allura” ko kallonta maheer bai yi ba yace “ku tashi mu tafi gida” hajja ta mike ta dago badiyyah, ammi zata riko badiyyan hajja tace “aa bar ta kawai ki ji da kanki tunda kema ba isasshen lafiyar gareki ba” a haka suka fita maheer na biye da su a baya, suna shiga motar hajja tace “gida kawai za ka kai ni, na sa mariya taje ta min share share ta daura girkin da zata kawo mana asibiti ban ma san baza su bamu gado ba” shi dai maheer bai ce komai ba, after 30 mins of driving ya iso gidan hajja yayi parking, hajja ta sauka tare da badiyyah ammi zata sauka yace “ammi we need to talk” ammi ta kallesa sai kuma ta koma motar, tuni hajja ta shige cikin gida da badiyyah tana mata sannu, maheer ya mika ma ammi takardan hannunsa, haka kawai ammi ta ji gabanta ya fadi, ta dinga kallon takardan kafin ta amsa tace “na meye” bata jira cewarsa ba ta fara warware takardan, sai kuma ta kallesa da sauri tace “ka gaya min na meye ni ba ganewa zan yi ba maheer” ya sauke idonsa kasa yace “she is pregnant…. 4 weeks pregnant” ammi da gabanta ya wani yanke ya fadi ta saki takardan ta jingina da kujeran motar tana zaro ido tace “innalillahi wa inna ilaihi rajiun, ita badiyyar??” maheer dai bai sake cewa komai ba, nan da nan hawaye ya cika idon ammi ta dinga nanata innalillahi wa inna ilaihi raji’un jikinta na ɓari, gaba daya ta rikice a motar sai maganganu take daga karshe ta bude motar ta sauka kawai ta shige gidan hajja cikin tashin hankali, maheer ya ja motarsa ya kara gaba, ammi na shiga parlor ta tarar da hajja rike da badiyyah da ta kirba amai nan tsakar parlorn, hajja sai sannu take mata tana cewa “to nace a kwantar dake ance min ba haka ba, ya zan musu, tun dawowarku zuwa yanzu kinyi amai yafi a kirga gashi cikin babu komai” mama ladi dake zaune parlon sai yamutse fuska take tace “yanzu fisabilillahi ita yarinya ce ma da zata sako amai daga tsaye? ko yaro yaji amai ya san inda zai je yayi” a fusace hajja ta dakatar da mama ladi tace “ban gayyato ki gidana ba ladi? uban me ma ya kawo ki in ba neman magana ba, yaushe rabon da ki tako cikin gidan nan??” ammi ta fashe da matsanancin kukan takaici tace “kin cucemu badiyyah, kin cuce mu….” aunty mariya ta fito kitchen da sauri tace “lafiya ammi? me ke faruwa kuma” ita kanta hajja kasake tayi tana kallon ammi jin furucin da take ma badiyyah, mama ladi ta mike da sauri tace “auzubillahi wani satan ta sake yi kuma?” ammi na kallon aunty mariya cikin tashin hankali duk jikinta na rawa tace “mariya ciki ne da badiyyah har na sati hudu, mariya ki gaya min ta ina za mu fara mariya” wani ihu mama ladi tayi tace “ciki fa kika ce ammi? cikin ɗan mutum ko me?” ko rufe baki mama ladi bata yi ba suka ga hajja ta sulale kasa.
mayraah na fita daga asibitin bayan ta isa bakin titi inda zata je ta samu abun hawa taji wayarta dake jaka na vibrate, ta bude jakar ta ga khalil ne ke kiranta, ƙin dagawa tayi ta mayar da wayar tana duba cash din jakarta taga babu ma cash din sai dubu daya don kusan kullum idan ta fito tana siyan energy drink biyu wani lokacin har uku saboda low bp dinta sannan tana yin transport din komawa gida shi yasa cash din bai dade mata, nan ta hau dube duben atm card dinta bata gani ba a jakar sai na usman kawai, tunanin inda ta jefa nata ta fara yi, ko dai ta bar shi a daki ne can gidan ummi the last time da tayi using dinsa ko kuma ya fadi ne bata sani ba, tunanin faduwan yasa hankalinta ya tashi, ta rasa yanda zata yi gashi yau dama bata yi niyyar komawa gidan ummi ba suleja kawai zata wuce abun ta, can dai da ta gaji da tsayuwa ta ciro atm card din usman tana jujjuyawa tana nazarin tayi amfani da shi ko kar tayi a ranta, wani me adaidaita sahu ta tare tace masa inda zata cire kudi take son ya kai ta, tana shiga bayan sun yi tafiyar like 15 minutes yace “ga wani banki hajiya” ta kalli bank din tace “mu je dai, bana son cire kudi a wnn bankin din” haka yayi ta tafiya da ita suna ta wuce bankuna da dama sai tace su je wani, har dai mai adaidaita sahun ya gaji yace “hajiya kudin ki fa yawa yake, kar mu je muna wallahi tallahi a hanya” mayraah tace “ba damuwa mu je zan baka ko nawa ne” daga karshe dai bayan tafiya me tsayi tace masa ya tsaya, ta sauka tana kallonsa tace “amma zaka yi hakuri in cire kudin in dawo yanzu” ya wani hade rai yana kallonta, can ya kashe napep dinsa ya sauko yanda zai dinga ganinta da kyau yace “ina jira” shiga bank din tayi ta tafi atm machine din, duk da yanda gabanta ke faduwa haka ta saka ta fara cire dubu goma tukun, ai ko ya ciru, bayan nan ta sa 50k shi ma ta cire sannan ta maida atm card din cikin jakarta da sauri ta fito ta dawo gun mai adaidaita sahun ta shiga tace “mu tafi” yace “mu je ina?” tace “inda zan samu motar zuwa suleja zaka kai ni” yace “to bani kudin kawo ki nan da nayi tukun” dubu biyar ta kirga ta basa amma duk ta kagu su bar wajen, yana amsan kudin bayan ya ga nawa ne ya tada adaidaita sahun suka bar wajen, sai kusan magrib mayraah ta iso suleja a gajiye ga yunwa da take ji don har wani juya mata kanta yake, bayan ta sauka a daidaita sahun da ya kawota anguwan nasu don yace bazai shiga layin ba haka ta fara trekking zuwa cikin layin tana tafiya a hankali, tun daga nesa take kallon motar da ta hango anyi parking few houses before her’s babu ko kiftawa. Har Mayraah ta isa dai dai inda aka yi parking motar bata daina kallon motar ba, as if tana son tabbatar da motar waye, kasa ci gaba da tafiya tayi zuciyarta na bugawa ganin an bude kofar motar alamar wanda ke ciki zai sauko, idonta na kansa har ya sauko ya kulle motar ya rungume hannu yana kallonta without blinking, ta wani hade rai ta ci gaba da tafiya kamar zata tashi sama, zata wucesa yace “Ilham” a mugun fusace ta juyo tace “Me yasa kake bibiyata? And how did u get here??” Yana kallonta directly yace “Saboda tun daga first day din da Ahmad ya kawo ki hospital baki da lafiya na gano da yawa daga maganganunki karya ne, nasan karya kike tun a sannan, u never called ur people that very night da Ahmad ya baki waya ki kirasu, wasu nambobi daban da kika san basa amfani kika yi dialing, don har yau i have the 2 numbers na karba gun Ahmad kuma ina kira inji a kashe, wacece ke? Why did u chose to say all sort of lies about so many things to me? Take a look at ur self, baki yi kama da warce tasan wani abu wai shi wahala ba a rayuwa, baki yi kama da warce ta fito daga gidan da sai an tara kudin admission kafin ki taho makaranta ba, sannan a ilimin ki da wayewarki bazan yarda cewar baki san anyi terminating admission dinki kika taho Abuja ba, show me the admission list kin ki, wani school ne kin ki fada min, ke da kika tsaya tara kudin makaranta da kyar ta yaya ma za kiyi lodging hotel me tsadan nan, har kiyi ikirarin zaki iya kama gidan dubu dari uku a Abuja, so many unnecessary lies, kin ce sunanki Mayraah kin dawo kince Ilham u think i forgot, and worst of all ke kadai kike zaune gidan da zaki shiga yanzu not with anybody kamar yanda kika yi claiming cewar gidan stepmom dinki ne, har briefing dinki labarin rayuwata nayi duk don ki zama relax and tell me a little about ur self amma kin ki, ban san mission dinki a Abuja ba, amma baki yi kama da warce ta fito daga gidan da ba tarbiya ba, you look decent and well brought up, as a medical Dr na hango depression a idanuwanki, damuwa na daga cikin abinda ke contributing na low bp dinki…. Nayi kokarin ganin kin fara aiki a hospital din ko zai canza maki thinking dinki akan abubuwa da dama da ya shafi rayuwarki amma naga ba haka bane, and kin nuna u are not even after the job, u are not desperate about it, sannan u don’t mind being fired, that aside kina da enough cash a tare da ke” Mayraah ta kasa ci gaba da kallonsa nan da nan hawaye ya cika idonta, kasa daurewa tayi ta hade kanta da motar ta fashe da kuka sosai, shi dai kallonta kawai yake, can ya sauke ajiyar zuciya yace “Zan je masallaci, ana kiran sallah, ki shiga ciki kiyi sallah, idan na dawo masallaci i will call u out” Kai kawai ta gyada masa hawaye na sauka idonta ta wuce sa ta karasa gate din gidanta ta ciro makulli a jaka ta bude ta shiga ciki, sai a sannan ya dauke kai daga kallonta ya karasa masallacin da ya ji ana kiran sallah.
Mayraah na zaune kan darduma tun da ta idar da sallan magrib, har sannan ta kasa daina kuka don ya famo mata ciwon da ke cikin zuciyarta, bata taɓa sa wa a rai wai zata zauna ta gaya ma wani anything about her self ba, she just want to be, bata son tana tuna abinda zai dameta, juyawa tayi tana kallon wayarta dake vibrate, can ta jawo ta daga ta kai kunne, Dr Khalil yace “Ina jiran ki” Ta sauke idonta bata ce komai ba ya katse wayar, bayan few minutes ta mike ta linke darduman ta fita waje, tana tafiya a hankali ta karasa har gun motar yana zaune driver seat leaving the door open, hakan ya sa ta zaga ta bude front seat ta shiga ta zauna ba tare da ta kallesa ba tana fidgeting fingers dinta, shi dai kallonta kawai yake, can yace “Mayraah” Ta daga idanuwanta ta kallesa yace “Tell me who u are, me ya kawo ki garin Abuja” Nan da nan hawaye ya cika idonta, yace “Assuming i have any other intention toward u kinsan bazan kai ki gidanmu ba, ko ince gidansu matata, duk abubuwan nan da kika ga nake ta kokarin yi a kanki don bana son kije ki fada wani hali ne ba don komai ba, ni mutum ne me tausayi kowa ya sani so i have no bad intention toward u, don kin gaya min wacece ke iyaka idan naga da inda zan baki shawara sai in baki kuma bazan baki shawaran da zai cuce ki ba, idan kuma taimako ne da bai fi karfina ba sai in maki, trust me Mayraah” Ta goge hawayen dake sauka idonta ta gyada masa kai, a hankali tace “Sunana Mayraah Mahmud…” Ya gyada mata kai yana kallonta, tace “I was born and brought up in kano” Sai kuma ta fashe masa da kuka yace “Kin ga kiyi hakuri, be strong and tell me what u want to tell me” Nan ma kai ta gyada masa tana goge hawayen da ya ki tsaya mata…. Mayraah bata boye masa komai game da rayuwarta ba har zuwa ranan da ta bar garin Kano, she told him every single thing, shi dai Dr Khalil kallonta kawai yake cike da tausayinta, abu biyu kadai ne yaji tausayinta a kai a duk labarin nan da ta basa, na farko wa enda take kallo a matsayin iyaye tun tasowarta bayan shekaru 22 ta gano ba su ne iyayen nata ba, he can’t imagine this great disappoinment, na biyu kuma fasa aurenta da aka yi saboda rashin sanin asalinta, shine kawai tausayinta da ya ji amma ita irin upbring din da ta samu ma mutane da yawa dake tare da iyayensu basu samu kwatankwacinsa ba, ta taso cikin gatanta da soyayya ta ko ina, she lived a comfortable life har zuwa sanda calamity din nan yayi befalling dinta, can ya tallabi chin dinsa yace “Mayraah” Ta daga jajayen idonta tana kallonsa yace “Ur story is not enough to leave home, baki ma Abbanki halacci ba, ita ma Ummin baki mata uzuri ba, da kin tuna irin soyayyar da ta maki tun baki san kanki ba na tabbatar babu abinda zai yi motivating dinki ki bar gida, sannan yayyinki maza su ma baki masu halacci ba” Cikin kuka tace “May be u are saying all this because u are not in the shoe, kowa zai dinga gani kamar it’s easy but u promise u it’s not, it’s painful, i tried my best to be fine with them amma daga karshe kawai naga idan na ci gaba da zama zuciyata zata iya bugawa at anytime, i can’t stand Ammi not talking to me a gidan bayan ba haka na taso take min ba, at the end su ma yayyin nawa avoiding dina suka fara yi ai, Abba did marry because of me….” Ta kasa ci gaba ta fara wani kukan, Dr Khalil yayi kasa da murya yace “Zaki koma gida Mayraah! dole za ki koma gida” Ta share idonta tana kallonsa tace “Bazan koma ba anytime now, idan kuma kace zaka takurani i am leaving Abuja…. i promise u” Da mamaki yake kallonta, can yace “To ke yanzu halaccin da zaki masu kenan? Kika san halin da suke ciki bayan barin ki gida?” Tace “Ba halaccin da zan masu ba kenan, i will never forget their good deeds and they still remain my parents har ko da yaushe, bani da kowa sama da su, kawai dai ina son in bada space ne zuciyar kowa yayi sanyi… Ina son komai ya dawo dai dai a family din, tunda ta dalilina kaga yanda abubuwa marasu dadi suke ta faruwa, i am the caused of everything, tun daga sanda aka fasa aurena abubuwa ke ta faruwa, i am blaming my self for everything” Dr Khalil yayi shiru kamar me nazari, can yace “Ya ma kika ce sunan yayan naki that is a Medical Dr?” Ta wani kallesa tace “I don’t think that is necessary” Ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips yace “Ohk then, kin samu labarin fitowar result dinku na makaranta?” Ta girgiza kai a hankali tace “Bani da contact din kowa yanzu” Ya sauke ajiyar zuciya yace “Shikenan” Bai sake cewa komai ba ita ma haka, and they were silent for almost 3 minutes kowa da tunanin da yake a ransa, A hankali tace “It’s getting late, kuma zaka koma Abuja” Gyara zamansa yayi ya sauke ajiyar zuciya yace “Haka ne, amma don Allah ina son kiyi hakuri ki daina dawowa Sulejan nan kwata kwata saboda ke macece bai kamata ki kama gida ke kadai ki dinga rayuwa ciki ba, don’t forget everyone is watching u, za a maki fassaran me zaman kanta….” Mayraah ta kallesa tace “How did u find out nan da nake?” Yace “Nace maki tun farko dama ni ban taɓa yarda dake ba ko na second daya, though confidently kike karyanki but facial expression dinki ke exposing dinki, ina me baki shawara next time ki daina karya bai yi fitting dinki ba kuma za a gano ki cikin few minutes….” Ta sunkuyar da kanta, yace “I came here through ur neighbor’s Husband, yarinyar da ta rasu kwanaki a hospital, i had to trace the man’s number, don ranan da za su zo daukar gawan yarinyar yayi ta kirana ban daga ba ina aiki, sai yayi min text message, so sai da nayi tracing text message dinsa sannan na samu number” Mayraah ta wani hade rai tace “To banda sa ido irin na mutane shine har yace maka ni kadai nake rayuwa a gidan nan?” Yace “Aa bai ce haka ba, ce min yayi according to his wife ke student ce a jami’a, weekend kawai kike dawowa yi a gidan” Mayraah bata sake cewa komai ba, Dr Khalil yace “And lastly yanzu idan na bar nan zan je gidan MD, i will beg him on ur behalf cause dazu bayan tafiyarki ya shigo har office ya sameni, ke da nace kije ki basa hakuri sai kika ki basa kika yi masa kerere a bakin kofa, why Mayraah…” Da sauri ta wani hade rai tace “Ta yaya zan basa hakuri bayan yace in fita daga office dinsa” Dr Khalil ya ɗan yi murmushi yace “Ai yana cewa ki fita baxa ki fita ba zaki fara basa hakurin cikin ladabi, not to just walk out don yace ki fita” Mayraah ta kauda kai, Dr Khalil yace “Ba aikin kike bukata ba sbda ke ba shi ne ma a gabanki ba shi yasa u won’t mind ko kin rasa aikin da thousand of people ke nema, but i wont allow that happen sbda bana son ki sake zama Sulejan nan, ban ga alamar an maki tarbiyar da zaki zama me zaman kanta ba” Ita dai bata ce komai ba, yace “Ki shiga gida sai da safe, gobe ki shirya ki taho asibitin” A hankali ta bude motar ta sauka, sai da ya ga shigarta gidan sannan ya bar layin a ransa yana nanata sunan Maheer da ta ambata masa a labarin da ta basa, sai kusan karfe tara saura ya shigo Abuja, yana parking bakin gate din gidan MD wayarsa ya fara ring, yana dubawa yaga Zainab ce, murmushi yayi, yayi silencing wayar don yasan taga bai dawo bane yasa ta kirasa, ya lura da ita duk kwanan nan she is acting insecured akansa, ya gaisa da mai gadin gidan ya shiga, a parlor ya tadda MD with different textbooks a gabansa da laptop, Dr Khalil yace “Mun kusa fara ce maka professor fa mutumin nan” MD ya daga kai ya kallesa, Murmushi khalil yayi ya zauna yana facing dinsa yace “To ya ake ciki?” MD ya rufe laptop din gabansa yace “Next week fa zata shigo, ina ga her plan is to meet the workshop” Dr Khalil ya bude ido yace “Really, i tot kace makarantar da take lecturing za su yi commencing exams” MD yace “To haka dai ta ce min” Dr Khalil yace “Kace akwai ƙura kenan” MD ya daga kafada yace “Ita da Dr Ajay kenan, yaushe rabona da asibitin, ai ta sani” Dr Khalil yace “Lallai kam, MD alfarma na zo nema don Allah” MD ya kallesa, nan da nan ya hade rai yace “Ba dai maganar fitsararriyar yarinyar nan ya kawoka gidana ba” Dr Khalil ya girgiza kai yace “Wallahi kayi misperceiving dinta ne MD, she is so good sannan ta iya aiki” MD ya girgiza kai yace “Ban ga alama ba, wai ba ita bace ta kasa ba ma yarinya common injection ba a ward ranan, sannan muna aiki a theatre tayi contaminating mana equipments, how is she good, don Allah do not spoil my mood Khalil, kai ma kasan bamu da vacancy” Dr Khalil yace “Na sani, shi yasa nace alfarma pls” da mamaki MD yace “To ko dai budurwarka ce yarinyar nan?” Dr Khalil yayi dariya yace “Kai ma kasan daga Madam dita ai babu kari” MD ya ɗan yi tsaki yace “Wallahi i hate dealing with rude human beings, zaka takurani Khalil” Dr Khalil yace “Ka dai yi hakuri don Allah” MD ya kara jan tsaki, bayan few seconds yace “Ina CV dinta?” Khalil ya shafa kansa yace “Za a kawo” MD yace “Till then” Khalil yace “Don Allah kafin su Madam su shigo kasar nan ka bata aikin nan, kasan in suna nan it will be hard wllh” MD yace “Ka ma maida ni ban san abinda nake ba Khalil, ta yaya zan bada aiki babu CV?” Khalil yace “Ko Hafsat ba sai daga baya aka kawo ba, kuma me wuyar dama mutum yayi graduating ko” MD yace “Don Allah lokacin kwanciya na yayi, in dai yarinyar nan ne bazan bata aiki babu takardu ba, apart of takardu sai nayi interviewing dinta, kuma idan naga she is not fit for the job Billah sai dai kayi hakuri bazan bata ba kaji har na rantse, even after the interview idan tayi passing kenan she will be starting as an Enrolled nurse” Khalil yayi shiru yana kallonsa, can a hankali yace “Enrolled nurse kuma MD” MD ya fara tarkata textbooks dinsa da nufin barin parlon, Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace “Toh shikenan ba matsala, amma a fara interview din tukunna pls” MD yace “Then she should come together with an apology letter in 2 days time, gobe bani da lokacinta haka ma jibi, sai ta bari on Sunday kenan idan Allah ya sa na shiga Asibitin” Yana gama fadin haka yace “I will be going to Bed Khalil” Khalil ya ɗan yi murmushi ya mike yace “To shikenan, thank you sir, Allah ya tashe mu lafiya” Daga haka ya bar parlon. Maheer dake zaune dakin Usman sai kallonsa yake har ya rufe hand luggage dinsa, can Maheer yace “When did u see the debit alert?” Ba tare da Usman ya kallesa ba yace “Not long ago” Maheer yace “To yanzu ina za ka?” Usman yace “I contacted my account officer ya sanar min a Abuja ta cire kudin” Da mugun mamaki Maheer yace “Abuja?” Usman dai bai ce masa komai ba, Maheer yace “Yanzu Abujan zaka tafi da daddaren nan?” Usman yace “Yeah” Maheer yace “But… Ta yaya za ka fara tracing nata a garin Abuja that is wide??” Usman yace “Watch and see, i have been waiting for this day dama” Maheer ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, tun da Usman ya kirasa ya sanar masa Mayraah ta cire kudi a account dinsa yaji wani kwanciyar hankali ya zo masa don the silence is too much, shirun ne yasa duk hankalinsa ya tashi, but tunda har ta cire kudi ya nuna she is fine and doing well kilan kudin account dinta ya kare kenan, Maheer yace “But ya kamata ka fara zuwa gidan Hajja ka dubata har yanzu she is not saying anything, she is really shock” Usman ya kallesa yace “Wani abu ya faru ne da zan je dubata?” Buda baki Maheer yayi yana kallonsa don sarai yasan abinda ke faruwa duk commotion din nan da aka yi throughout yau yana sane amma yaki tofa nasa, Maheer ya mike ya dafa shoulder dinsa yace “Saboda Ammi zaka yi Usman, ni ma ba don Ammi ba i won’t involve my self in this, yanzu haka can zan tafi, kayi hakuri mu je tare” Usman bai ce masa komai ba suka fita gidan a tare. Maheer ne ya fara shiga parlon Hajja da sallama Usman na biye da shi a baya, Hajja na kwance an sa mata drip sai bin kowa take da ido tana numfashi sama sama, Mama Ladi na gefenta sai fifita take mata ta tsuke baki, Ammi da idanuwanta yayi jajir ita ma tana zaune kasa har a sannan bata daina kukan da take ba, Aunty Mariya dai tayi tagumi, Abba ma na zaune parlon don ko minti biyar bai yi da shigowa ba su Maheer suka zo, Maheer ya karasa kusa da Hajja yana dubata, Mama Ladi ta fashe da kuka tace “Mashir ni dai da kawai a tafi asibiti a duba min er uwa da kyau, naga kamar karkacewa bakin nata yake kokarin yi, ita kenan gareni a rayuwar nan fa ka rufa min asiri mu tafi asibiti” Maheer yace “Ko mun je asibitin abin nan da nake shi za a mata, in sha Allah zata samu sauki” Shi dai Usman na tsaye bakin kofa, Abba ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Ammi for the first time yace “Ina Badiyyar?” Mama Ladi tace “Er iskar na daki in gaya maka Mamuda, wa ma zai bi ta kanta muna kokarin ceton ran er uwata wallahi ko sanin halin da take ciki bamu yi ba yanzu haka, kawai yanzu tunda zaratan mazan nan sun shigo kamata yayi su risketa a dakin da duka ta fadi uban da yayi mata ciki duk mu ji, tun dazu nake ce ma Ammi da Mariya su shiga su tambayeta cikin waye sun ki hankalinsu na kan lafiyar uwarsu” Abba ya sunkuyar da kai yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Sai ga hawaye na sauka idon Hajja, Mama Ladi ta fashe da kuka tana goge mata hawayen da dankwali tace “Tun dazu a haka take, sai dai kawai mu ga hawaye na bin gefen idonta ni dai na shiga uku na lalace Badiyyah ta cucemu” Abba na kallon Maheer yace “Kira min ita” Maheer bai so wannan aiken na Abba ba, don shi kansa tun dazu bai sa Badiyyah a ido ba bai kuma tambayi isilinta ba ya ma zata ta gudu ta bar gidan, amma bai ma Abba musu ba ya mike ya tafi zuwa dakinta, bude kofar yayi ya shiga ya ganta kwance kasa kamar warce ta yi wata uku tana jinya da alama har yanzu ko ruwa bata samu ta kai baki ba, tana ganinsa ta rushe da kuka ta mike zaune da kyar tace “Yaya don girman Allah ka rufa min asiri ka bani magani in cire cikin nan” bata rufe baki ba ya sauke mata lafiyayyen mari yayi ball da ita yace “Ni kike ce ma in baki magani ki cire ciki?” Bude kofar yayi fuskarsa a murtuke yana nuna mata waje yace “Fita ki je ki gaya masu who is responsible kar in kakkarya ki” Jikinta na rawa ta fara rarrafe zuwa bakin kofar don ko tashi bazata iya ba, rakubewa tayi jikin pillar dake corridor din tana kallon mutanen parlon hawaye na sauka idonta, Abba da Mama Ladi sai Usman kawai ke kallonta, don Ammi kauda kai tayi haka ma Aunty Mariya da zuciyarta ke tafarfasa, Mama Ladi na nunata da yatsa tayi mitsi mitsi da ido tace “Allah ya isa tsakaninmu da ke Badiyyah, kaf zuri’a ba a taɓa dauko mana abun kunya ba sai a kanki, Allah ya isa bamu yafe ba, yanzu da wani ido za mu kalli yan ubanmu?” Sai kuma ta rushe da matsanancin kuka tace “Ba don mun zama daya da Mamudan ba shi kansa da wani ido za mu kallesa wannan abun kunya haka a pamily dinmu” Abba na kallon Badiyyah calmly yace “Who is responsible?” Ta kara makalewa jikin pillar tana zazzare ido kamar me nazarin abinda zata ce, Abba ya sake jefo mata tambayar still looking at her, ta daga kai a hankali ta kalli Maheer.
Mayraah na zaune kan darduma tun da ta idar da sallan magrib, har sannan ta kasa daina kuka don ya famo mata ciwon da ke cikin zuciyarta, bata taɓa sa wa a rai wai zata zauna ta gaya ma wani anything about her self ba, she just want to be, bata son tana tuna abinda zai dameta, juyawa tayi tana kallon wayarta dake vibrate, can ta jawo ta daga ta kai kunne, Dr Khalil yace “Ina jiran ki” Ta sauke idonta bata ce komai ba ya katse wayar, bayan few minutes ta mike ta linke darduman ta fita waje, tana tafiya a hankali ta karasa har gun motar yana zaune driver seat leaving the door open, hakan ya sa ta zaga ta bude front seat ta shiga ta zauna ba tare da ta kallesa ba tana fidgeting fingers dinta, shi dai kallonta kawai yake, can yace “Mayraah” Ta daga idanuwanta ta kallesa yace “Tell me who u are, me ya kawo ki garin Abuja” Nan da nan hawaye ya cika idonta, yace “Assuming i have any other intention toward u kinsan bazan kai ki gidanmu ba, ko ince gidansu matata, duk abubuwan nan da kika ga nake ta kokarin yi a kanki don bana son kije ki fada wani hali ne ba don komai ba, ni mutum ne me tausayi kowa ya sani so i have no bad intention toward u, don kin gaya min wacece ke iyaka idan naga da inda zan baki shawara sai in baki kuma bazan baki shawaran da zai cuce ki ba, idan kuma taimako ne da bai fi karfina ba sai in maki, trust me Mayraah” Ta goge hawayen dake sauka idonta ta gyada masa kai, a hankali tace “Sunana Mayraah Mahmud…” Ya gyada mata kai yana kallonta, tace “I was born and brought up in kano” Sai kuma ta fashe masa da kuka yace “Kin ga kiyi hakuri, be strong and tell me what u want to tell me” Nan ma kai ta gyada masa tana goge hawayen da ya ki tsaya mata…. Mayraah bata boye masa komai game da rayuwarta ba har zuwa ranan da ta bar garin Kano, she told him every single thing, shi dai Dr Khalil kallonta kawai yake cike da tausayinta, abu biyu kadai ne yaji tausayinta a kai a duk labarin nan da ta basa, na farko wa enda take kallo a matsayin iyaye tun tasowarta bayan shekaru 22 ta gano ba su ne iyayen nata ba, he can’t imagine this great disappoinment, na biyu kuma fasa aurenta da aka yi saboda rashin sanin asalinta, shine kawai tausayinta da ya ji amma ita irin upbring din da ta samu ma mutane da yawa dake tare da iyayensu basu samu kwatankwacinsa ba, ta taso cikin gatanta da soyayya ta ko ina, she lived a comfortable life har zuwa sanda calamity din nan yayi befalling dinta, can ya tallabi chin dinsa yace “Mayraah” Ta daga jajayen idonta tana kallonsa yace “Ur story is not enough to leave home, baki ma Abbanki halacci ba, ita ma Ummin baki mata uzuri ba, da kin tuna irin soyayyar da ta maki tun baki san kanki ba na tabbatar babu abinda zai yi motivating dinki ki bar gida, sannan yayyinki maza su ma baki masu halacci ba” Cikin kuka tace “May be u are saying all this because u are not in the shoe, kowa zai dinga gani kamar it’s easy but u promise u it’s not, it’s painful, i tried my best to be fine with them amma daga karshe kawai naga idan na ci gaba da zama zuciyata zata iya bugawa at anytime, i can’t stand Ammi not talking to me a gidan bayan ba haka na taso take min ba, at the end su ma yayyin nawa avoiding dina suka fara yi ai, Abba did marry because of me….” Ta kasa ci gaba ta fara wani kukan, Dr Khalil yayi kasa da murya yace “Zaki koma gida Mayraah! dole za ki koma gida” Ta share idonta tana kallonsa tace “Bazan koma ba anytime now, idan kuma kace zaka takurani i am leaving Abuja…. i promise u” Da mamaki yake kallonta, can yace “To ke yanzu halaccin da zaki masu kenan? Kika san halin da suke ciki bayan barin ki gida?” Tace “Ba halaccin da zan masu ba kenan, i will never forget their good deeds and they still remain my parents har ko da yaushe, bani da kowa sama da su, kawai dai ina son in bada space ne zuciyar kowa yayi sanyi… Ina son komai ya dawo dai dai a family din, tunda ta dalilina kaga yanda abubuwa marasu dadi suke ta faruwa, i am the caused of everything, tun daga sanda aka fasa aurena abubuwa ke ta faruwa, i am blaming my self for everything” Dr Khalil yayi shiru kamar me nazari, can yace “Ya ma kika ce sunan yayan naki that is a Medical Dr?” Ta wani kallesa tace “I don’t think that is necessary” Ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips yace “Ohk then, kin samu labarin fitowar result dinku na makaranta?” Ta girgiza kai a hankali tace “Bani da contact din kowa yanzu” Ya sauke ajiyar zuciya yace “Shikenan” Bai sake cewa komai ba ita ma haka, and they were silent for almost 3 minutes kowa da tunanin da yake a ransa, A hankali tace “It’s getting late, kuma zaka koma Abuja” Gyara zamansa yayi ya sauke ajiyar zuciya yace “Haka ne, amma don Allah ina son kiyi hakuri ki daina dawowa Sulejan nan kwata kwata saboda ke macece bai kamata ki kama gida ke kadai ki dinga rayuwa ciki ba, don’t forget everyone is watching u, za a maki fassaran me zaman kanta….” Mayraah ta kallesa tace “How did u find out nan da nake?” Yace “Nace maki tun farko dama ni ban taɓa yarda dake ba ko na second daya, though confidently kike karyanki but facial expression dinki ke exposing dinki, ina me baki shawara next time ki daina karya bai yi fitting dinki ba kuma za a gano ki cikin few minutes….” Ta sunkuyar da kanta, yace “I came here through ur neighbor’s Husband, yarinyar da ta rasu kwanaki a hospital, i had to trace the man’s number, don ranan da za su zo daukar gawan yarinyar yayi ta kirana ban daga ba ina aiki, sai yayi min text message, so sai da nayi tracing text message dinsa sannan na samu number” Mayraah ta wani hade rai tace “To banda sa ido irin na mutane shine har yace maka ni kadai nake rayuwa a gidan nan?” Yace “Aa bai ce haka ba, ce min yayi according to his wife ke student ce a jami’a, weekend kawai kike dawowa yi a gidan” Mayraah bata sake cewa komai ba, Dr Khalil yace “And lastly yanzu idan na bar nan zan je gidan MD, i will beg him on ur behalf cause dazu bayan tafiyarki ya shigo har office ya sameni, ke da nace kije ki basa hakuri sai kika ki basa kika yi masa kerere a bakin kofa, why Mayraah…” Da sauri ta wani hade rai tace “Ta yaya zan basa hakuri bayan yace in fita daga office dinsa” Dr Khalil ya ɗan yi murmushi yace “Ai yana cewa ki fita baxa ki fita ba zaki fara basa hakurin cikin ladabi, not to just walk out don yace ki fita” Mayraah ta kauda kai, Dr Khalil yace “Ba aikin kike bukata ba sbda ke ba shi ne ma a gabanki ba shi yasa u won’t mind ko kin rasa aikin da thousand of people ke nema, but i wont allow that happen sbda bana son ki sake zama Sulejan nan, ban ga alamar an maki tarbiyar da zaki zama me zaman kanta ba” Ita dai bata ce komai ba, yace “Ki shiga gida sai da safe, gobe ki shirya ki taho asibitin” A hankali ta bude motar ta sauka, sai da ya ga shigarta gidan sannan ya bar layin a ransa yana nanata sunan Maheer da ta ambata masa a labarin da ta basa, sai kusan karfe tara saura ya shigo Abuja, yana parking bakin gate din gidan MD wayarsa ya fara ring, yana dubawa yaga Zainab ce, murmushi yayi, yayi silencing wayar don yasan taga bai dawo bane yasa ta kirasa, ya lura da ita duk kwanan nan she is acting insecured akansa, ya gaisa da mai gadin gidan ya shiga, a parlor ya tadda MD with different textbooks a gabansa da laptop, Dr Khalil yace “Mun kusa fara ce maka professor fa mutumin nan” MD ya daga kai ya kallesa, Murmushi khalil yayi ya zauna yana facing dinsa yace “To ya ake ciki?” MD ya rufe laptop din gabansa yace “Next week fa zata shigo, ina ga her plan is to meet the workshop” Dr Khalil ya bude ido yace “Really, i tot kace makarantar da take lecturing za su yi commencing exams” MD yace “To haka dai ta ce min” Dr Khalil yace “Kace akwai ƙura kenan” MD ya daga kafada yace “Ita da Dr Ajay kenan, yaushe rabona da asibitin, ai ta sani” Dr Khalil yace “Lallai kam, MD alfarma na zo nema don Allah” MD ya kallesa, nan da nan ya hade rai yace “Ba dai maganar fitsararriyar yarinyar nan ya kawoka gidana ba” Dr Khalil ya girgiza kai yace “Wallahi kayi misperceiving dinta ne MD, she is so good sannan ta iya aiki” MD ya girgiza kai yace “Ban ga alama ba, wai ba ita bace ta kasa ba ma yarinya common injection ba a ward ranan, sannan muna aiki a theatre tayi contaminating mana equipments, how is she good, don Allah do not spoil my mood Khalil, kai ma kasan bamu da vacancy” Dr Khalil yace “Na sani, shi yasa nace alfarma pls” da mamaki MD yace “To ko dai budurwarka ce yarinyar nan?” Dr Khalil yayi dariya yace “Kai ma kasan daga Madam dita ai babu kari” MD ya ɗan yi tsaki yace “Wallahi i hate dealing with rude human beings, zaka takurani Khalil” Dr Khalil yace “Ka dai yi hakuri don Allah” MD ya kara jan tsaki, bayan few seconds yace “Ina CV dinta?” Khalil ya shafa kansa yace “Za a kawo” MD yace “Till then” Khalil yace “Don Allah kafin su Madam su shigo kasar nan ka bata aikin nan, kasan in suna nan it will be hard wllh” MD yace “Ka ma maida ni ban san abinda nake ba Khalil, ta yaya zan bada aiki babu CV?” Khalil yace “Ko Hafsat ba sai daga baya aka kawo ba, kuma me wuyar dama mutum yayi graduating ko” MD yace “Don Allah lokacin kwanciya na yayi, in dai yarinyar nan ne bazan bata aiki babu takardu ba, apart of takardu sai nayi interviewing dinta, kuma idan naga she is not fit for the job Billah sai dai kayi hakuri bazan bata ba kaji har na rantse, even after the interview idan tayi passing kenan she will be starting as an Enrolled nurse” Khalil yayi shiru yana kallonsa, can a hankali yace “Enrolled nurse kuma MD” MD ya fara tarkata textbooks dinsa da nufin barin parlon, Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace “Toh shikenan ba matsala, amma a fara interview din tukunna pls” MD yace “Then she should come together with an apology letter in 2 days time, gobe bani da lokacinta haka ma jibi, sai ta bari on Sunday kenan idan Allah ya sa na shiga Asibitin” Yana gama fadin haka yace “I will be going to Bed Khalil” Khalil ya ɗan yi murmushi ya mike yace “To shikenan, thank you sir, Allah ya tashe mu lafiya” Daga haka ya bar parlon. Maheer dake zaune dakin Usman sai kallonsa yake har ya rufe hand luggage dinsa, can Maheer yace “When did u see the debit alert?” Ba tare da Usman ya kallesa ba yace “Not long ago” Maheer yace “To yanzu ina za ka?” Usman yace “I contacted my account officer ya sanar min a Abuja ta cire kudin” Da mugun mamaki Maheer yace “Abuja?” Usman dai bai ce masa komai ba, Maheer yace “Yanzu Abujan zaka tafi da daddaren nan?” Usman yace “Yeah” Maheer yace “But… Ta yaya za ka fara tracing nata a garin Abuja that is wide??” Usman yace “Watch and see, i have been waiting for this day dama” Maheer ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, tun da Usman ya kirasa ya sanar masa Mayraah ta cire kudi a account dinsa yaji wani kwanciyar hankali ya zo masa don the silence is too much, shirun ne yasa duk hankalinsa ya tashi, but tunda har ta cire kudi ya nuna she is fine and doing well kilan kudin account dinta ya kare kenan, Maheer yace “But ya kamata ka fara zuwa gidan Hajja ka dubata har yanzu she is not saying anything, she is really shock” Usman ya kallesa yace “Wani abu ya faru ne da zan je dubata?” Buda baki Maheer yayi yana kallonsa don sarai yasan abinda ke faruwa duk commotion din nan da aka yi throughout yau yana sane amma yaki tofa nasa, Maheer ya mike ya dafa shoulder dinsa yace “Saboda Ammi zaka yi Usman, ni ma ba don Ammi ba i won’t involve my self in this, yanzu haka can zan tafi, kayi hakuri mu je tare” Usman bai ce masa komai ba suka fita gidan a tare. Maheer ne ya fara shiga parlon Hajja da sallama Usman na biye da shi a baya, Hajja na kwance an sa mata drip sai bin kowa take da ido tana numfashi sama sama, Mama Ladi na gefenta sai fifita take mata ta tsuke baki, Ammi da idanuwanta yayi jajir ita ma tana zaune kasa har a sannan bata daina kukan da take ba, Aunty Mariya dai tayi tagumi, Abba ma na zaune parlon don ko minti biyar bai yi da shigowa ba su Maheer suka zo, Maheer ya karasa kusa da Hajja yana dubata, Mama Ladi ta fashe da kuka tace “Mashir ni dai da kawai a tafi asibiti a duba min er uwa da kyau, naga kamar karkacewa bakin nata yake kokarin yi, ita kenan gareni a rayuwar nan fa ka rufa min asiri mu tafi asibiti” Maheer yace “Ko mun je asibitin abin nan da nake shi za a mata, in sha Allah zata samu sauki” Shi dai Usman na tsaye bakin kofa, Abba ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Ammi for the first time yace “Ina Badiyyar?” Mama Ladi tace “Er iskar na daki in gaya maka Mamuda, wa ma zai bi ta kanta muna kokarin ceton ran er uwata wallahi ko sanin halin da take ciki bamu yi ba yanzu haka, kawai yanzu tunda zaratan mazan nan sun shigo kamata yayi su risketa a dakin da duka ta fadi uban da yayi mata ciki duk mu ji, tun dazu nake ce ma Ammi da Mariya su shiga su tambayeta cikin waye sun ki hankalinsu na kan lafiyar uwarsu” Abba ya sunkuyar da kai yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Sai ga hawaye na sauka idon Hajja, Mama Ladi ta fashe da kuka tana goge mata hawayen da dankwali tace “Tun dazu a haka take, sai dai kawai mu ga hawaye na bin gefen idonta ni dai na shiga uku na lalace Badiyyah ta cucemu” Abba na kallon Maheer yace “Kira min ita” Maheer bai so wannan aiken na Abba ba, don shi kansa tun dazu bai sa Badiyyah a ido ba bai kuma tambayi isilinta ba ya ma zata ta gudu ta bar gidan, amma bai ma Abba musu ba ya mike ya tafi zuwa dakinta, bude kofar yayi ya shiga ya ganta kwance kasa kamar warce ta yi wata uku tana jinya da alama har yanzu ko ruwa bata samu ta kai baki ba, tana ganinsa ta rushe da kuka ta mike zaune da kyar tace “Yaya don girman Allah ka rufa min asiri ka bani magani in cire cikin nan” bata rufe baki ba ya sauke mata lafiyayyen mari yayi ball da ita yace “Ni kike ce ma in baki magani ki cire ciki?” Bude kofar yayi fuskarsa a murtuke yana nuna mata waje yace “Fita ki je ki gaya masu who is responsible kar in kakkarya ki” Jikinta na rawa ta fara rarrafe zuwa bakin kofar don ko tashi bazata iya ba, rakubewa tayi jikin pillar dake corridor din tana kallon mutanen parlon hawaye na sauka idonta, Abba da Mama Ladi sai Usman kawai ke kallonta, don Ammi kauda kai tayi haka ma Aunty Mariya da zuciyarta ke tafarfasa, Mama Ladi na nunata da yatsa tayi mitsi mitsi da ido tace “Allah ya isa tsakaninmu da ke Badiyyah, kaf zuri’a ba a taɓa dauko mana abun kunya ba sai a kanki, Allah ya isa bamu yafe ba, yanzu da wani ido za mu kalli yan ubanmu?” Sai kuma ta rushe da matsanancin kuka tace “Ba don mun zama daya da Mamudan ba shi kansa da wani ido za mu kallesa wannan abun kunya haka a pamily dinmu” Abba na kallon Badiyyah calmly yace “Who is responsible?” Ta kara makalewa jikin pillar tana zazzare ido kamar me nazarin abinda zata ce, Abba ya sake jefo mata tambayar still looking at her, ta daga kai a hankali ta kalli Maheer.
Maheer ya wani hade rai ya daka mata tsawa yace “Baza ki bude baki kiyi magana ba kina bata ma mutane lokaci” Ta fashe da kuka a hankali tace “Wallahi Haseenah ce ta hada ni da shi ni ban san shi ba” Daga Ammi har Aunty Mariya basu san sanda suka juya da sauri suna kallon Badiyyah ba, Mama Ladi da ta gwalo ido tace “Wacece haka? Sunan fa matar Mashir naji ta kira ko dai kunnena ne jama’a? Sanisa dai da duka muka sani?” Cikin kuka Badiyyah tace “Wallahi ita ce ta hada mu, Malaminta ne shi yake mata aiki a Zaria” Salati Mama Ladi ta saki bayan ta ajiye maficin hannunta tana tafe hannu cikin kidimewa tace “Malaminta kuma?” Maheer kam kallon Badiyya kawai yake babu ko kiftawa kamar yanda Abba da Usman dake tsaye bakin kofa ma suke kallonta, Cikin rawan murya Badiyyah tace “Dama bayan an fasa auren Mayraah nace mata ina son Musharraf din ya dinga kulani, shine ta hadani da malamin wai ya iya aiki, shikenan mu ka fara waya da shi na fara tura masa dubu hamsin sai watarana yace in je Zaria zan amshi wasu turarruka da zan dinga amfani da shi, ni kuma sai nayi ma Hajja karya zan je Bichi sai na tafi Zaria wajensa” Tana kai wa nan ta kara rushewa da kuka, Mama Ladi dake ta zare ido tace “Sai aka yi yaya?” Cikin kuka sosai Badiyyah tace “Wallahi ni ban taɓa iskanci ba Haseenah ce ta hadamu da shi, kuma yace min shi ne ma yayi mata aiki har ta auri Ya Maheer, sannan ya bata asiri da ta kai dakin Ammi wai don Ammi taji ta tsani Mayraah, ita ma kuma ai tana zuwa wajensa a zaria sai da tayi aure ne ta daina zuwa wajen sa” Mikewa Mama Ladi tayi ta dafe gwiwa tana kallon Hajja da hawaye ke sauka ta gefen idonta tace “To Allah ya sa dai kunnuwanki basu samu matsala ba kina jin duk abinda marainiyar ki ke cewa, mu dai sai dai mu ce Allah ya isa lalata mana zuri’a da za ayi da shege, yau ga dai Badiyyah da cikin boka” Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka ta rike kanta, Ammi ma kukan take sosai wani bakin ciki da takaici na taso mata a zuciya, ita dai Aunty Mariya shock ya sa ko motsi ta kasa yi a inda take zaune sai kallon Badiyyah take, shi kansa Abba kallon Badiyyah kawai yake ko kiftawa babu, can ya girgiza kai ya mike kawai ya fita daga parlon, Usman ya juya ya bi bayansa, Maheer ya kusa minti biyar tsaye parlon da tunani iri iri a ransa, can ya nufi kofa ya fita shi ma, Ammi ta mike ta bi bayansa da sauri har a sannan tana kukan takaici, tsayawa yayi har ta karaso inda yake cikin rawan murya tace “Yanzu Maheer ta yaya za ayi a cire cikin nan? Ya za mu yi yanzu ya fita Maheer?” Da mamaki Maheer ke kallonta yace “A cire fa kika ce Ammi?” Ta fashe da kuka tace “To me zance Maheer? da wani ido za mu kalli duniya? Wannan abun kunyar har ina Maheer? Badiyyah ta cuce mu, ta cuce mu wllh” Maheer ya girgiza kai yace “Ai in ma wani ya kawo shawaran a cire cikin ke me hanawa ne Ammi” Muryar Mama Ladi suka ji da karfi tana cewa “Ashe baki da kai Ammi? Ina maki kallon me ilimi ashe ba haka bane? Wani cikin za a cire? So kike Allah yayi fushi da kaf zuri’ar mu? Ga laifin zina sannan ga na zubar da ciki, to wallahi babu ruwana sai inyi ta kaina in fita daga zuri’ar nan in shiga duniya kamar yanda Mera tayi, babu zunubin shegiyar da zai shafeni ban ji ba ban gani ba, ai tunda taje ta yo cikin dole sai ta haifesa a ba Hajja ko kuma a baki ku yi raino don nasan Mariya bazata amsa ba, ni ma kuma ba ruwana wallahi, da ana canza ma tuwo suna wallahi a yau din nan da na canza pamily bakina alekum na koma wani pamilyn, yanzu zancen da nake maki wllh kunyan Mamuda nake ji tun dazu na kasa hada ido da shi” Ammi dai kuka take ta kasa cewa komai ta nemi dakali ta zauna, Maheer ya fita daga tsakar gidan kawai, a kofar gida ya tadda Abba tsaye alamar dai lamarin nan ya girgiza sa ba kadan ba, shi dai Usman na tsaye jikin gate din gidan har sannan bai ce komai ba, shi fa bai yi mamaki ba ko kadan yasan akwai ranan da za a zo wanna gaɓar in har Hajja ta ci gaba da biye Badiyyah to gashi nan kuwa an zo, Abba na kallon Maheer bayan ya fito yace “I won’t decide for you Maheer, duk hukuncin da kaga ya kwanta maka a zuciya game da matarka zaka iya yankewa but… Ka tabbatar baza kayi hakan ba sai kana da kwakkwaran hujjoji da zaka gabatar ma danginta don Badiyyah ba abun yarda bace, a yau na gama sarewa da lamarinta sannan na zame hannu a duk wani abu da ya shafe ta babu ruwana, sannan zan gaya ma mahaifiyarku daga yau bana son Badiyyah ta sake takowa cikin gidana” Abba na kai wa nan ya shiga motarsa ya wuce. Mayraah na zaune kan darduma bayan ta idar da sallan asuba tana azkar dinta idonta a lumshe ta jingina da bango, wayarta ne ya fara ring ta bude ido tana kallon wayar cike da mamakin wanda ke kiranta by this time, Dr Khalil ta gani jikin screen din, ta sake duba agogo taga karfe shidda, picking call din tayi ta kai kunne hade da sallama, ya amsa yace “Good morning, how was ur night?” Tace “Alhamdulillah, ina kwana” yace “Lafiya lau, i just want to let u know ba sai kin shigo hospital yau ba MD na da meeting, but just make sure karfe tara na yi ki tafi gidan Ummi mu hadu a can” Mayraah ta ɗan yi shiru, yace “Are u there?” A hankali tace “Eh ina ji” Yace “Good! Zan kira in ji ko kin tafi anjima nima sai rana zan shiga asibitin” Tace “Toh” Katse wayar yayi ya juya yaga Zainab tsaye kansa tana masa wani kallo, bai ma san ta fito parlorn ba, a fusace tace “To kar ta kuskura ta sake kai kafarta gidan mahaifiyata don wallahi zan mata rashin mutuncin da bazata taba mancewa a rayuwarta ba, ka nemi wani wajen da zaka kai ta amma in har tayi mistake din zuwa gidanmu yau din nan to zata ga ikon Allah, halan ita arniya ce da bata da iyaye har zata shigo garin Abuja namiji ya dinga accommodating dinta, kuma ko bata da iyaye ai bazata rasa yan uwa ba ko yawon bariki ta shigo yi a Abujan ne dama” Dr Khalil dai kallonta kawai yake ya ma rasa me zai ce mata, tace “Naga rainin hankalin ya kai rainin hankali yanzu, wato har kiranta kake da asuba ka gaya mata kar ta ma je asibiti saboda baza ka je ba, duk kwanan nan dama ina ta lura da take taken ka, ga wani gidan Ummi da ka tsiri zuwa kullum tunda ka kai ta can, an mayar da ni wata shashasha to my patient is finished, kuma ka sani babu yarda tsakanina da kai yanzu” Ya mike tsaye yace “Listen Zainab….” Ko sauraronsa bata tsaya tayi ba ta wuce daki kamar zata tashi sama, ya sauke ajiyar zuciya bai ma san yanda zai mata bayani ta fahimci babu komai tsakaninsa da Mayraah ba sae Kasancewarta er uwar sa musulma da baxai so ganin ta fada halaka ba, gani yayi ta fito daga daki da akwati kamar dama ta hada akwatin ta ajiye gefe abinda take jira kenan, da mamaki yace “Ina zaki Zainab?” Ko tsayawa bata yi ba ta bude kofa ta fice daga parlon, ya kalli dakin da twins dinsu ke ciki suna bacci, komawa yayi ya zauna don yasan ko ya bi ta tunda har taki tsayawa a nan ta sauraresa to a wajen ma bazata sauraresa ba sai ma dai kawai su tona ma kansu asiri, he definitely knows ba gidan Ummi zata ba gidan Aunty Rabi’ah zata dama ita ke zugata always. Tara da yan mintuna Mayraah ta fito daga gida bayan Dr Khalil ya sake kiranta yace kawai ta taho asibiti ba sai taje gidan Ummi ba kuma, wajen karfe sha daya ta shigo asibitin ta gaisa da nurses din da ta gani reception ta tafi sama zuwa office dinsa, hijab ne jikinta bata saka uniform ba, zaune ta samesa office din da twins dinsa sun cika sa da surutu shi kuma yana ta aikin gabansa, tun da ta hadu da su a supermarket ranan bata sake ganinsu ba sai yau don bata taɓa ganinsu gidan Ummi ba, ko kilan an kai su bata nan bata sani ba, ta karasa tana murmushi tana kallon kyawawan yaran tace “Su ma sun zo aiki yau ne Dr?” Shi dai kawai yayi murmushi yana ci gaba da abinda yake yace “Ya hanya?” Tace “Alhamdulillah” tace “Ya sunansu?” Yace “Fatima and Khadija, ana kiransu Ashnaah and Ashfah” Tace “They are so cute” yace “Dama zan fita, ke nake jira so u can stay with them here” Mayraah tace “Ohk, Maminsu fa?” Yace “Bata jin dadi ne” Mayraah tace “Toh Allah ya sauwake” Yace “Ameen” Yana kallon girls din yace “Za ku zauna tare da Aunty zan je in dawo yanzu kun ji? Ga cartoon zan kunna maku sai ku yi kallo, do not disturb Aunty” Ashnaah da Ashfah suka kalli Mayraah a tare, dukawa tayi tana masu murmushi ta kamo hannunsu tace “Hello cuties, yanzu Daddy zai dawo, i will keep u company” Dr Khalil ya dau makullin motarsa bayan ya sa masu cartoon a tv dake office din ya kalli Mayraah yace “Ga cornflakes dinsu da abinci a jaka if they need” Mayraah tace “Ohk” fita yayi daga office din zai tafi gidan Aunty Rabi’ah don ya kira Zainab ya fi a kirga bata daga kiran, Da ya kira Ummi kuma normally suka gaisa nan ya gane ba can taje ba kamar yanda ya zarga kawai sae bai ce ma Ummi komai ba, Mayraah bata san yaran are sharp haka ba, don cikata suka yi da surutu ta rasa wanda ma zata amsa cikinsu, bayan tafiyarsa da kusan minti talatin Ashnaah tace “Aunty i want cornflakes” Mayraah tace “Ohk” Ashfah tace “Me too” Murmushi Mayraah tayi ta tafi inda ya nuna mata jakar ta durkusa tana dubo cornflakes din a ciki, bude office din aka yi ta juya da sauri, sosai gabanta ya fadi ganinsa amma lokaci daya ta dauke kai ta ci gaba da abinda take, tana ji ya shigo office din yaran suka je da gudu suka rungumesa ya duka ya ba ko wannensu peck yana kallonsu yana murmushi yace “Where is papa?” Ashnaah tace “He is gone” Yace “And he left u 2 all alone?” Ashfah ta nuna masa Mayraah da ta mike tsaye, ya juya suna hada ido ya wani sha kunu kamar ba shi ke murmushi ba ya mike tsaye ya jefa files din hannunsa kan table din Dr Khalil, tayi gathering courage zata gaishesa taga har ya fice daga office din daga ita har yaran suka bi sa da kallo, tabe baki tayi ta zagayo ta mika ma yaran bowl din cornflakes da ta hada masu. Sai kusan azahar Dr Khalil ya dawo, duk yaran sun yi bacci ta kwantar da su kan kujera, yana shigowa ya ajiye car key dinsa ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta yayi kasa da murya yace “Me yasa baki gaida MD ba da ya shigo office din nan dazu, Why pls Mayraah?” Hade rai tayi tace “Ni gaskiya Dr bazan iya aiki a asibitin nan as far as wannan mutumin yana nan, ya tsaneni, how will i greet someone that just disappeared daga gani na, he is just too rude for my liking, sannan ya fiye nagging” Dr Khalil yace “Let me tell u something, in fa kina karkashin mutum dole za kiyi hakuri a rayuwar nan, mu ma nan duk hakurin mu ke, MD is nyc but he have anger issues sannan baya son wasa baya son raini, he is a man of principle, mun yi degree tare da shi ne shi yasa har muka ɗan saba yake daga min kafa a abubuwa da yawa” Da mugun mamaki tace “To asibitin sa ne nan din with his principality?” Murmushi Dr Khalil yayi yace “Ba nashi bane, amma he is the second in command, he is a braniac Mayraah yasan aiki sosai, i think his dad is also a Dr in the US yanzu haka, and he is an only son, dole sai kinyi hakuri da shi, ni ina maki sha’awar son ace kin zama staff a nan saboda zaki ga advantage din hakan nan gaba” Daukar jakarta tayi tace “Tun da ka dawo ni zan tafi” Yace “No, i spoke to him now, zai yi interviewing dinki, he is less busy a office yanzu” Sosai gabanta ya fadi tace “But i am not ready Dr” yace “Dole ayi inputing data dinki yau Mayraah, don gobe me asibitin nan will be around saboda next workshop da za mu je, kin ga idan bai baki employment din ba u are not a staff, sannan babu vacancy, and they will be none anytime soon” Mayraah da taji hankalinta ya tashi tace “To amma wani irin interview zai min, i don’t have knowledge of how it is…” Dr Khalil ya katse ta yace “Just compose ur self, u are not dull Mayraah, i know u can do it” Bude drawer yayi ya ciro farin takarda ya mika mata yace “Apology letter, in kinje kin gaishesa sai ki basa hakuri da baki respectfully sannan ki mika masa wannan” Sake baki Mayraah tayi tana kallon takardan, can tace “Apology letter for what? Are we in secondary school?” Dr Khalil ya daure fuska yana kallonta, da tasan stress din da yayi going through yau duk a kanta da bazata ci gaba da stressing dinsa ba ita ma, first yaje shawo kan matarsa duk a kanta, secondly ko gamawa da matar tasa bai yi ba sai ga kiran MD babu abinda ya mance bai gaya masa a waya ba, yana shigowa asibitin yanzu yaje ya samu MD after almost 30 minutes of persuasion ya shawo kansa har ya yarda yayi mata interview din yau and she is here trying to complicate issues the more, Mayraah ta amshi takardan, on a serious note Dr Khalil yace “Mayraah ko zaginki yayi kice kin gode, kuma kar ki kuskura ki fito office din duk ma me zai ce maki” Ta ɗan yi murmushi kawai ta juya ta fita, ya zauna ya sauke ajiyar zuciya a yanda ya lura ma ta fi MD din girman kai amma bata sani ba, Mayraah na tafiya sama ta tsaya kofar office din MD din tana kallon sunan dake manne jikin kofar daga sama.
Mayraah tayi knocking din office din a hankali ta koma gefe ta tsaya, jin ba a ama ba bayan some seconds ta sake knocking, Sai da tayi knocking sau uku sannan taji ya bada izinin shigowa, ta bude kofar a hankali suna hada ido tun kan ta saka kafarta cikin office din yayi saurin cewa “I am occupied Madam, leave and come back tomorrow 8am prompt” yana fadin haka ya ci gaba da sipping juice dake hannunsa yana operating laptop, kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa, a karo na farko tun barin ta gida Musharrat ya fado mata a rai, don last day da ta je kai masa project work dinta a office dinsa da yanda yace ta tafi ta dawo 5:30pm prompt ne ya shiga rotating a kanta, ganin bata bar bakin kofar ba ya daga kai ya sake kallonta ya hade rai yace “Are you daft?” Wani tsinannen kallo ta jefa masa, wanda hakan yasa ya ajiye juice din hannunsa ba tare da yasan yayi hakan ba cause he was taken aback by her reaction, tuni ta kulle kofar office din ta bar wajen fuskarta daure, har ta sauka second floor ta kasa kauda tunanin Musharraf da ya mamaye ranta wanda hakan yasa kuzarinta ya ragu, office din Dr Khalil tayi knocking ta shiga bayan yayi mata izini, da mamaki yake kallonta ya mike tsaye yace “What happened again?” Ta kirkiri murmushi tace “No, na samesa yana cin abinci ne, shine yace in bari gobe karfe takwas na safe idan
Allah ya kai mu” Dr Khalil yace “Are you sure Mayraah?” Ta gyada masa kai tace “Da gaske fa, yace gobe da safe in sha Allah” Dr Khall ya Koma ya zauna yace “Ohk” Daukar handbag dinta tayi tana kallonsa tace “Na gaji, ina son in tafi” Yace “Toh ki gaida su Ummi, inna dai na gidan Baffan su Mimi, cousin din Zainab zata yi aure next week” Tayi murmushi tace
“Allah sarki, pls idan twins sun tashi kace masu sai mun sake haduwa i will miss them” Yace “To zan gaya masu” juyawa tayi ta fita daga office din ta sauka downstairs, sallama tayi da Nurse Hafsat sannan ta fita haraban asibitin, zaunawa tayi karkashin wani bishiya ta ciro wayarta a jaka, a hankali ta fara dialing number Musharraf da ake samunsa not his private line dake kulle, tafi minti uku tana kallon numbers din ta runtse ido kawai ta goge ta maida wayar cikin jakarta ta mike walking slowly ta fita daga asibitin, tana taran adaidaita sahu ta gaya masa inda zai kai ta sannan ta shiga, after many minutes ride yayi parking inda tace ya tsaya sannan tace “Don Allah ka jira ni zan amshi sako ne sai ka kai ni wani wajen daban” Yace “Toh” Karasawa tayi ta shiga shagon Aminu, gaisawa suka yi da fara’a yace “Ya makarantar Hajiya” Tace “Alhamdulillah ya kasuwa?” Yace “Lafiya lau wallahi, kin ga na kwana biyu ma ban shiga Sulejan ba ni” Tace “Allah sarki, don Allah SIM card nake son zan kara siya” Yace “Toh wani network kenan?” Tace “Ko wanne, sai ka hada min da katin dubu daya” Dauko mata yayi ta ciro dubu biyar a jakanta ta basa tace
“Ka saka katin waya da sauran canjin” Godiya ya mata sosai bayan ya amsa, tayi murmushi ta yi masa sallama ta koma cikin adaidaita sahun dake jiranta.
Mayraah na sauka kofar gidan Ummi bayan ta ba mai adaidaita sahun kudinsa ta shiga gidan, Ahmad na zaune compound making a phone call, kawai ta dan masa murmushi not wanting to distract him ya bi ta da ido har ta shiga gidan, karime kadai ce a gidan bayan sun gaisa karime tace “Ai ko awa daya yan gidan basu yi da fita ba in gaya maki, kinsan aminiyar Hajiya ke aurar da er ta, to can Hajiya ta tafi da Mimi, gobe asabar ne daurin aure ranan lahadi kuma ayi taron biki, ina jin ranan lahadin za su dawo, Hassan da Hussaini kuma sun je gidan baffans tare da Inna tun jiya, Baffan zai aurar da er sa satin nan da za mu shiga” Mayraah dake zaune parlon tana danna wayarta tace “Allah sarki” Karime tace “Ai gobe baki da aiki ko?” Mayraah ta daga kai ta kalleta ta dan yi murmushi, Karime tace “Sai mu je gidan bikin kawai tare, Hajiya ta ce in je gobe, ina jin bata san za ki dawo ba tunda mun san can Suleja kike weekend dinki” Mayraah tace “Zan je aiki goben in sha Allah” ta fada haka ne ba don tana da intention din zuwa asibitin gobe ba sai don kawai bata son bin karime gidan bikin, Karime tace “Allah sarki, to bari in zubo maki abinci” Daga haka ta mike ta shiga kitchen Mayraah ta bi ta da kallo, Karime zata yi shekara kusan arba’in da biyu, kuma ta fi shekara bakwai tare da Ummi sai dai taje ganin yaranta da iyayenta a kauyensu ta dawo don ta zama kamar wata er uwar Ummi, Karime na kawo mata abincin ta ajiye Mayraah tace “Nagode sosai” Karime tace “Kin ga da daddare ba sai mun yi girki ba, tun da akwai burodi kawai soya kwai za mu yi mu sha shayi don shi yallabai dama shayl yake sha da daddare” Mayraah dai ta dan yì murmushi ta dau plate din abincin ta fara ci, sama sama take biye karime da ta cikata da hira a parlon don duk ta kagu ta wuce daki ta saka sabon sim card da ta siyo, kiran la’asar ya sa Mayraah ta mike ta tafi kai plate din kitchen ta wanke sannan ta dawo ta tarar har Karime ta shiga daki ita ma zata yi sallah, Mayraah ta dau jakanta ta wuce nata dakin da take sauka a gidan, alwala tayi, bayan ta idar da sallah ta dau sabon sim din ta saka a wayarta, ganin ya hau ta loda katin, dialing din number Musharraf tayi da sabon Sim card din, tana ji ya fara ring sai da gabanta ya fadi, ta daura goshinta saman knees dinta har sannan zuciyarta na bugawa tana jiran ya daga, sai da ya kusa katsewa taji ya daga, shiru tayi shi ma yayi shiru bai ce komai ba, after few seconds taji ya katse wayar, murmushi tayi don tasan dama bazai ce komai ba in dai bai san number ba haka yake, sake dialing number tayi duk da a ranta tasan ba lallai ya sake dagawa ba ai kam har ya gama ringing bai daga ba, kawai ta kashe sim card din cikin wayar ta ajiye wayar ta kwanta. Mama Ladi ce zaune gefen Hajja dake jingine da bango tana zaune kan shimfidar da aka mata a parlonta wajen karfe biyar na yamma, Mama Ladi na washe baki tace “Alhamdulillah jiki ai ya fara kyau, gashi har kin kusa shanye shayin, tun jiya fargabana ta ina zan fara jinyarki idan shanyewar barin jiki ya sameki, wallahi hankalina yayi matukar tashi bazan boye ma kowa ba” Ammi dai na zaune parlon tana kallonsu, Aunty Mariya kuma na kitchen tana dama ma Hajja kunu, Mama Ladi ta kalli Ammi tace “Ke fa nace maki ki tashi ki tafi gida kar Mamuda ya ga rashin hankalinmu ya sake tabbatar da mu kananun mutane ne, tun shekaranjiya fa kike nan ko mutuwa aka yi ya ci ace kin koma dakinki barin ma ga Hajja har ta fara tashi zaune ga kuma shayi tana sha, nima zuwa anjima in sha Allahu zan taho sai Mariya ta zauna tayi jinyar Hajjan da me laulayin can, don gaskiya bazan iya jure karin aman da Badiyyah take kirba mana ba, in tayi aman karnin har nan malam, to a kan me, da ba dan sunna ba ta dinga cutar mu da karni, bazan iya ba wallahi” A karo na farko Hajja ta bude baki a hankali tana girgiza kai tace “A fitar min da ita daga gidana dama jira nake in gama shan shayin inyi magana, a tafi da ita duk inda za aje da ita, in ko ba haka ba in bi Mariya mu tafi kaduna ta sauke ni gidan yahanasu” Tana magana ne hawaye na sauka idonta, Mama Ladi ta saki baki tana kallon Hajja da mamaki, can tace “A fita da ita a kai ta ina Hajja? Ko dai baki gane wa nake nufi ba, Badiyyah fa nake magana, Badiyya guda fa taki” Hajja na gyada kai wani bakin ciki na kara tokare mata makogwaro tace
“Ita Ladi, bazata kwanar min a gida yau ba ta tafi duk inda za ta, ni ma kaduna zan tafi gun yahanasu” Ammi tayi kasa da murya tace “To ina za ta Hajja? Da dai kin yi….” Dakatar da ita Hajja tayi cikin rawan murya tace “Wallahi tallahi bazan kwana da Badiyyah gidan nan ba yau kun ji har na rantse, dama ina ta addu’ar in samu karfin yin magana tun jiya Allah bai bani iko ba sai yanzu, to Allah ya isa tsakanina da ita, Allah ya isa, Allah ya isa wannan abun gorin da ta ja min har karshen rayuwata, duk soyayyar da na nuna mata saboda tausayin maraicinta duk jan ta jiki da nayi don kawar mata da maraici a rayuwarta sakayyar da Badiyyah zata min kenan, da haka zata saka min? ta cuce ni, ta ja min abun kunya, ta ja min abun magana, ta ja min abin gorin da har in koma ga mahaliccina….” Kasa ci gaba tayi saboda tarin da ta fara kamar zata shide tana gwalo ido, Mama Ladi tayi saurin mikewa tana kallon Ammi tace “Kin ga tun da tace a fitar mata da ita daga gidan nan bazata kwanar mata ba to gaskiya ki shiga ki temaka mata ta hada kayanta a akwati a dora ta motar Bichi ta tafi wajen dangin ubanta, haka kawai bakin cikinta bazai kashe min yayata ba in shiga uku, maza a fita da ita ba ruwana, ko kuma ni in je in hado mata tsummokaran nata da kaina” Hajja na kuka tana tari tace “Ku fita da ita ko ni in tafi, ku fitar min da ita nace” Mama Ladi ta nufi dakin Badiyyah da gudu tana cewa “Daga wannan tarin fa wani ake zare ran, wallahi ba ruwana
Badiyyah ta zo ta tafi kar in rasa yayata” kwance
Mama Ladi ta tarar da Badiyyah shame shame a kasa kamar mara galihu, o bin ta kanta bata yi ba tana toshe hanci ta bude inda kayanta suke ta dinga kwaso su tana zubawa cikin akwatin da ta bude, Badiyyah sai bin ta take da ido tana sauke numfashi a hankali, tun shekaranjiya babu me bi ta kanta a gidan sai Ammi dake ajiye mata kunu a bakin kofar dakinta tayi tafiyarta, ji take kamar mutuwa kawai zata yi, komai ya dena mata dadi a rayuwar, Mama Ladi na gama cusa kayan cikin akwati tana kallonta tace “Tashi ki fita a samar maki adaidaita sahu ki tafi can gun dangin ubanki su yi jinya, mu ba yan iska bane duk ta sunna aka same mu, don haka baza mu yi jinyan cikin shege ba Allah ya tambayemu” Badiyyah ta mike zaune da kyar tashin hankali karara a kan jemammen fuskarta tace “Mama Ladi wallahi basa so na, ko a baya ba jin dadin zaman can garin nake ba don Allah ki rufa min asiri Mama Ladi” Mama Ladi bata sake sauraronta ba ta fito parlor da akwatinta, Ammi na tsaye tana kallon Hajja dake kuka hade da tari ta dage a fitar mata da Badiyyah daga gidan, Mama Ladi tace “To ni dai bani da karfin dagota
Ammi ki je ki fito da ita ga akwatin nata na fito da shi, ko shatar adaidaita sahu ne sai a dauko mu biyasa ya kai ta har Bichi” Sai ga Badiyyah ta shigo parlon da rarrafe ta fashe da kuka tace “Don girman Allah Hajja ki ce ma Mama Ladi a bar ni nan bazan iya zaman Bichi ba basa sona ke ma kin sani” Wani rikicewa Hajja tayi ganin Badiyyah ta dinga tari da karfi tana nuna alamar a fitar mata da ita, Dole haka Ammi ta fita da Badiyyah compound don Hajja ta dena ganinta, Mama Ladi ta dauki akwatin Badiyyah ta bi su da shi, Badiyyah ta rike kafar Ammi tana kuka sosai tace “Don Allah Ammi kema kinsan bani da inda zan je, basa sona a Bichi, don Allah ku yi min rai Ammi” Ammi dai na tsaye ta kasa cewa komai, Mama Ladi na ajiye masu akwatin ta koma gun er uwarta Hajja tace “An fitar da ita yanzu za a daura ta a mota ya kai ta Bichin don Allah ki kwantar da hankalinki yaya” Hajja dake ta sauke numfashi da kyar Aunty Mariya na durkushe gabanta ta rike hannayenta biyu, cikin sarkewar murya tace “Mariya ki kai ni wajen yahanasu kawai” Aunty Mariya ta kwantar da murya tace “Hajja yamma yayi mu kama hanyar kaduna yanzu, ki yi hakuri gobe da sassafe sai mu tafi in Allah ya yarda” Mama Ladi ta zauna gefenta tace “Tafiyar yamma babu dadi yaya, gobe da asuba har ni sai mu je Kadunan in hankalinki zai kwanta da haka, idan ya so idan nayi kwana biyu sai in bar ki tare da yahanasun ni in dawo” Kai kawai Hajja ke gyada masu tana sauke numfashi, Ammi dai an bar ta tsaye da Badiyyah da akwatinta a tsakar gida ta rasa yanda zata yi, Aunty Mariya ta kira da wayarta dake hannunta, ba a dau lokaci ba Aunty Mariya ta fito tsakar gidan, ko kallon Badiyyah dake kwance kasan compound din tana rusa kuka bata yi ba ta karasa gun Ammi da ta koma gefe tana jiranta, Ammi na kallon Aunty Mariya cike da damuwa tace “Yanzu ya za mu yi Mariya?” Aunty Mariya tace “Ya za mu yi me Ammi?” Ammi tace “To ina za a kai yarinyar nan yanzu?” A takaice Aunty Mariya tace “Aa, ba dangin ubanta na Bichi ba, ko kin manta ne Ammi” nan da nan hawaye ya cika idon Ammi tace “Kar ki manta Mariya yau ace Rukayya na da rai….” Kasa ci gaba tayi saboda kukan da ya taho mata, Aunty Mariya dai tayl shiru nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta, cikin rawan murya Ammi tace “Hannunka baya rubewa ka yanke ka yar, ko mun ki ko mun so Badiyyah ta mu ce, er uwar mu ta jini ce ta haifeta gashi bata doron kasa yau ga halin da er ta ke ciki, kuma Allah ya gani mun yi bakin kokarinmu kan Badiyyah, i tried my best Mariya, my children tried their best also, ke za a ce ba a garin kike ba, Amma Allah yasan kokarin da nayi kan Badiyyah” kasa ci gaba Ammi tayi, Aunty Mariya ta goge hawayen idonta tace “Yanzu ya za mu yi yaya?” Ammi na hawaye tace “Wallahi ban sani ba, kin ga tace bata son ganinta ni kuma yanzu ba da bane a gidana, i don’t have that power anymore, ban san ko Mahmud zai amince Badiyyah ta koma can ba” Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace “Ni kuma kin san family house nake, bazan dau Badiyyah da ciki in fara kai ta gidana ba ya zame min abun gori gun facalolina da dangin mijina” Ammi na gyada kai tace “Haka ne, kawai yanzu dukarta zan yi mu tafi gida sai in ga yanda za mu yi da Mamuda” Aunty Mariya tayi kasa da murya tace “In har ya nuna bai amince ba ko jayayya kar kiyi da shi Ammi, ki nemi izini kawai ki kai ta Bichi gobe, nima goben za mu tafi da Hajja kadunan tunda tace baxata zauna nan ba, ga Mama Ladi tace za ta bi mu” Ammi tace “Toh shikenan” Aunty Mariya ce ta fita ta samo masu adaidaita sahu, aka saka akwatin Badiyyah a ciki, Ammi ta daure fuska tana kallon Badiyyah dake kwance a kasa tace
“Tashi ki fita” Da rarrafe Badiyyah ta karasa gate din ta lallaba ta shiga adaidaita sahun, Aunty Mariya tayi ma Ammi sallama tana tsaye har adaidaita sahun ya juya ya bar layin sannan ta koma cikin gida. Ammi na isa gida dab da magrib ta sauka ta ba me adaidaita sahun kudinsa sannan ta sauko da akwatin Badiyyah ba tare da ta bi ta kanta ba ta shiga cikin gidan, Badiyyah ta sauko da kyar tana biye da ita a baya tana maida numfashi, Ammi taga motar Abba a garage alamar yana nan, Haseenah ce ta fito daga Chalet sanye da Hijab bayan ta leko compound jin an bude gate taga Ammi ce, ta sauka kasa ta karasa gun Ammi tace “Ammi sannu da zuwa” Ko kallonta Ammi bata yi ba tace “Sannu” Zata amshi akwatin hannun Ammi, Ammi ta ki sake mata tace ta bar shi kawai, tun shekaranjiya Haseenah ke gidan bayan an sallameta daga asibiti kamar yanda Abba ya umarce Maheer ya kawo ta gidan don tana ma gidan Badiyyah tayi wannan tonan sililin a parlon Hajja, kamar ance
Haseenah ta juya taga Badiyyah ta shigo compound wujiga wujiga duk ta rame tayi baki, nan da nan Haseenah ta hade rai ta kauda kai, Badiyyan dake fama da kanta ko bin ta kan Haseenah bata yi ba ta shige cikin gidan da sauri don kwanciya kawai take son yi ga amai da ke taso mata, Haseenah ta dan yi jim, sai kuma ta bi bayansu zuwa main building din gidan ita ma, a parlor ta tadda Badiyyah ta kwanta, Ammi kuma ta haura sama, Lokaci daya ta ga Badiyyah ta mike da gudu ta shige bandakin dake parlor tana kakarin amai, bude baki Haseenah tayi da mamaki bayan ta bi ta da kallo, a hankali tace “Amai kuma??” Can dai ta juya da sauri ta fita daga parlon ta koma Chalet din da take. Ammi tayi shiru tana kallon Abba a sanyaye don maganganu kawai yake cikin fada inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, har ya kai aya, can ta sauke kanta kasa cike da karfin hali tace
“Shikenan Yallabai kayi hakuri… kayi hakuri, goben sai in kai ta Bichi idan Allah ya kai mu” A takaice Abba yace “Da dai ya fi don bazata zauna a gidana ba i stand my words” Daga haka ya mike ya shige
Bedroom dinsa Ammi ta bi sa da kallo wasu hawaye na sauka idonta, duk ya canza kamar ba shi ba, Abba da ko daga mata murya baya yi idan yana mata magana a baya, abu ko bai masa ba idan tace haka take so to haka nan zai yi don baya son bacin ranta kwata kwata amma yanzu duk babu wannan, duk hakan na neman zama tarihi daga yan watannin nan da suka shude, he is now a changed person, tunanin hakan ya kara breaking heart dinta sosai, ta mike ta fita daga parlonsa ta koma bangarenta ta ci kukanta ta gode Allah…..
Mayraah na kwance dakinta bayan isha Karime ta shigo da sallama tace “Hajiya ham ga can kwan na soya maki a kitchen sai ki yanki bredin da zai isheki ki debi ruwan shayi a flask ki bar ma yallabai sauran, ni zan shiga gidan makociyarmu in duba jikin er ta ta kone a kafa, to duk yau ban shiga ba” Mayraah ta gyada mata kai tace “In zan ci zan je in dauka” Karime tace “Toh sai na dawo” Mayraah ta bi ta da kallo sae kuma tace “Amma ba dadewa za ki yi ba ko?” Karime ta juyo tace “Toh akwai dae wani pim din hausa da ake yi duk ranan juma’a, wani lokacin in Ummi ta shiga ta kwanta da wuri na kan je gidan in kalla, kinsan duk an rufe tashoshin gidan nan saboda yan biyun nan maxa da yarinyar nan Mimi da basu son maida hankali su yi karatu sai kallo, to yallabai duk ya rufe tasoshin ba a kallon finafinai a aidan nan. ke baki ga tun da kika zo sae dai ki ga an kamo tashan labarai ba” Mayraah tace “Yanzu dai kallo za ki je yi kenan” Karime ta kyalkyale da dariya tace “Baxan boye maki ba shi zan je inyi gaskiya, karfe goma ake gama pim din, ana gamawa zan dawo in sha Allah” Mayraah tace “Toh… Shikenan, sai kin dawo” Karime tace “Toh kar dai ki bar kwan ya sandare” Daga haka ta fita daga dakin.
Mayraah ta sauko daga kan gadon da take kwance bayan tafiyar karime da kusan minti sha biyar, wayarta ta dauko ta bude second sim din da ta kashe tun dazu, ta zauna gefen gado tana ta kallon wayar as if contemplating to call him again or not to, after many minutes of thinking ta ajiye wayar a hankali ta mike ta shiga bandaki, wanka tayi ta fito, tana cikin dauko daya daga dogayen rigunan bacci da ta siya a Suleja cikin jakarta taji wayar ta na vibrate, ta dauko kayan baccin ta mike tana gyara daurin towel din jikinta ta karasa kusa da wayar tana duba me kiranta, sai da gabanta ya fadi ganin number Musharraf, ta zauna gefen gadon a hankali ta dau wayar tana kallo, har ya katse bata daga ba, ya sake kira nan ma bata daga ba har ya gama ringing, sake kira yayi this time around sai ta daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren ta ji yace “Pis who is this?” Ai bata san sanda ta zamo kasa ta zauna ba, she just realized she missed him so very much, ta kasa cewa komai zuciyar ta na bugawa, daga daya bangaren yace “! know u can hear me, ols say something…” Mayraah ta jinginar da kanta da gado a hankali tace “Good evening” Musharraf ya mike tsaye daga zaunen da yake yace “Mayraah” Shiru tayi bata ce komai ba, ya marairaice mata yace “Piss tell me kina ina Mayraah?” A hankali tace “Ina lafiya” Trying all best to be calm yace “I know, yes i know, amma piss ki gaya min inda kike trust me, tell me pis Mayraah, just trust me pis” Lkei daya ya birkice mata, Ta langwabar da kai tace
“You don’t worry about that” Yace “Nooe pis, Mayraah kin san halin da kika tafi kika bar ni ciki kuwa, not only me, ur brothers, ur parent, haba Mayraah, pls i am begging u ki gaya min inda kike, Baby don’t u trust me?” Mayraah ta lumshe ido ta bude tace “I am somewhere far away, kar ka damu tunda ka ga na kira ka i am fine, and i just wanted to say hi…” A hankali yace “Mayraah” bude kofar dakin taji anyi ta juya da sauri taga Ahmad, kallonsa ta dinga yi don duk tunaninta idan ya ga yanayin da take zai fita sai taga ba haka ba, instead he is even walking in, dauke kanta tayi zuciyarta na bugawa tace “I will call you back” Bata jira cewar Musharraf ba ta katse wayar wondering dalilin da zai sa ya shigo mata daki duk da yanayin da ya ganta, she just tied a towel, geten gadon ta ji alamar ya zauna, Ikci daya ta juya ta kallesa tace “Iam sorry, i want to dress up” Ya dan yi shiru yana kallonta, sai kuma ya buda mata hannu alamar what is there? Kasa motsawa tayi daga inda take zaune with shock amma taki nuna hakan a fuskarta, ko hijab dinta ta kasa yunkurin daukowa don dole sai ta tashi zata yi hakan, banda faduwa babu abinda gabanta yake gaba daya ta rasa wani tunanin zata yi a lokacin, silencing kiran da Musharraf yake ta yi mata tayi ta ajiye wayar a gefenta, kawai gani tayi ya dawo gabanta ya durkusa yana kallon idonta as if counting his words yace “I understand what u are going through Mayraah, Khalil briefed me earlier, it’s sad and i get kin fito ne ki samu relieve by chilling away ur worries right? I love ur courage and braveness” Mayraah ta fara matsawa jikin gadon a hankali tana kallonsa babu ko kiftawa, a hankali tace
“You are drunk” Buda ido yayi sosai yana gyada mata kai yace “Not much though, but how did u know? Ko kema kina sha ne?” Tayi murmushin da lyakarsa lips tace “Yeah” ya kara buda ido yace “Really?” Ta gyada masa kai tace “I won’t mind some” Ya karyar da kai vace “Unfortunately I can’t bring that home because of my Ummi, i drink only outside” Sosai gaban Mayraah ya fadi a tunaninta zai ce bari yaje ya dauko mata ne tasan na kwatanci, nan da nan hankalinta ya tashi, yayi kasa da murya holding on to her hand yace
“Would u mind us spending the night somewhere….” Ta dake tace “Somewhere like??” Yace “Hotel, club, guess inn… And what have you” Tayi saurin gyada masa kai tace “Ok, let me get dressed” Yayi kasa da murya yace “Thank you…” Bata yarda ta mike ba a gabansa, gaba daya idonsa na kirjinta, da sauri tace
“Can u excuse me in shirya?” Yace “C’mon meye in, kin shirya while am here” Daga ta zai yi ta wani fizge hannunta tace “Stop it” Ya mike yace “Ohk then” Jikin window ya koma ya tsaya ya rungume hannunsa yace “Ki shirya” Babu yanda ta iya haka ta mike tsaye, wani takaici ya tokare mata wuya, she was trying her best kar ta bari hawaye ya taran mata a ido, daukan kayanta tayi ta shiga bandaki ya bi ta da ido, sai a sannan hawaye ya fara sauka idonta ta jingina da bangon bandakin bayan few minutes ta saka kayan ta fito ta dau Hijab dinta ta saka, ta dau handbag dinta with her charger and phone, duk yana ta bin ta da kallo, without looking at him tace “I am done” har suka fita compound din gidan a motarsa Mayraah bata yarda sun hada ido ba, kamo hannunta yayi vana kallonta yace “or should we go for the hotel we met first?” Ta gyada masa kai kawai, yace “Ork, but do u have an international passport?” Duk da tana da shi haka ta girgiza masa kai tace “Nop” Da mamaki yace
“Why? Big gal kamar ki ace baki da International passport” Ta yi feigning murmushi bata dal ce komai ba, yayi kasa da murya yace *I will get you one if u don’t mind, sai a maki visa ko na Uk ne don zaman kasar nan baya wani cire ma mutum damuwa a rai ga sa ido irin na malam bahaushe, u need to be far far away, i think next week zan koma i will try and see if we can make it together” Mayraah tace “Thank you” All through the ride shi yake ta surutunsa, ita kam tavi nisa tunanin da take suna isa hotel din kafin ya shiga ciki ta kallesa tace “Zan dan amso abu a mart din can na gaba, wait for me” Yace “Me za ki amso?” Tace
“Chewing gum” Yace “Oh ok, bari in amso maki” Ta masa murmushi tace “Ai baka san irin wanda nake so ba” Yace “True” Bude motar tayi ta sauka ta kulle masa tana kallonsa tace “Not every girl that left home is a bitch, not every girl that left home is useless, don kaga na baro gida ba yana nufin ni er iska bace, kuma hakan ba yana nufin bani da tarbiya bane, i chose leaving home because of my mental health..” Tana kai wa nan tayi tafiyarta, sai a sannan wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, ko waiwayawa bata vi ba har tayi nisa daga hotel din, tana isowa main road ta tare adaidaita sahu ta shiga ta gaya masa inda zai kai ta, har suka iso bata san sun iso ba don tayi nisa tunanin da take ga hawayen da ke ta saukan mata, sai da mai tricycle din yayi alerting dinta sannan ta sauka tana goge idonta ta basa kudinsa, tana shiga gate ta nemi kujera ta zauna, sai da tayi kukanta me isarta sannan ta ciro wayarta, missed calls din Musharraf ta gani ya fi goma, tayi dialing number Dr Khalil yana fara ringing ya daga, gaishesa tayi a hankali, ya amsa yace
“Ya kike, ya gida?” Tace “Alhmdih, are you at work?” Yace “Yeah ina night duty, Why do u ask?” Tace “Aa just want to be sure” Yace “Are you okay?” Wasu hawaye ne suka cika identa kawai ta katse wayar, mikewa tayi taji ya sake kiranta bata daga ba ta shiga cikin asibitin, sau uku yana kiranta bata daga ba, tana shiga reception ta gaida nurses da ta gani ta haura sama zuwa office dinsa, wata nurse fa’iza ta mike da sauri ta tafi inda jakarta yake ta ciro wayarta ta fara kiran Zainab. Dr khalil na zaune still calling her line ta shiga office din ko knocking bata yi ba, yana ganinta ya mike yana kallonta, bata yarda sun hada ido ba ta zauna kan kujera, ya zagayo yace “Mayraah are you okay?” Bata san sanda ta fashe da kuka ba, ya iso gabanta da mamaki yace “Lafiya? Talk to me, me yake faruwa?” Duk da tambayoyin nan da yake jefo mata hankalinsa kawai ya tafi kan kila Zainab taje ta sameta ne a gida don not long ago ya kira Ummi tace masa tana gidan biki, ganin taki basa amsa sai kuka take ya duka gabanta yace “Piss talk to me Mayraah, an maki wani abun ne?” Bude office din aka yi duk suka juya, MD ne ya shigo, Dr Khalil ya mike yana kallonsa, Mayraah ta kauda kanta da sauri, tunda ya kallesu sau daya bai sake kallonsu ba ya ajive files din hannunsa yana kallon Khalil yace “See me off” Dr Khalil yace “Ohk” fita yayi office din Dr Khalil na kallon Mayraah yace “I will be back right away” Daga haka ya fita daga office din ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake sauka idonta. Dr Khalil na kallon MD bayan sun fita reception yace “Drivern ya iso ne?” MD yace “Ban kirasa ba, just drop me” Dr Khalil yace “Ni fa da na ga kayi dare na zata u will pass the night here MD™️ MD na mika masa makullin hannunsa yace
“Ka taba ganin na kwana asibiti in ba dole ba?” Dr Khalil bai amshi makullin nasa ba yace “Sae dai mu je a motata ka bar naka a nan, tunda zan dawo asibitin” MD vace “Mu tafi a nawa sai ka dawo da shi, bazan iya jira sai kaje sama ka dauko key ba” Yana fadin haka ya bude front seat ya shiga, Dr Khalil ya zaga ya shiga driver seat, sai da suka bar asibitin Dr Khalil yayi dialing number Mayraah, tana dagawa yace “Nan da 30 minutes zan dawo in sha Allah, ki jirani” yana gama fadin haka ya katse wayar, MD dake kallonsa yace “Wato ita wannan mannerless teenager din budurwarka ce shi yasa ka dage sai ta samu aiki a asibitin nan ku jone salon ka daina maida hankali a aikin ka ko, sannan ita wannan er mitsitsiyar yarinyar har yaushe aka haifeta tayi degree? thank God ba aikin za a bata ba, kuma baza a taba bata ba as far as i remain the MD in here, sannan on a serious note bana son sake ganinta a asibitin nan, she is neither a staff nor a patient don haka ban ga dalilin da zata
dinga shigowa ba, i will talk to the securities not to let her in from henceforth” Dr Khalil dai bai tankasa ba driving dinsa kawai yake. Bayan tafiyar Khalil da kusan minti arba in Mayraah dai na zaune office dinsa ta jinginar da kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da take taji an bude kofar office din ta juya duk tunaninta shi ne ya dawo, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab ta shigo office din fuska a murtuke kamar an jefota,
Mayraah ta sauke idonta daga kallonta, lokaci daya jikinta yayi sanyi, Zainab ta karaso har gabanta tana kallonta da kyau tace “Ke don kaza kazanki duk fadin garin Abuja baki ga maza yan iska mara mafada karuwai irinki ba sai mijina za ki makale ma? Baki ga matsiyata masu zaman kansu kaman ki ba sai mijina?
To wai ma ke uban wa yace maki Khalil dan Iska ne? ko kuma ance maki shi ma daga sama ya fado bashi da iyaye kamar ki? Don in har kina da iyaye ban jin zaki dinga irin wannan kazamin rayuwar da kike kamar sakakkiyar akuya a garin Abuja, baki can baki nan, baki gidan mutane, baki asibiti, baki hotel, baki
Suleja da kika kama gida kike zaman kanki ko ance maki duk ban bincika ba? to bari ki ji wallahi wallahi ina ja maki kunne da babban baki ki fita harkar mijina, iam warning u ki fita harkar khalil, stay away from my husband kada inyi maki abinda baki taba zato ba a rayuwarki don wallahi ba mutunci ne da ni ba, ba nil da kirki wallahi, sannan in ba zina iyayenki suka yi suka haifeki ba to ki bar min gidan uwata ki kama gabanki ki je can ki ci gaba da rayuwar zaman kai da kike a suleja, mu gidanmu gidan tarbiya ne, sai ki want dinga yawo da hijabi sumi sumi kamar ta kirki nan kuma lalata mazan mutane kike yi cikin Abuja, i am cutting you this first and last warning idan kuwa ba haka ba nace maki duk abinda na maki ke kika ja ma kanki, banza kawai karuwa me zaman kanta” Zainab na kai wa nan ta fice daga office din kamar zata tashi sama, Mayraah ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune. Sai bayan awa daya Dr Khalil ya dawo asibitin, Mayraah na zaune yanda Zainab ta fita ta bar ta ya shigo office din, ya karaso yana kallanta bayan ya ajiye makullin motar MD kan table dinsa yace “Ki gaya min me ya faru Mayraah, why are you crying?” Shiru tayi har sai da ya dawo gefenta ya zauna leaving enough distance tsakaninsu yace “Pis say something, an maki wani abu ne kika shigo kina kuka daxu?” Mayraah ta kallesa sannan a hankali tace
“Dama idan mutum ya bar gidan su yaje wani waje sai a fara masa kallon yana iskanci?” Tana masa tambayar hawaye ya cika idonta, Dr Khalil yayi shiru yana kallonta, ta fashe da kuka ba tare da tasan tayi hakan ba, tace “Ko dai nayi kama da warce take iskanci ne?” Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace
“Gaya min me ya faru?” Tace “No! answer my questions first” Dr Khalil yace “Mayraah, in our society today da kuma al’adan mu na hausa fulani duk macen da ta bar gaban iyayenta for whatsoever reason dole zata yi facing five da haka a rayuwa, kin ga wasu za su mata kallon warce tafi karfin iyayenta, wasu su mata kalon er iska warce idonta ya bude amma sai suka tashi da wani aiki da asuba tare da sauran likitocin asibitin, zuwa karfe tara Mayraah ta gama shawaran abinda zata yi a zuciyarta, tun cikin dare take tufka da warwara a ranta ko baccin kirki bata yi ba sai bayan sallahn asuba ta samu bacci ya dauketa, yanzu kuwa tana tashi ta tafi bandakin office dinsa ta wanke bakinta da mouth wash ta wanke fuskarta sannan ta fito ta dau Handbag dinta ta nufi kofa ta fita har sannan kuma su Dr Khalil basu fito theatre ba, tana sauka stairs tayi ido hudu da MD da shigowarsa reception din kenan da wasu turawa biyu sai bakin fata daya duk sanye da suit, a tare da su wata dattijuwa ce warce bata da maraba da halfcast coporately dressed in black suit with skirt da iyakarsa gwiwa, dai dai nan su Dr Khalil ma suka fito theatre da likitoci kusan hudu, gaba daya nurses gaida matar suke da ladabi, har ma da Dr’s din tana amsa su cikin fara arta da turancinta me cike da phonic, MD gaba daya attention dinsa na kan Mayraah bayan ya wani hade rai kamar bai taba dariya ba da ya hangota,
wato a asibitin ma ta kwana kenan, Mayraah ta karasa saukowa downstairs ita ma ta gaida matar, Matar ta sakar mata murmushi tace “Helloo” Har tayi gaba ta sake juyowa tace “Are you a staff here young lady?” Mayraah ta dan kalli MD da ya kafeta da ido, a Ikci daya ta kalli Dr Khalil taga ya nodding mata kai alamar ta ce eh, da sauri ta gyada ma matar kai kamar kadangariya, matar ta kalli bakin mutumin dake cikin fararen fatan tace “Dr Yemi, you remember my Late moslem frnd Hajiya Amina?” Yace “Oh yes, Late Professor Amina, exactly i remembered Ma” Matar ta nuna Mayraah tace “Her replica, she just reminded me of her, may her soul rest in peace” Duk suka amsa da “Ameen” Matar tace “Ba don nasan yaranta ba kuma bata da karamar yarinya da nace ke yarinyar ta ce..” Mayraah dai sai murmushin karfin hali take tana kallon kyakkyawan dattijuwar don bata taba zaton tana jin Hausa ba sai gashi tayi hausa, amma Hajiya Amina da tace take replicating ya tsaya ma Mayraah cak a rai, to ko dai she is related to the Hajiya Amina tunda tace suna kama, MD na kallon Ceo din tasu da ladabi yace “Ma, Youve stood for so long”
Mayraah ta sauko daga kan gadon da take kwance bayan tafiyar karime da kusan minti sha biyar, wayarta ta dauko ta bude second sim din da ta kashe tun dazu, ta zauna gefen gado tana ta kallon wayar as if contemplating to call him again or not to, after many minutes of thinking ta ajiye wayar a hankali ta mike ta shiga bandaki, wanka tayi ta fito, tana cikin dauko daya daga dogayen rigunan bacci da ta siya a Suleja cikin jakarta taji wayar ta na vibrate, ta dauko kayan baccin ta mike tana gyara daurin towel din jikinta ta karasa kusa da wayar tana duba me kiranta, sai da gabanta ya fadi ganin number Musharraf, ta zauna gefen gadon a hankali ta dau wayar tana kallo, har ya katse bata daga ba, ya sake kira nan ma bata daga ba har ya gama ringing, sake kira yayi this time around sai ta daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren ta ji yace “Pls who is this?” Ai bata san sanda ta zamo kasa ta zauna ba, she just realized she missed him so very much, ta kasa cewa komai zuciyar ta na bugawa, daga daya bangaren yace “I know u can hear me, pls say something….” Mayraah ta jinginar da kanta da gado a hankali tace “Good evening” Musharraf ya mike tsaye daga zaunen da yake yace “Mayraah” Shiru tayi bata ce komai ba, ya marairaice mata yace “Plss tell me kina ina Mayraah?” A hankali tace “Ina lafiya” Trying all best to be calm yace “I know, yes i know, amma plss ki gaya min inda kike trust me, tell me pls Mayraah, just trust me pls” Lkci daya ya birkice mata, Ta langwabar da kai tace “You don’t worry about that” Yace “Nooo pls, Mayraah kin san halin da kika tafi kika bar ni ciki kuwa, not only me, ur brothers, ur parent, haba Mayraah, pls i am begging u ki gaya min inda kike, Baby don’t u trust me?” Mayraah ta lumshe ido ta bude tace “I am somewhere far away, kar ka damu tunda ka ga na kira ka i am fine, and i just wanted to say hi….” A hankali yace “Mayraah” bude kofar dakin taji anyi ta juya da sauri taga Ahmad, kallonsa ta dinga yi don duk tunaninta idan ya ga yanayin da take zai fita sai taga ba haka ba, instead he is even walking in, dauke kanta tayi zuciyarta na bugawa tace “I will call you back” Bata jira cewar Musharraf ba ta katse wayar wondering dalilin da zai sa ya shigo mata daki duk da yanayin da ya ganta, she just tied a towel, gefen gadon ta ji alamar ya zauna, lkci daya ta juya ta kallesa tace “I am sorry, i want to dress up” Ya ɗan yi shiru yana kallonta, sai kuma ya buda mata hannu alamar what is there? Kasa motsawa tayi daga inda take zaune with shock amma taki nuna hakan a fuskarta, ko hijab dinta ta kasa yunkurin daukowa don dole sai ta tashi zata yi hakan, banda faduwa babu abinda gabanta yake gaba daya ta rasa wani tunanin zata yi a lokacin, silencing kiran da Musharraf yake ta yi mata tayi ta ajiye wayar a gefenta, kawai gani tayi ya dawo gabanta ya durkusa yana kallon idonta as if counting his words yace “I understand what u are going through Mayraah, Khalil briefed me earlier, it’s sad and i get kin fito ne ki samu relieve by chilling away ur worries right? i love ur courage and braveness” Mayraah ta fara matsawa jikin gadon a hankali tana kallonsa babu ko kiftawa, a hankali tace “You are drunk” Buda ido yayi sosai yana gyada mata kai yace “Not much though, but how did u know? Ko kema kina sha ne?” Tayi murmushin da iyakarsa lips tace “Yeah” ya kara buda ido yace “Really?” Ta gyada masa kai tace “I won’t mind some” Ya karyar da kai yace “Unfortunately I can’t bring that home because of my Ummi, i drink only outside” Sosai gaban Mayraah ya fadi a tunaninta zai ce bari yaje ya dauko mata ne tasan na kwatanci, nan da nan hankalinta ya tashi, yayi kasa da murya holding on to her hand yace “Would u mind us spending the night somewhere….” Ta dake tace “Somewhere like??” Yace “Hotel, club, guess inn… And what have you” Tayi saurin gyada masa kai tace “Ohk, let me get dressed” Yayi kasa da murya yace “Thank you….” Bata yarda ta mike ba a gabansa, gaba daya idonsa na kirjinta, da sauri tace “Can u excuse me in shirya?” Yace “C’mon meye in kin shirya while am here” Daga ta zai yi ta wani fizge hannunta tace “Stop it” Ya mike yace “Ohk then” Jikin window ya koma ya tsaya ya rungume hannunsa yace “Ki shirya” Babu yanda ta iya haka ta mike tsaye, wani takaici ya tokare mata wuya, she was trying her best kar ta bari hawaye ya taran mata a ido, daukan kayanta tayi ta shiga bandaki ya bi ta da ido, sai a sannan hawaye ya fara sauka idonta ta jingina da bangon bandakin bayan few minutes ta saka kayan ta fito ta dau Hijab dinta ta saka, ta dau handbag dinta with her charger and phone, duk yana ta bin ta da kallo, without looking at him tace “I am done” har suka fita compound din gidan a motarsa Mayraah bata yarda sun hada ido ba, kamo hannunta yayi yana kallonta yace “or should we go for the hotel we met first?” Ta gyada masa kai kawai, yace “Ohk, but do u have an international passport?” Duk da tana da shi haka ta girgiza masa kai tace “Nop” Da mamaki yace “Why? Big gal kamar ki ace baki da International passport” Ta yi feigning murmushi bata dai ce komai ba, yayi kasa da murya yace “I will get you one if u don’t mind, sai a maki visa ko na Uk ne don zaman kasar nan baya wani cire ma mutum damuwa a rai ga sa ido irin na malam bahaushe, u need to be far far away, i think next week zan koma i will try and see if we can make it together” Mayraah tace “Thank you” All through the ride shi yake ta surutunsa, ita kam tayi nisa tunanin da take suna isa hotel din kafin ya shiga ciki ta kallesa tace “Zan ɗan amso abu a mart din can na gaba, wait for me” Yace “Me za ki amso?” Tace “Chewing gum” Yace “Oh ok, bari in amso maki” Ta masa murmushi tace “Ai baka san irin wanda nake so ba” Yace “True” Bude motar tayi ta sauka ta kulle masa tana kallonsa tace “Not every girl that left home is a bitch, not every girl that left home is useless, don kaga na baro gida ba yana nufin ni er iska bace, kuma hakan ba yana nufin bani da tarbiya bane, i chose leaving home because of my mental health…” Tana kai wa nan tayi tafiyarta, sai a sannan wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, ko waiwayawa bata yi ba har tayi nisa daga hotel din, tana isowa main road ta tare adaidaita sahu ta shiga ta gaya masa inda zai kai ta, har suka iso bata san sun iso ba don tayi nisa tunanin da take ga hawayen da ke ta saukan mata, sai da mai tricycle din yayi alerting dinta sannan ta sauka tana goge idonta ta basa kudinsa, tana shiga gate ta nemi kujera ta zauna, sai da tayi kukanta me isarta sannan ta ciro wayarta, missed calls din Musharraf ta gani ya fi goma, tayi dialing number Dr Khalil yana fara ringing ya daga, gaishesa tayi a hankali, ya amsa yace “Ya kike, ya gida?” Tace “Alhmdlh, are you at work?” Yace “Yeah ina night duty, Why do u ask?” Tace “Aa just want to be sure” Yace “Are you okay?” Wasu hawaye ne suka cika idonta kawai ta katse wayar, mikewa tayi taji ya sake kiranta bata daga ba ta shiga cikin asibitin, sau uku yana kiranta bata daga ba, tana shiga reception ta gaida nurses da ta gani ta haura sama zuwa office dinsa, wata nurse fa’iza ta mike da sauri ta tafi inda jakarta yake ta ciro wayarta ta fara kiran Zainab. Dr khalil na zaune still calling her line ta shiga office din ko knocking bata yi ba, yana ganinta ya mike yana kallonta, bata yarda sun hada ido ba ta zauna kan kujera, ya zagayo yace “Mayraah are you okay?” Bata san sanda ta fashe da kuka ba, ya iso gabanta da mamaki yace “Lafiya? Talk to me, me yake faruwa?” Duk da tambayoyin nan da yake jefo mata hankalinsa kawai ya tafi kan kila Zainab taje ta sameta ne a gida don not long ago ya kira Ummi tace masa tana gidan biki, ganin taki basa amsa sai kuka take ya duka gabanta yace “Plss talk to me Mayraah, an maki wani abun ne?” Bude office din aka yi duk suka juya, MD ne ya shigo, Dr Khalil ya mike yana kallonsa, Mayraah ta kauda kanta da sauri, tunda ya kallesu sau daya bai sake kallonsu ba ya ajiye files din hannunsa yana kallon Khalil yace “See me off” Dr Khalil yace “Ohk” fita yayi office din Dr Khalil na kallon Mayraah yace “I will be back right away” Daga haka ya fita daga office din ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake sauka idonta. Dr Khalil na kallon MD bayan sun fita reception yace “Drivern ya iso ne?” MD yace “Ban kirasa ba, just drop me” Dr Khalil yace “Ni fa da na ga kayi dare na zata u will pass the night here MD” MD na mika masa makullin hannunsa yace “Ka taba ganin na kwana asibiti in ba dole ba?” Dr Khalil bai amshi makullin nasa ba yace “Sae dai mu je a motata ka bar naka a nan, tunda zan dawo asibitin” MD yace “Mu tafi a nawa sai ka dawo da shi, bazan iya jira sai kaje sama ka dauko key ba” Yana fadin haka ya bude front seat ya shiga, Dr Khalil ya zaga ya shiga driver seat, sai da suka bar asibitin Dr Khalil yayi dialing number Mayraah, tana dagawa yace “Nan da 30 minutes zan dawo in sha Allah, ki jirani” yana gama fadin haka ya katse wayar, MD dake kallonsa yace “Wato ita wannan mannerless teenager din budurwarka ce shi yasa ka dage sai ta samu aiki a asibitin nan ku jone salon ka daina maida hankali a aikin ka ko, sannan ita wannan er mitsitsiyar yarinyar har yaushe aka haifeta tayi degree? thank God ba aikin za a bata ba, kuma baza a taɓa bata ba as far as i remain the MD in here, sannan on a serious note bana son sake ganinta a asibitin nan, she is neither a staff nor a patient don haka ban ga dalilin da zata dinga shigowa ba, i will talk to the securities not to let her in from henceforth” Dr Khalil dai bai tankasa ba driving dinsa kawai yake. Bayan tafiyar Khalil da kusan minti arba’in Mayraah dai na zaune office dinsa ta jinginar da kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da take taji an bude kofar office din ta juya duk tunaninta shi ne ya dawo, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab ta shigo office din fuska a murtuke kamar an jefota, Mayraah ta sauke idonta daga kallonta, lokaci daya jikinta yayi sanyi, Zainab ta karaso har gabanta tana kallonta da kyau tace “Ke don kaza kazanki duk fadin garin Abuja baki ga maza yan iska mara mafada karuwai irinki ba sai mijina za ki makale ma? Baki ga matsiyata masu zaman kansu kaman ki ba sai mijina? To wai ma ke uban wa yace maki Khalil ɗan iska ne? ko kuma ance maki shi ma daga sama ya fado bashi da iyaye kamar ki? Don in har kina da iyaye ban jin zaki dinga irin wannan kazamin rayuwar da kike kamar sakakkiyar akuya a garin Abuja, baki can baki nan, baki gidan mutane, baki asibiti, baki hotel, baki Suleja da kika kama gida kike zaman kanki ko ance maki duk ban bincika ba? to bari ki ji wallahi wallahi ina ja maki kunne da babban baƙi ki fita harkar mijina, i am warning u ki fita harkar khalil, stay away from my husband kada inyi maki abinda baki taɓa zato ba a rayuwarki don wallahi ba mutunci ne da ni ba, ba ni da kirki wallahi, sannan in ba zina iyayenki suka yi suka haifeki ba to ki bar min gidan uwata ki kama gabanki ki je can ki ci gaba da rayuwar zaman kai da kike a suleja, mu gidanmu gidan tarbiya ne, sai ki wani dinga yawo da hijabi sumi sumi kamar ta kirki nan kuma lalata mazan mutane kike yi cikin Abuja, i am cutting you this first and last warning idan kuwa ba haka ba nace maki duk abinda na maki ke kika ja ma kanki, banza kawai karuwa me zaman kanta” Zainab na kai wa nan ta fice daga office din kamar zata tashi sama, Mayraah ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune. Sai bayan awa daya Dr Khalil ya dawo asibitin, Mayraah na zaune yanda Zainab ta fita ta bar ta ya shigo office din, ya karaso yana kallonta bayan ya ajiye makullin motar MD kan table dinsa yace “Ki gaya min me ya faru Mayraah, why are you crying?” Shiru tayi har sai da ya dawo gefenta ya zauna leaving enough distance tsakaninsu yace “Pls say something, an maki wani abu ne kika shigo kina kuka daxu?” Mayraah ta kallesa sannan a hankali tace “Dama idan mutum ya bar gidan su yaje wani waje sai a fara masa kallon yana iskanci?” Tana masa tambayar hawaye ya cika idonta, Dr Khalil yayi shiru yana kallonta, ta fashe da kuka ba tare da tasan tayi hakan ba, tace “Ko dai nayi kama da warce take iskanci ne?” Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace “Gaya min me ya faru?” Tace “No! answer my questions first” Dr Khalil yace “Mayraah, in our society today da kuma al’adan mu na hausa fulani duk macen da ta bar gaban iyayenta for whatsoever reason dole zata yi facing fiye da haka a rayuwa, kin ga wasu za su mata kallon warce tafi karfin iyayenta, wasu su mata kallon er iska warce idonta ya bude tunda an san dai tafi karfin iyayenta ne ya sa ta shiga duniya, don babu iyayen da za su ba ma er su go ahead ta tafi tayi zaman kanta, wasu za su mata kallon warce ke karuwanci, bazan boye maki ba Mayraah at first da na ga take taken ki nayi maki kallon warce ta zabi ta shigo Abuja tayi rayuwar shashanci ne, even the hotel u lodged in na sa maki question mark a lokacin, but at the same time u look innocent” Goge hawayen dake sauko mata tayi tana kallonsa, yayi kasa da murya yace “Tell me what happened” Cikin rawan murya tace “Shi yasa Ahmad yake min kallon er iska har yake tunanin zan iya bin sa hotel mu kwana?” Khalil ya zaro ido yana kallonta, yace “Ahmad??” Ta fashe masa da kuka sosai, mikewa Khalil yayi ya ma kasa ce mata komai gaba daya jikinsa yayi sanyi Ahmad bazai taɓa canzawa ba kenan, bayan few seconds ya sauke wani ajiyar zuciya ya duka gabanta yana kallonta a hankali yace “Only this is enough for you kiji hankalinki ya koma gida Mayraah, mace in ba gaban iyayenta take ba kowa ma kallon da yake mata kenan to be frank…. You have given dem enough space na sati biyu yanzu, nasan duk hankalinsu ba a kwance yake ba na rashin ki” Mayraah tayi murmushin takaici tana share idonta bata son tace masa komai game da abinda matarsa ta shigo tayi mata bayan fitarsa, bazata so ta dalilinta happy family din su samu issues ba, tunani ne iri iri a ranta a lokacin, daren ranan a nan asibitin Khalil ya sa ta kwana, with d hope that as early as possible kafin zuwan MD zai je yayi dropping dinta, amma sai suka tashi da wani aiki da asuba tare da sauran likitocin asibitin, zuwa karfe tara Mayraah ta gama shawaran abinda zata yi a zuciyarta, tun cikin dare take tufka da warwara a ranta ko baccin kirki bata yi ba sai bayan sallahn asuba ta samu bacci ya dauketa, yanzu kuwa tana tashi ta tafi bandakin office dinsa ta wanke bakinta da mouth wash ta wanke fuskarta sannan ta fito ta dau Handbag dinta ta nufi kofa ta fita har sannan kuma su Dr Khalil basu fito theatre ba, tana sauka stairs tayi ido hudu da MD da shigowarsa reception din kenan da wasu turawa biyu sai bakin fata daya duk sanye da suit, a tare da su wata dattijuwa ce warce bata da maraba da halfcast coporately dressed in black suit with skirt da iyakarsa gwiwa, dai dai nan su Dr Khalil ma suka fito theatre da likitoci kusan hudu, gaba daya nurses gaida matar suke da ladabi, har ma da Dr’s din tana amsa su cikin fara’arta da turancinta me cike da phonic, MD gaba daya attention dinsa na kan Mayraah bayan ya wani hade rai kamar bai taɓa dariya ba da ya hangota, wato a asibitin ma ta kwana kenan, Mayraah ta karasa saukowa downstairs ita ma ta gaida matar, Matar ta sakar mata murmushi tace “Helloo” Har tayi gaba ta sake juyowa tace “Are you a staff here young lady?” Mayraah ta ɗan kalli MD da ya kafeta da ido, a lkci daya ta kalli Dr Khalil taga ya nodding mata kai alamar ta ce eh, da sauri ta gyada ma matar kai kamar kadangariya, matar ta kalli baƙin mutumin dake cikin fararen fatan tace “Dr Yemi, you remember my Late moslem frnd Hajiya Amina?” Yace “Oh yes, Late Professor Amina, exactly i remembered Ma” Matar ta nuna Mayraah tace “Her replica, she just reminded me of her, may her soul rest in peace” Duk suka amsa da “Ameen” Matar tace “Ba don nasan yaranta ba kuma bata da karamar yarinya da nace ke yarinyar ta ce…” Mayraah dai sai murmushin karfin hali take tana kallon kyakkyawan dattijuwar don bata taɓa zaton tana jin Hausa ba sai gashi tayi hausa, amma Hajiya Amina da tace take replicating ya tsaya ma Mayraah cak a rai, to ko dai she is related to the Hajiya Amina tunda tace suna kama, MD na kallon Ceo din tasu da ladabi yace “Ma, You’ve stood for so long”
Da ido Mayraah ta bi su har suka haura sama da sauran Dr’s din dake biye da ita za su rakata office dinta, Ceo din na hawa second stairs ta kara juyawa ta kalli Mayraah, sai kuma ta kalli MD dake bayanta tace “What is that her name again?” MD ya girgiza kai da sauri yace “I have no idea Ma’am” Ta kalli Mayraah tace “What did u say ur name is?” Mayraah da gabanta ke faduwa tace “My name is Mayraah” Ceo ta bude ido tace “Mary Ann?” Dr khalil yace “She is Mayraah Ma’am” Daga likitocin har nurses duk kallon Mayraah suke, MD dai bai sake kallon downstairs din ba, Ceo na gyada kai tace “She should meet me in my office, in 30 mins time” Tana fadin haka ta ci gaba da tafiya sauran likitocin na biye da ita, Dr Balogun yayi ma Mayraah thumbs up ya wuce sama yana amsa gaisuwan da take masa, Dr Khalil ya nufo ta ya mata murmushi yace “Good morning” Tace “Ina kwana?” Yace “Har kin tashi baccin?” Ita dai bata ce komai ba, yace “Kije office dina ki jira tunda tace ki sameta nan da minti talatin” Mayraah tace “Toh” Sama ta wuce, few of the nurses suka bi ta da kallo with enviousness and jealousy. Dr Khalil ya bude office dinsa kenan zai shiga wayarsa ya fara ring yana dubawa yaga MD ke kiransa, ya kalli Mayraah dake zaune office din ya karasa ciki yace “Yanzu za a kawo maki breakfast” Tace “Toh Nagode” Fita yayi daga office din zuwa office din MD, tsaye ya samesa office din yana jiransa, MD ya nufesa cikin fada yace “Kasan implications din da kake kokarin ja min kuwa yanzu Khalil? How on earth will i explain to the CEO that this silly gal isn’t a staff here?? I told u bana son sake ganin yarinyar nan a asibitin nan you are taking me for granted, saboda tsabar bata da kunya an tambayeta if she is a staff tayi nodding kanta, waye yayi employing dinta? Wa ya bata aikin? Ko ka fara bada aiki ne a asibitin nan ban sani ba?” Dr Khalil ya nemi waje ya zauna yace “To avoid the complications u are talking about kawai kayi imputing data dinta a system yanzu MD a wuce wajen” a fusace MD yace “Never!! Bazan taɓa bata aiki a asibitin nan ba like i have already said, ko dole sai tayi aiki a nan? Ba ga asibitoci iri iri da zaka iya samar mata aiki ba, all my thought was that u will be contented with Zainab amma ashe ba haka bane, ka makale ma er cikinka kasa duk ta rainamu ko aikin bata samu ba, baza kuma ta taɓa samu ta wajena ba, watch and see” Yana kai wa nan ya fice daga office din, Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi. Ceo na zaune babban office dinta wanda mutum sai yayi tunanin a kasar waje ne tana stamping wasu files MD ya shigo, tana ci gaba da abinda take tace “I won’t be able to go round the hospital today because i will be leaving in an hour time, i have a meeting to attend, and when did u say the next workshop is in Lagos?” Da ladabi MD yace “In 2 weeks time Ma’am” Tace “Ohk, i think zan koma UK nan da kwana biyu saboda exams da yaran nan za su fara, I will be back before the Lagos workshop, Send me the names and details of all our staffs i have a little token for them, and lest i forget there will be a medical conference in the US, za mu je da staffs biyu….” Bata jira ya bata amsa ba tace “Where is the Lady i asked to meet me in 30 mins time? Did she hear me right?” Yayi kasa da kai yace “Erm… Ma’am, but” Daga kai tayi ta kallesa don duk wannan maganar da take kanta na kasa tace “Is there anything Aliyu?” Ya girgiza kai da sauri yace “No, i will get her right away” Daga haka ya juya ya fita daga office din. Mayraah na zaune office din Dr Khalil ta bude burger din da aka kawo mata with healthy toppings for breakfast sai black tea taji an bude kofa, juyawa tayi Dr Khalil ya shigo yana kallonta yace “MD yana kiranki office dinsa yanzu, pls and pls Mayraah be a good gal, i am hoping data dinki zai yi imputing, banda girman kai da kallon rainin wayo” Mayraah na kallonsa da mamaki tace “Girman kai da kallon rainin wayo kuma?” Dr Khalil yace “Yes kina da girman kai, sannan kin iya kallon rainin wayo amma duk baki san kina yi ba” Shiru tayi tana kallonsa don ita tunda take babu wanda ya taɓa ce mata tana da girman kai ko kallon rainin wayo, hakan kuma kamar yayi shock dinta, Dr Khalil ya zauna gefenta yace “The thing is that, ke girman kai shi ma MD girman kai shi yasa ku ka kasa jituwa… Halinku daya da shi i am telling u the truth” Mayraah ta hade rai tace “Aa ni ba halinmu daya ba, i am not rude and arrogant, sannan ina ba mutane value dinsu, shi kuma he is rude and at the same time arrogant” Murmushi Dr Khalil yayi yace “In gaya maki gaskiya? Da za ki hadu da MD a waje ba a asibiti ba wallahi za ki ga he is the most lovely person to be with, idan aka ajiye aiki gefe daya wallahi yana da kirki and he is a free minded person outside of work, kawai shi baya son raini ne kuma baya son wasa da aiki, he is always serious when it comes to his discipline, shi yasa za ki ga kamar bashi da kirki, ba haka bane yana da kirki sosai, ni baki ga yanda muke da shi ba? He is my very good frnd amma da zaran muna asibiti ajiye frndship din yake aside ayi abinda ya kamata, and i do respect him as my boss” Mayraah dai bata ce masa komai ba don in duk jikinta kunnuwa ne bata jin zata yarda MD yana da kirki ita dai. Dr Khalil yace “So now, go and meet him in his office, and be a good gal while in there” Mayraah ta mike tace “I have always been a good gal, just that yana da anger issues ne” tana fadin haka ta nufi kofa ta fita. Tana tafiya a hankali ta isa office din MD, tayi knocking ta jira har sai da yayi mata izinin shigowa sannan ta bude kofar ta shiga, sau daya ta kallesa ta sunkuyar da kai tana tafiya a hankali ta isa har gaban table dinsa, shi dai tun da ta shigo bai dago ba idonsa na kan laptop da yake operating, tace “Good morning sir” Bai amsa ta ba yana ci gaba da abinda yake, fingers dinsa da ya daura kan table ta dinga kallo, bayan few seconds ta daga kanta a hankali idonta ya sauka kan eyebrows dinsa, kallonsa take babu ko kiftawa, shi kam har sannan bai daga kai ya kalleta ba operating laptop din gabansa kawai yake, can dai ta sake gathering courage tace “Good morning sir” Still not looking at her yace “I am not deaf Madam, where is ur CV? And did u have working experience in anywhere?” Shiru tayi tana kallonsa, sai a sannan ya daga kai ya kalleta yace “Good! no CV, No working experience, shine saurayinki ya dage sai na baki aiki with pending CV saboda ance masa korean film muke acting a nan, ko kuma ance masa i am also mad like he is, mutane nawa ke da CV dinsu available amma basu samun aikin ba sai ke da naki is still pending, infact ni ban ma yarda kinje higher school ba, kuma may be ya manta ba a bama underage aiki a asibitin nan, cause i don’t think u are up to 18, always coming here to inconvenience our Staffs and patient, to daga yau kar ki sake shigowa asibitin nan, i will talk to the securities to help u out immediately bamu da vacancy a nan, saurayin naki ai yana da connections me yasa bazai samar maki aiki a wasu asibitocin ba sai lallai wannan” Mayraah dai kallonsa kawai take, aka bude office din duk suka juya, Ceo ce da kanta ta shigo office din, MD ya mike da sauri ganinta yace “You need anything Ma’am” ta karasa tana mika masa wayar hannunta tace “Attend to them pls…” Amsa yayi ya daga ya kai kunne introducing himself immediately with his British accent, Ceo ta kwashe textbooks da ta gani kan table dinsa tace “Get urs pls” Sai a sannan ta kalli Mayraah da ta koma gefe ta tsaya kanta a kasa, tace “Ba ke nace ki sameni office ba?” Mayraah ta gyada mata kai kamar kadangariya, Gaba daya hankalin MD dake waya na kansu, Ceo ta mika mata textbooks din hannunta tace “Come with them” Mayraah ta amsa da ladabi sannan ta bi bayan Ceo din. Suna isa office dinta Mayraah bata zauna ba sai bin ko ina na office din take da ido, bata taɓa shiga office irin wannan ba sai sai ta gani a film kawai, kallon hoton ceo dake office din da wasu likitoci turawa ta dinga yi, Ceo na gama ajiye textbooks da ta dauko office din MD a library dinta ta dawo ta zauna ta nuna ma Mayraah kujera tace “Get sitted Mary Ann” Mayraah ta zauna kanta a kasa, ceo ta dau wayarta after few minutes ta mika ma Mayraah with a smile on her face, Mayraah ta amshi wayar tana kallon matar dake hoton, taga dai suna yanayi da matar amma matar ba fara bace, Ta daga kai ta kalli Ceo dake kallonta, Ceo tace “Did u see the resemblance?” Mayraah tayi murmushin karfin hali tace “Eh na gani muna kama” Ceo tace “Good, Her name is Amina, she is my childhood frnd, she is the reason i am where i am today, she was my God on earth….” Mayraah ta kifta ido jin kalmarta na karshe, can kawai ta hango gold rosary din dake makale wuyarta, Ceo tace “But she left so soon, Amina died 7 years ago, har yau har gobe ina jimamin mutuwar Amina da nake jinta kamar er uwata, her in-laws sent her to her early grave, they made marriage life difficult for her, they shattered her, har yau mijinta na nan Abuja” tissue din dake saman table dinta ta zaro tana share hawayen cikin idonta, jikin Mayraah yayi sanyi tana kallonta a hankali tace “Sorry about that ma’am” Ceo tayi murmushi tace “Thank you, zan hada ki da yaranta in sha Allah, i know they too will attest that u have a resemblance with Hajiya Amina, Abbakar is in Uk, Yusuf is in India, and Maryam is married in UK also, but they are all adopted, she adopted them tun suna yara from orphanage, ita Allah bai bata rayayyun ‘ya ya ba, it’s always one thing or another” jikin Mayraah yayi sanyi sosai ta kasa ce ma Ceo komai, har cikin ranta taji tana son tasan wa enda suka san Hajiya Aminar nan, a hankali tace “Don Allah zaki hadani da yaran nata?” Ceo na murmushi tace “Sure i will… You can leave now, tell MD to come over with the phone i took to him” Mikewa Mayraah tayi tace “Thank you Ma” Daga haka ta nufi kofa Ceo ta bi ta da kallo har ta fita ta kulle mata kofar. office din Dr Khalil ta nufa duk jikinta a sanyaye, ya ajiye wayarsa da yake ta kiran Ahmad yaki dagawa saboda yasan abinda ya aikata, ya mike yana kallonta bayan ta shigo ganin yanayinta yace “Ya ku ka yi da shi?” Mayraah ta zauna tace “Ka kirasa kace masa tace ya kai mata waya” Dr Khalil yace “Kin je office din nata ne?” Gyada masa kai tayi, yace “Shi ya turaki?” Ta girgiza kai tace “Ta sameni ne a office dinsa” zagayowa yayi ya dawo inda take yace “To ya ku ka yi da ita?” Mayraah tace “Kawai ta nuna min hoton matar da tace ne” Yace “Kuma kinga kuna kama?” Ta daga kai ta kallesa tayi masa nodding kawai, Dr Khalil yayi shiru with different thoughts running his mind kamar yanda ita ma tunani iri iri ke yawo a ranta a lkcn, can yace “Tace zata hada ku ne?” Nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah a hankali tace “Ae tace ta rasu” buda ido yayi sosai, can yace “To yaranta fa?” Mayraah na goge idonta tace “Tace zata hadamu” Khalil yace “Ita matsalarta shiririta ta da shauninta yayi yawa, yanzu tana iya kama hanya in ta tafi sai bayan shekara za mu ganta a kasar nan” Mayraah dai sai kallonsa take, yace “Amma ki kwantar da hankalinki kafin ta koma dai in tana ganin ki she will be remembering definitely” Mayraah tayi shiru, sai kuma a hankali tace “Zan wuce gida” Yace “Wani gida?” Ta daga kai ta kallesa, ya sauke idonsa yace “Zaman kan naki zaki koma Sulejan ki ci gaba da yi?” Ta wani kallesa, calmly yace “Mayraah” shiru tayi bata amsa masa ba, yace “Kamar yanda nace maki jiya, it’s high time ki koma gida yanzu, you’ve given them enough space nasan yanzu komai ya daidaita in sha Allah” Mayraah ta girgiza kai tace “I will go back when i know it’s right to do so” Da mamaki Dr Khalil yace “Abinda Ahmad yayi maki har yanzu bai zame maki darasi ba kenan, to let me tell you, ba Ahmad ba kowa ma kallon da zai maki kenan, don duk mace me mutunci ko gunduwa gunduwa da namanta iyayenta ke yi baxata bar gabansu ba, kuma duk warce kika ga ta bar gida ta tafi wani gari to babu wanda ya isa ya canza kallon er iskan da mutane za su dinga mata, ba ga su nan muna gani a Abuja ba sun tsallake sun bar gida sun dawo nan suna ta iskancinsu” Mayraah ta mike tace “Ni ai Allah ya san ba iskancin nake ba, kuma ban ce bazan koma gida ba, amma sai idan ta hadani da family din matar da na gani a hoto” Dr Khalil yace “Ai ko kina gida za a iya hakan, beside iyayenki na samun labarin kin samu aiki permanently a asibitin nan i know they will support u ki ci gaba da aikin ki, cause kowa yasan asibitin nan a kasar nan, it’s ba privilege working here….” Mayraah tace “I will think about that” Dr Khalil yace “Kinsan menene matsalarki Mayraah?” Mayraah tayi shiru tana kallonsa yace “Taurin kai” Zata yi magana aka bude office din duk suka juya, MD ne tsaye bakin kofar, Mayraah ta kauda kanta tana kallon Khalil tace “We will continue on phone” Daga haka ta dau pack din burger dinta da jakarta ta nufi kofa ganin babu hanyar da zata wuce tace “Excuse me pls” Dr Khalil ya koma kujeransa ya zauna yana kallonsu yana murmushi, MD na mata wani kallo yace “Zan ƙwada maki mari, ni kike ce ma excuse you pls? Or are you harebrained?” Bata ko kallesa ba ta raba ta gefensa almost touching him tayi ficewarta a ranta kuwa cewa tayi sai dai ya ci kansa. MD ya juya ya kalli Dr Khalil a fusace kafin yace komai Dr Khalil yace “Kasan me Dr Aliyu? Har nayi picturing ka mace ma yarinyar nan kun fara soyayya da zai yi leading to marriage, it will really make sense, dama naga kamar yanzu baka da budurwa ko?” Yana kai wa nan ya fashe da dariya not minding MD’s weird facial expression a lokacin. Mayraah na isa Suleja bayan tayi share sharen gidan don ta kwan biyu bata zo ba ko ina yayi ƙura, tayi wanka sannan ta dafa Indomie ta ci, tun jiya da daddare ta kulle sim card din da ta kira Musharraf da shi saboda yanda ya dinga kiranta, dauko wayar tayi kamar zata bude sim din kuma kawai ta fasa ta ajiye wayar, tana ta zaune dakinta maganganun Zainab na mata yawo a kai, making her feel so hurt a zuciyarta, kawai sai tayi murmushi tana goge hawayen da ya cika idonta, hoton nan da ceo ta nuna mata ne kawai ya jinkirta abinda tayi niyya a ranta yau, she really want to know who the woman in the picture is, amma da ta tuna Ceo tace mata ta rasu sai jikinta yayi sanyi sosai, Ahmad ne ya fado mata, ita fa ta dade bata yi mamaki irin mamakin abinda Ahmad yayi mata ba, to gani yayi tayi kama da yan iska ne ko kuma ya taɓa ganin tayi wani action da yayi kama da na iskanci? Har cikin ranta taji tana appreciating Dr Khalil kuma tana jinsa kamar Ya Maheer because he was there for her always, kiran azahar ya sa ta tashi taje tayi alwala, sai da tayi sallah sannan ta kwanta tayi baccin da bata samu tayi ba jiya. Bayan la’asar Mayraah na wanke plate din da tayi amfani da shi a kitchen taji ana knocking gate din gidan, so tari idan Maman Hanan ta lura ta dawo suleja ta kan shigo mata su yi hira, wani lokacin kuma daya neigbor dinta Harira ma na shigowa duk sanda suka ga ta dawo, Hijab dinta ta saka ta fita, tana tsaye jikin gate din gidan tace “Waye?” taji muryar namiji yace “Assalamu alaikum” Mamaki ne ya cikata, tace “Waye?” Yace “Baƙi ne ki bude gate din ki fito” Sosai gabanta ya fadi tace “Baƙi kuma? Ni bana expecting baƙi daga ko ina” Mutumin yace “Eh mu ma dalili ne ya kawo mu, bamu yi tunanin za mu zo anguwan nan yau ba” Kasa cewa komai Mayraah tayi don gaba daya ta tsorata, mutumin yace “To cut everything short don naga kamar kin tsorata, mu jami’an tsaro ne… We are not here to harm u Madam, amma idan kika ki bude gate din, we are sorry there is nothing we can do about it za mu bude gate din by all means” Mayraah that was so afraid tace “But what did u want from me?” Yace “Open the gate” ƙin budewa tayi ta koma ciki ta dau wayarta ta fara dialing number Dr Khalil a tsorace.
Bayan wani ɗan lokaci Mayraah ta dawo bakin gate din, tayi gathering courage duk da yanda gabanta ke faduwa tace “Sorry… brother na yace i shouldn’t open the gate till he comes” shiru duk ta ji sun yi bayan ta gaya masu haka, sai kuma taji mutumin yace “Ki bada number brother din naki” Mayraah tayi tsuru tsuru jin abinda yace, sake maimaita maganar yayi, cike da karfin hali tace “Aa ni bazan bada ba sai na tambayesa tukunna” Mutumin yace “Kirasa yanzu kice we are requesting for his number, call him immediately” Komawa cikin gidan Mayraah tayi ta sake kiran number Dr Khalil, yana fara ring ya daga yace “I am on my way now kar ki bude gate din” Kamar zata yi kuka tace “Wai sun ce in basu numberka kuma” Ya ɗan yi shiru sai kuma yace “Number na?? ohk ok basu kawai, but do not open the gate, just call out the number for them” Ta gyada masa kai kamar yana ganinta, yace “Kin ji me nace?” A hankali tace “Toh” Komawa gate din tayi bayan ya katse wayar, cikin karfin hali tace “Yace in baku number din, zan kira maku digit din yanzu” Mutumin dake bata amsa yace “Ohk, do so now” Kiran numbers din khalil ta shiga yi har ta gama, mutumin yace “Good” Ji tayi kamar sun bar bakin gate din, ita dai sai zare ido take har taji tafiyar motarsu, duk da haka bata yarda ta bude gate din ba ta koma cikin gidan duk hankalinta a tashe, gaba daya ta rasa wani tunani ma zata yi, tana ta zaune cikin fargaba har wayarta ya fara ring wajen karfe biyar da wani abu taga Dr Khalil ne ke kiranta, dagawa tayi ta kai kunne da sauri, yace “Fito ki bude gate din” Tace “Ka zo ne?” Yace “Eh ina waje” mikewa tayi dama har sannan bata cire hijab din jikinta ba ta fita zuwa bakin gate din, bugun zuciyarta ya tsanata cike da karfin hali ta makale jikin gate din tace “Ka kadai ne?” Yace “Ni kadai ne mana Mayraah” a hankali ta bude gate din with throbbing heart, tsaye ta gansa bakin gate din, ta marairaice masa tace “Did they call u pls?” Yace “Yea they called, but it’s not even something serious” Tace “Toh me suka zo yi? Me ya faru? Did commit any offense?” Yace “Za mu je station din yanzu, kawai tambayoyi za su maki….” Ta fashe da kuka sosai tace “Toh ba sai mutum yayi laifi ba ake kai sa station, ni me nayi? Don Allah kar ka boye min ka gaya min” Yace “Nace maki it’s not something serious Mayraah, yanxu haka daga station din nake, kawai suna daukan statement dinki zan dawo da ke gida, kar ki wani daga hankalinki” Cikin kuka tace “Statement of what? What wrong have i committed?” Yace “Na fa ce ki kwantar da hankalinki, i am with you, yanzu ba daga Abuja nake ba saboda ke?” Share idonta tayi tana kallonsa, yace “Dauko wayarki mu tafi lokaci na wucewa” A hankali ta juya ta koma cikin gidan, wayarta ta dauko da handbag dinta ta fito, a cikin motarsa ta samesa yana jiranta, bayan ta kulle gidan ta tafi ta bude front seat ta shiga motar, kana ganinta kasan duk jikinta yayi sanyi sosai kuma a tsorace take, bayan sun bar layin ya kwantar da murya yace “Pls calm down Mayraah, kema kinsan bazan bari ayi harming dinki ba, beside i told u it’s not something serious, u need not to worry kar ki je jininki yayi kasa” Ta fashe da kuka tace “But i want to know what i did, ina son sanin menene ya sa suka zo za su tafi da ni, wani laifin nayi? I know kasani tunda kaje station din, definitely u are aware, you are just hiding it from me, don girman Allah ka gaya min menene ko zan samu relieve” Dr Khalil ya ɗan kalleta, sai kuma yace “Ohk bazan boye maki ba, kinsan me ke faruwa?” Ta girgiza masa kai da sauri zuciyarta na bugawa, ya ɗan yi shiru sai yace “Kinsan ko wani society or rather community, da irin ka’idarsu ko kuma ince da irin way of life dinsu, da yanda suka ba al’adarsu da addinin su muhimmanci, right??” Shiru tayi tana kallonsa waiting for him to go straight to the point, ya sauke ajiyar zuciya yace “To kin dai ga garin nan da kike ciki yawanci majority dinsu musulmai ne, sannan akwai Hausawa babu laifi, so the community are against gidan da kika kama kina zaune ke kadai kina zaman kanki don suna da yara kuma suna duba tarbiyar yaransu suna tsoron kada yaransu suyi tunanin hakan abu ne me kyau mace ta kama babban gida irin wannan tayi zamanta, sannan sunce ke kince kina karatu amma sun gano ba karatu kike ma a garin Abujan ba, iyaka idan kinje kinyi abinda za ki yi a Abuja sai ki dawo nan ki bude gida ki shiga bayan kwana biyu ki sake komawa cikin Abuja, sannan a complain dinsu sun ce akwai saurayin da ma yake zuwa ya sameki a nan din” Sake baki Mayraah tayi tana kallonsa har zuwa sanda ya dasa aya, she was so shock and speechless, yace “To ban san ko bayan zuwan da nayi last week ko akwai wani wanda ke zuwa wajenki ba” Mayraah bata san sanda ta fashe da kuka ba tace “Allah ya saka min, wallahi bazan yafe masu ba, tunda na dawo nan babu wanda ya taɓa zuwa wajena sai kai, bazan taɓa yafe wannan kazafin da suka min ba” Dr Khalil ya langwabar da kansa yace “Kinga abinda nake gaya maki ai ko, mutuncin ya mace gaban iyayenta, in ko ba gaban iyayenta ba to gidan mijinta, in dai a arewa ne duk inda za ki je to wallahi kallon da za a maki kenan baza ki taɓa canza su daga maki kallon nan ba, a takaice gani suke sharholiyarki kike shigowa kiyi a Abuja sai ki dawo nan Suleja ki fakee, let me tell u something…. kiwon mutane ake yanzu ba fa dabba ba, duk footstep dinki a kan idon mutane yake” Mayraah dai ta kasa cewa komai sai kukan bakin ciki da takaici take, har suka iso garin Abuja ta kasa daina kukan da take har ya ma daina lallashinta, wani station taga sun zo, bayan yayi parking a waje yana kallonta yace “Kiyi hakuri in sha Allah komai ya zo karshe daga yau, wipe off ur tears and trust me I will be by ur side” A hankali ta goge idonta tana kallonsa cikin rawan murya tace “Toh yanzu me zan ce masu idan mun shiga?” Yace “Kar ki damu, na riga na masu bayanin komai, iyaka Statement dinki za a dauka, shikenan” Daga haka ya sauka daga motar ita ma ta sauka har lkcn hawaye ya ki tsaya mata, she felt so hurt da irin kallon da mutane suke mata, ga Ahmad, Zainab, and now sulejan da take, calmly yace “Na fa ce ki daina wannan kukan” Ta gyada masa kai da kyar tana kara goge idonta, ya nufi cikin station din tana biye da shi a baya. Dr Khalil ya gaisa da yan sandan cikin station din yace “Za mu iya shiga office din Dpo din?” Police officern yace “Ehh suna ciki har yanzu, You can go in….” Ya kalli Mayraah dake tsaye gefensa kamar warce tayi ma sarki karya gaba daya a tsorace take don bata taɓa shigowa police station ba, calmly yace “Mu je” Bin bayansa tayi har xuwa office din Dpo din, ya bude kofar ya fara shiga da sallama sannan ita ma ta shiga gabanta na faduwa sosai, makalewa tayi jikin kofar tana kallon wanda ke zaune kan Sofa a office din babu ko kiftawa, can ta juya a hankali ta kalli Dr khalil kamar idanuwanta za su fito, Dpo ya daure fuska yace “Kee, shigo ki kulle ma mutane office” Ji tayi kamar ta zura a guje, ta dai kulle kofar da kyar ta sunkuyar da kai, amma ta kasa karasawa ciki don gaba daya tayi shock a wajen, tuni Dr Khalil ya tafi ya zauna kan kujera, Dpo ya bata thumbs up yana gyada kai cikin jinjina yace “The runaway girl!!” Kasa daga kai tayi, cikin daga murya yace “Ya sunanki?” Da kyar ta daga kai ta kallesa cikin karfin hali tace “Mayraah” Yace “Mayraah the runaway girl…. to nemi kujera ki zauna” Ta saci kallon wanda ke zaune kan sofa din, ai tana ganin irin kallon da yake mata tayi saurin dauke kai kamar munafuka ta tafi ta zauna kan kujera ta takure waje daya, shi dae Khalil murmushi kawai yake, Dpo yace “Kin san wannan da yake zaune?” Sunkuyar da kai tayi, ya mata tsawa yace “Ke…” Cikin rawan murya tace “Yayana ne” Yace “Ya sunansa?” saboda tsoron kar ya sake mata wani tsawan cikin rawan murya tace “Ya Usman” Dpo yace “Yau kwananki nawa da barin gida?” Ta fashe da kuka ta kasa cewa komai, yace “Ba kuka nace ki min ba malama, warce ta iya tsallakawa ta bar gida ai zuciyarta ya kekashe kenan babu wani batun kuka, kwananki nawa yau da barin gida?” Cikin rawan murya tace “Kamar 3 weeks” Yace “Kuma baki da intention din komawa anytime soon ko?” Daga kai tayi tana kallonsa hawaye na sauka idonta, Dpo din yayi shiru, sai kuma ya nuna mata kujeran dake gaban table dinsa yace “Dawo nan ki zauna” Mikewa tayi tana kuka ta tafi ta zauna kan kujeran, yace “Mayraah” Ta daga kai ta kallesa hawaye na sauka idonta, yace “Abinda kika yi kin kyauta kenan? Saboda wasu unforseen circumstances sun faru that doesn’t mean it is the end of life my dear, what if hannun mutanen banza kika fada? Did you know the type of era we are in now? Kinsan irin munanan cases da muke dealing da kullum a wajen nan? me yasa za ki zabi kawai ki bar gida saboda an samu matsala? pls nan gaba ko wani kika ga zai yi abun nan da kika yi ki basa shawaran kar yayi ba shi da amfani, ita dama rayuwa kowa da ƙaddararsa taki a haka ta zo sai kiyi hakuri ki zama me imani ki amshesa hannu bibbiyu, ko da wasa karki sake tunanin wannan shine solution dinki ke macece, leaving home is never a solution, ke baki tunanin halin da iyayenki da yan uwanki za su shiga saboda abin nan da kika aikata? Ko ke ba musulma bace? Don duk musulmi an san sa da tawakalli ne” Ita dai kanta na kasa hawaye sai sauka idonta yake, yace “Yanzu kin san ta yanda aka bi ki har Suleja?” Ta girgiza masa kai, ya dauko wani kwali ya ajiye mata a gabanta, kallon kwalin ta dinga yi sai kuma ta saci kallon Usman dake kallonta tayi saurin dauke kai, Dpo yace “Ko da wasa next time do not try this nonsense again pls” Sai kuma ya kalli Dr Khalil yace “Kai kuma Allah ya saka maka da alkhairi for all ur effort, ni yanzu zan fita, za ku iya tafi Allah ya tsare gaba…..” Har suka fito daga office din Dpo Mayraah bata yarda ta kalli Usman ba, sai makalewa kusa da Dr Khalil take, bayan sun fita daga police station din, Dr Khalil na kallon Usman yace “Ina kuka nufa yanzu, don naga it’s almost magrib” Ita dai Mayraah na can gefe tsaye gabanta sai faduwa yake, ta saci kallon Usman yafi a kirga, Usman yace “Ba komai, na saba driving din dare, i will drive to kaduna in sha Allah” Dr Khalil yace “Toh ba damuwa, idan ka isa kadunan sai mu yi waya” Usman yace “To in sha Allah, thank you so much Dr” Dr Khalil yayi murmushi yace “You are welcome” Daga haka Dr Khalil ya koma gun Mayraah yace “Ki je ku tafi…” Ko rufe baki bai yi ba Mayraah ta fashe da kuka tace “Wallahi ni dai tsoronsa nake ji, na shiga uku” Dr Khalil ya buda ido yace “Saboda me?” Cikin kuka tace “Zai iya marina na sani, dama yaya Maheer ne” Dr Khalil yayi murmushi yace “Haba dai, ba abinda zai maki” Cikin kuka tace “Wallahi zai iya, me yasa ba Yaya Maheer bane ya zo” Juyawa Dr Khalil yayi ya kalli Usman da ya rungume hannu yana tsaye jikin mota fuskarsa babu yabo babu fallasa, komawa yayi wajensa yana ɗan murmushi yace “Barrister don Allah ayi mata hakuri, tace tsoro take ji zaka bugeta” Usman ya girgiza kai yace “Not at all…. Ka tambayeta ko na taɓa dukanta, she is waisting our time, muna da tafiya a gaba” Dr Khalil yace “To plss ayi hakuri barrister” Sai da Dr Khalil yayi da gaske da Mayraah sannan ta tafi ta shiga motar Usman, amma tana shiga sai ta wani tsuke fuska tana makale da handbag dinta, Usman ya kara yi ma Dr Khalil sallama sannan ya bude driver seat ya shiga ya tada motar, Dr Khalil ma ya nufi motarsa, har suka hau kan hanya bai ce mata ba ita ma bata ce masa ba.
Mayraah na ganin sun kusa Suleja ta kallesa a karo na farko tana fidgeting fingers dinta a hankali tace “Don Allah yaya zan iya dauko jakana?” Ganin bai ce mata komai ba driving dinsa kawai yake, ta kauda kai bata sake cewa komai ba. A hankali Mayraah ta bude idonta daga baccin da ya dauketa ta gansu a cikin garin kaduna, gyara zama tayi da sauru ta tana kallonsa don ya maida mata kujeran bava vanda zata zama comfortable sanda take baccin, shi dai driving dinsa kawai yake pretending kamar bai ma san ta tashi ba, tun daga Abuja har zuwa yanzu da suke kaduna yaki ce mata komai, duk da almost half of the journey ma bacci take, wani hotel taga sun shiga bayan yayi parking ya bude motar ya sauka, babu bata lokaci ita ma ta sauko tana kallonsa ya kulle motarsa ya nufi cikin hotel din, ta wani tura baki ta bi bayansa, executive room ya biya masu, bayan ya amshi makullin dakin suka bar reception din, ita dai bin sa kawai take a baya har zuwa dakin, har cikin ranta take wishing dama Maheer ne, babban parlor ne da bedroom suka yi lodge in… Bayan ya ajiye wayoyinsa da car key ya cire agogonsa ya ajiye kan kujeran parlon Mayraah dai sai bin sa take da kallo tana turo baki, sai a sannan ya daga kai ya kalleta, ta sunkuyar da kai da sauri kamar munafuka, sai kuma ta ga ya nufi kofa har ya fita ya kulle kofar, a hankali ta karasa ta bude kofar bedroom din ta shiga ciki, bayan ta ajiye handbag dinta da wayarta ta koma parlon, sabulun da hotel din suka basu ta dauka ta shiga bandaki tayi wanka sannan dauro alwala ta fito ta koma daki, bayan ta idar da sallah ta rage Ac din dakin ta kwanta duk da yunwan da take ji don ko abincin rana bata ci ba, tana ta kwance taji an bude kofar dakin, kin juyowa tayi sai ma kulle ido da tayi da sauri don bata san me zai ce mata ba, sai taji yace “Fito ki dauki abinci” tana jin haka ta bude ido ta turo baki duk da ba ganinta vake ba sai kuma ta mike zaune tana murza ido tana kallonsa, juyawa yayi ya bar bakin kofar, ta sauka daga kan gado ta bi bayansa, Kallon ledan abincin dake Kallon ledan abincin
Ка
table din gabansa tayi, sae taki karasawa ta dauka c
A
fa bata yarda da wanna shirun da yay mata ba, can ganin bai ce mata komai ba a hankali tace “To ni don Allah ka ajiye min kasa in dauka” Sae a sannan ya daga kai ya kalleta, tayi narai narai da ido ita ma tana kallonsa, gani take kawai planning din yanda zai wanka mata mari yake, tashi taga yayi ya bar wajen ya koma 3 seater ya zauna, tana tafiya a hankali a tafi ta dau ledan ta koma daki tana satan kallonsa, shi kuma ya bi ta da kallo. Washegari da asuba Mayraah ta idar da sallah bayan ta gama azkar dinta har ta koma ta kwanta taji yayi knocking kofar dakin, ta mike zauna tana kallon kofar har ya bude, zamowa kasa tayi daga kan gadon murya can kasa tace “Ina kwana yaya” yace “Ban sani ba… dauko stuffs dinki mu tafi” Ta dan buda ido tace “Bazan yi wanka ba” Kallon da taga ya mata ya sa ta tashi da sauri ta dau handbag dinta da waya, ya juya ya bar bakin kofar ta bi bayansa tana duba wayarta dake nuna karfe shidda da rabi, check out suka yi daga hotel din bayan ya basu makullin dakin, ta bude front seat din motarsa ta shiga, bayan some minutes of warming up the car suka fita daga hotel din ya kama hanyar kano. Karfe tara suka shigo garin kano, Mayraah na gain sun kusa gida haka kawai jikinta yayi sanyi, lokaci daya taji ta rasa sukuni, she don’t know how everybody will accept her back, bata san ko Ammi will still welcome her back home ba, tunanin hakan yasa hawaye ya cika idonta ba tare da ta sani ba don kawai ji tayi yana sauka fuskarta, rufe fuskarta tayi da hijab dinta tana shessheka,
Usman ya kalleta yana ci gaba da tukinsa yace “Ohk in maida ki Abujan kenan?” Cikin kuka tace “Aa” Yace “To me ya faru?” Ta fashe da wani sabon kukan tace “Ban san ko Ammi…” Kasa ci gaba tayi saboda kuka, Usman yayi kasa da murya yace “Ammi missed you, since you left she is not fine” Mayraah ta daga kai ta kallesa hawaye na sauka idonta, bai sake ce mata komai ba har suka shigo anguwan, yana horn bakin gate mai gadi ya bude gate din da sauri, ya shiga ciki yay parking a garage, Bayan ya kashe motar ya juya ya kalli Mayraah da ta fada duniyar tunani, yace “I hope u will never repeat such mistake again” Ta juya a hankali ta kallesa sai kuma ta gyada kai, a hankali yace “Abba was there for you, i was there for u, so was Doctor but u decided to follow ur heart that lead you astray” Cikin rawan murya tace “I am sorry” bude motar yayi ya sauka, amma ta kasa bude motar ta fito duk jikinta yayi sanyi wasu sabbin hawayen na zuba idonta, zagayowa yayi ya bude mata kofar yana kallonta, sunkuyar da kai tayi ta sauka ya nuna mata entrance din gidan yace “Mu je” Babu musu ta fara tafiya tana share hawayenta gabanta na faduwa, tsoro take kada Ammi taki ce mata komai, she don’t think zuciyarta zai iya daukan hakan, yana biye da ita a baya har suka iso entrance din shiga parlor, ta kasa bude kofar ta juya ta kallesa har sai da ya karasa gabanta ya bude kofar bai shiga ba ya juya yana kallonta, muryarta na rawa tace “I am afraid” Yace “U need not to be, everyone misses u badly” Ta gyada masa kai tana goge idonta, yace “Shiga…” Ba musu ta wucesa ta shiga parion ya bi ta da kallo, Mayraah a shiga parlon tayi ido hudu da Haseenah dake tsaye kofar kitchen tana iran sabon mai aikin Ammi ta bata irish din da taji tana soyawa wai ita bazata iya girki ba, Sake baki Haseenah tayi tana kallonta, Mayraah ta dauke idonta ta kalli direction din stairs jin kamar ana saukowa, Maheer ne ke saukowa tare da Ammi yana ce mata “Gaskiya Ammi i am only doing this because of you, but it’s stressful for me, menene yasa baza a sa ta a mota ita ma ta tafi kadunan ba….” Ido hudu yayi da Mayraah dake kallonsa babu ko kiftawa, ai bata san sanda ta nufesa da gudu ta rungumesa ba ta fashe da kuka, murya can kasa as if bai yarda ita bace yace “Mimi??” Haseenah tayi saurin dauke kai bayan ta saki wayarta dake hannunta ba tare da tasan ma tayi hakan ba, juyawa Usman yayi bayan ya dauke kai ya fita daga parlon, Ammi ta kasa motsawa daga stairs din da take tsaye, hawaye na zuba idon
Mayraah ta rufe fuska a kirjinsa tayi karfin halin cewa “I missed you so much yaya” as if whispering yace “Why did u leave just like that Mimi?” Ido hudu tayi da Ammi dake tsaye hawaye a fuskarta ta kasa saukowa downstairs din, Mayraah ta sauke idonta kasa… Zame jikinta tayi daga na Maheer ta daga kai tana kallonsa kamar vanda shi ma yake kallonta babu ko kiftawa, he is just hoping this is not one of his everyday dreams, har sannan hawaye bai daina sauka idon Mayraah ba, kawai tayi gathering courage ta tafi wajen Ammi, Ammi na ganin haka ta fashe da kuka sosai, Mayraah ta rungumeta cikin
Mayraah ta rungume:
rawan murya tace “Don Allah kiyi hakuri Ammi, ban san yanda zan yi ba ne…” Haseenah bata san sanda ta fita daga Parion ba tare da ta amshi irish din da take ira ba ta koma Chalet. Mama Ladi da ta fito daga bangaren Ammi cike da masifa tana cewa
“Haka kawai ba dangin iya ba na baba wannan wahala haka, o’o wallahi bazan iya ba don nayi ma kaina fada na daina shiga abinda bai shafeni, ga daki can an bar mata ban san me yasa take bivo mu nan tayi ta mana kazanta tana cutata ba…
Komawa baya Mama Ladi tayi da sauri tana gwalo ido bayan ta hango Mayraah tace “Wacece wanna kuma?” Sai a sannan
Mayraah ta sake Ammi ita ma tana kallonta, Mama Ladi ta rike haba tana gyada kai tace “Ba shakka!! to ina iyayen naki da suka jefa ki a kwata kina jaririya? Inji dai tare ku ka dawo da su?” Mayraah ta sunkuyar da kanta, Mama Ladi tace “Amma wallahi ke kam da ba don kada Ammi ta kullaceni ba sai ince butulu ce ke me manta alkhairi, haka kawai kika kama hanya kika shiga duniya kika bar mata da hawan ini mu kuma kika bar mu da rashin isasshen bacci kullum cikin tunaninki da alhinin bacewarki, Sannan yanzu ba kunya ba tsoron Allah galau galau kin kwashi kafafuwa kin dawo ke kadai, ni fa duk tunanina tare ai za ku dawo da iyayen naki tunda baki da mutunci kiri kiri kin nuna ai babu abinda kika hada damu, duk abinda muke maki kika rufa ido kika ci mana mutunci, haka nayi kwana biyu a asibiti wajenki ko runtsawa ban yi ba ga yunwa, amma baki gani ba sai da kika zalunce mu kika daga mana hankali, Mamuda ya dawo kamar wani zautattce wani lokacin takalmi wari wari yake sa wa ya fita, duk caji opis din kano babu wanda bai tafi ya kai cigiyarki ba, mu dai Allah ya isa rashin cin abinci da wadatattcen bacci da kika janyo mana” Tuni Ammi ta kama hannun Mayraah suka bar wajen, Mama Ladi ta bi bayansu still.
Tun da Mayraah ta shigo parlon Ammi take kallon Badiyyah dake kwance kasa tayi wani bakikirin kamar bata taba haske a rayuwarta ba ga was ban kuraje da suka cika mata fuska, Mayraah ta zauna kan kuiera don Ammi da take son tambaya ko Badiyyar bata da lafiya ne tuni ta fita daga parlon, kasa daurewa Mayraah tayi tana kallon Mama Ladi tace “Mama bata da lafiya ne?” Mama Ladi tace “Wa? Wai Badiyyah? Ai Badiyyah cikin shege tayi in baki labari Mera, cikin shege dai da kika
Tsabar shock Mayraah bata san sanda ta mike tsa’
Mama Ladi tace “Aa koma ki zauna ba wani batun rikicev
n
kema bamu san daga inda kike ba yanzu haka” Mayraah ta dinga kallon Mama Ladi babu ko kiftawa, Mama Ladi na kakkabe kujeran da taga Badiyyah ta zauna dazu tace “Hajja dai in gaya maki ta sallama ma duniya Badiyyah tace ko sunanta aka kira mata bata yafe ba, ta mata Allah ya isa yafi cikin kwando, ko ido suka hada sai ki ga Hajjan ta fara tari kamar zata shide vanzu haka zancen da nake maki Haiia tana can gidan Yahanasu a kaduna, sai kin ga gidan ko kiwon kare baza ayi a gidan nan ba don sai cuta ta kama karen ya mutu a banza, ni dai tun da na rakata ko minti sha biyar banyi cikin dan kuturun gidan ba na gudu gidan Mariya tunda dai abinda ya far ba wai ya shafeni bane kawai zumunci nake dubawa, banda ma na kai zuciya nesa ai da sai dai ki dawo ki ga na canza wani pamilyn, don wanna pamilyn namu dai ba pamilyn nuna ma duniya bane, pamilyn mu ya zama barbadadden pamilyn, Badiyyah ta lalata mana Pamily kawai sai dai muce Allah ya isa, gidan Mariya da na gudu in samu sauki can kuma yanda kika san kasuwar kurmi tunda babban gida ne war mijin da ban mijin duk suna ciki da bataliyarsu, wanna karen ya shigo, wancan dokin ya fita haka dai abun ba tsari, ke in takaice maki washegari da asuba nasa aka kaini tasha na hau mota na dawo kano inda na fi wayo, to shine sabida rashin tsoron Allah aka makala ma baiwar Allah Ammi Badiyyar take ta fama yanzu haka, banda ma Mamudan mutumin kirki ne ina zai yarda wannan annobar ta zauna masa gida ta lalata masa tarbiyyar yaransa maza, ai da muna da yan uwa a kauye kyan Badivvah kawai a turata can har sai ta haihu ta zauna tavi renon shegen a can, to bamu da kowa a kauye, Mamudan ma fa da farko kin amincewa yay yace a fitar masa da ita daga gidansa, to kin dai san Abban naku da shegen tausayi ga kuma tausayin matarsa da yake, a haka dai daga karshe yace a kyaleta ta zauna amma ko nan da gate baya son ta je kada yan anguwa su sa shi a bakin duniva suce ga me cikin shege a gidansa, kiri kiri
Mariya taki tafiya da ita aka bar Ammi da wahala, Allah dai ya isa kawai” Mayraah sai kallon Badiyyah da hawaye ke sauka idonta kawai take, kullum sai tayi kuka kamar ranta zai fita a gidan saboda Mama Ladi, da kyar ma in Mama Ladi bata daura mata depression ba saboda bad mouth dinta, Mama Ladi tace “Don haka kike baya baya da ita, mu ma duk baya baya muke da ita gaskiya, mu a zamaninmu idan mutum yayi cikin shege ma rataye kansa kawai yake ya mutu, ko kuma ya gudu ya bar garin sai bayan shekara hamsin, to ita kinga ai taki yin ko daya” Bude kofar parlon aka yi Ammi ta shigo da breakfast ta kawo ma Mayraah, ko bata bude baki tace komai ba kasan tana cikin farin ciki mara misaltuwa, she looks so happy wanda duk wanda vasanta vasan rabonta da wanna farin cikin an kwana biyu, Usman really took she and Maheer unaware don duk abinda yake yi bai gaya masu ba, Mama Ladi ta bi ta da kallo har ta ajiye tray din hannunta tana kallon Mayraah tace “Taho ki karya daughter” Mama Ladi ta rike haba tace “Yanzu tun safe in tashi ko ruwan shayi da ke da shegiyar sabuwar me aikinki baku bani ba sai wanna mata da bamu san daga inda take ba zaki kawo ma tray guda na kumallo jikinki na bari? Ni da na kwana gidan baki ban komai ba sai warce bata kwana ba?” Ko kallon Mama Ladi Ammi bata yi ba sai ma daukan tray din da tayi ta wuce dakinta da shi tace “Taho Mimi” Mayraah da duk jikinta yayi sanyi da halin da Badiyyah ke ciki ta share hawayen idonta ta bi bayan Ammi tana tafiya a hankali zuwa bedroom dinta. Ammi da kanta ta hada mata shayin ta debar mata komai sannan ta koma ta zauna tana kallonta, Mayraah ta daga kai tace “Ammi Abba fa?” A hankali Ammi tace “Na kirasa yana hanya” Mayraah ta dau shayin da Ammi ta hada mata ta fara sha, Ammi ta mike ta fita daga dakin zata je kai ma Mama Ladi nata breakfast din, Ammi na fita babu dadewa Maheer ya shigo dakin, Mayraah ta daga kai tana kallonsa har ya iso inda take ya duka yana kallonta, ta sauke idonta tace “In hada maka shayin kai ma?” Ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace “Ki rage min kawai” Tace “Sai mu sha tare…” Zaunawa yayi saman darduman yana facing dinta, bayan ta kurbi shayin hannunta ta mika masa, ya amsa ya kai baki, ita kuma ta fara cin irish din da Ammi ta zuba mata da ketchup da kwai, Ya ajiye cup din shayin bayan ya sha a hankali yace “Me yasa kika tafi Mimi?” Bata yarda ta dago kai ta kallesa ba cikin sanyin murya tace “That’s bygone yayana” Ya gyada mata kai kawai still looking at her, bayan few seconds tace “Baza ka ci irish din ba?” Dauka yayi ya fara ci, ta dau cup din shayin ta sha kadan ta ajiye, daga kai tayi suka hada ido, yace “I missed you Mimi” Ta dan yi
ma Mayraah, ko bata bude baki tace komai ba kasan tana cikin fa ( ciki mara misaltuwa, she looks so happy wanda du’ wanda vasanta yasan rabonta da wanna farin cikin an kva.a biyu, Usman really took she and Maheer unaware don duk abinda yake yi bai gaya masu ba, Mama Ladi ta bi ta da kallo har ta ajive tray din hannunta tana kallon Mayraah tace “Taho ki karya daughter’ Mama Ladi ta rike haba tace “Yanzu tun safe in tashi ko ruwan shayi da ke da shegiyar sabuwar me aikinki baku bani ba sai wanna mata da bamu san daga inda take ba zaki kawo ma tray guda na kumallo jikinki na bari? Ni da na kwana gidan baki ban komai ba sai warce bata kwana ba?” Ko kallon Mama Ladi Ammi bata yi ba sai ma daukan tray din da tayi ta wuce dakinta da shi tace “Taho Mimi” Mayraah da duk jikinta yayi sanyi da halin da Badiyyah ke ciki ta share hawayen idonta ta bi bayan Ammi tana tafiya a hankali zuwa bedroom dinta. Ammi da kanta ta hada mata shayin ta debar mata komai sannan ta koma ta zauna tana kallonta, Mayraah ta daga kai tace “Ammi Abba fa?” A hankali Ammi tace “Na kirasa yana hanya” Mayraah a dau shayin da Ammi ta hada mata ta fara sha, Ammi ta mike ta fita daga dakin zata je kai ma Mama Ladi nata breakfast din, Ammi a fita babu dadewa Maheer ya shigo dakin, Mayraah ta daga kai tana kallonsa har ya iso inda take ya duka yana kallonta, ta sauke idonta tace “In hada maka shayin kai ma?” Ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace “Ki rage min kawai” Tace “Sai mu sha tare…” Zaunawa yayi saman darduman yana facing dinta, bayan ta kurbi shayin hannunta ta mika masa, ya amsa ya kai baki, ita kuma ta fara cin irish din da Ammi ta zuba mata da ketchup da kwai, Ya ajiye cup din shayin bayan ya sha a hankali yace “Me yasa kika tafi Mimi?” Bata yarda ta dago kai ta kallesa ba cikin sanyin murya tace “That’s bygone yayana” Ya gyada mata kai kawai still looking at her, bayan few seconds tace “Baza ka ci irish din ba?” Dauka yayi ya fara ci, ta dau cup din shayin ta sha kadan ta ajiye, daga kai tayi suka hada ido, yace “I missed you Mimi” Ta dan yi murmushi tace “I missed you more” A haka Ammi ta shigo dakin ta samesu, Ammi na kallonsa tace “Ba ga can naku an kai maku ba?” Mayraah ta kalleta tace “Ammi nice nace ya ci”‘ Shi dai murmushi kawai yayi, Ammi ta zauna gefen gado still looking at them.
Mayraah na gama yin breakfast ta shiga yin wanka bandakin Ammi, Maheer kuma ya fita da tray din da suka yi breakfast din downstairs zuwa kitchen, ko da ta fito wanka ta tarar Ammi ta dauko mata kaya daga dakinta ta ajiye mata gefen gado, bayan ta shafa mai ta shirya ta fito parlor, har a sannan Badiyyah na parlon Ammi a kwance ita kadai, Mayraah na tafiya a hankali ta karasa kusa da ita ta durkusa tana kallonta tace “Ya jikin?” Kai kawai Badiyyah ta gyada mata, Mayraah tayi shiru tana kallonta hawaye na taruwa idonta, abubuwan da suka faru a baya ne da dalilin faruwansu kawai ke yawo mata a zuciya, da sauri ta goge idonta trying to shun away the thoughts off her mind, cikin sanyin murya tace “Kin yi breakfast ai ko?” Nan ma Badiyyah ta gyada mata kai tana kallonta, wani tausayinta Mayraah ta dinga ji har cikin ranta, she can’t just imagine Badiyyah da ta sani ce wannan, a whole Badiyyah, Ammi ce ta shigo parlon, Mayraah ta juya tana kallonta, tana tsaye bakin kofar tace “Fito ki je wajen Abbanki Mimi, he is around” Mayraah ta mike tana goge wasu hawayen dake taruwa idonta ta nufi Ammi, a tare suka sauka downstairs, Mayraah na hada ido da Abba dake zaune kan kujera ya mike tsaye yana kallonta, sosai jikinta yayi sanyi ta sunkuyar da kanta and for the first time she felt guilty akan abinda ta aikata, for the first time ta ji bata kyauta abinda tayi ba, nan da nan hawaye ya cika idonta ta nufesa da sauri ta rungumesa sosai ta fashe da kuka tace “I am sorry Abba, don Allah kayi hakuri, i don’t know what came over me, i was….” Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai, Abba yayi patting din bayanta a hankali bai ce komai, tayi kukanta me isarta sannan ta durkusa nan gabansa cikin rawan murya tace “Don Allah ka yafe min Abba” Har a sannan ta kasa hada ido da shi, Abba ya zauna kan kujera a karo na farko yayi magana yace “It’s okay Daughter…. I am glad you are back home hale and hearty, that was our prayer and hope, Alhamdulillah” Ganin yanda take kuka ya shafa kanta yace “Nace ya isa haka my dear” Ta gyada masa kai tana goge hawayen dake sauko mata, gefensa ya nuna mata ta dawo ta zauna ta daura kanta a jikinsa, sai a sannan ta lura da mutanen dake zaune parlon, Mama Ladi ce dake ta taɓe baki tana hararanta sai Hajiya Amina dake ta kallon Mayraah tana murmushi, matar looks so happy da dawowar Mayraah, Mayraah ta kalli Abba ya gyada mata kai yace “Go and greet her” Mikewa tayi ta ɗan kalli direction din dining da ta hango Usman a zaune shi ma yana kallonta, ta karasa har gaban Hajiya Amina ta durkusa gabanta ta gaisheta, Hajiya Amina ta dago ta sitting her down by her side ta jawota jikinta tana amsa gaisuwar ta da fara’a, Ammi dai na tsaye stairs taki karasowa cikin parlon all her attention na kan Mayraah, Mama Ladi da take ganin abinda ake bai shafeta ba ta mike tana kallon Ammi tace “Ke har yanzu fa shegiyar me aikinki bata kawo ma bakuwar nan abinci ba, ko kafura ce mai aikin da bata san ance baƙon ka annabinka ba” Ammi bata tanka Mama Ladi ba, don dauke kai ma tayi, Hajiya Amina na murmushi tana kallon Mama Ladi tace “Ayya Mama nace mun yi breakfast kafin mu fito” Mama Ladi tace “Aa ko farfesun ne bari inje in debo maki da burodi mu bamu gaji rowa ba a pamilyn mu” Daga haka ta wuce kitchen da sauri, Ammi ta juya ta wuce sama Abba ya bi ta da kallo, Mayraah na son tashi daga kusa da Hajiya Amina ta bi Ammi amma sai ta kasa, gaba daya she is not comfortable sitting down with her, mikewa Abba yayi ya wuce sama. Sai kusan karfe sha biyu Hajiya Amina da Abba suka bar gidan har sannan kuma Ammi bata sauko kasa ba, sai upstairs Hajiya Amina ta tafi tayi mata sallama a part dinta, Mama Ladi kuwa babu wanda zai ce ba wajenta Hajiya Amina ta zo ba don babu labarin karaye da bata ba Hajiya Amina ba, saboda ita ne ma har Hajiya Aminar ta iya kai wa karfe sha biyu a gidan, tunda ita kadai ce downstairs sai Usman dake aiki da laptop dinsa a dining area. Mayraah ta shiga dakin Ammi bayan tafiyar Hajiya Amina ganinta kwance har a sannan ta zauna gefenta tana kallonta tace “Ammi ko dai baki da lafiya ne?” Ammi ta sakar mata murmushi tace “Aa kawai hutawa nake Daughter” Mayraah tace “Toh ba abinda za a kawo maki?” Ammi tace “Aa… i am okay” Shiru Mayraah tayi, tun dazu take zaune dakin da Badiyyah take kwance bayan Ammi tace ma Badiyyar ta koma can za a gyara mata part dinta, ita dai ta rasa wani irin tausayin Badiyyah take har cikin ranta, sai Mama Ladi ce ta zo ta kirata taje suyi sallama da Hajiya Amina tana mata mitar meye hadinta da Badiyyar zata ne ta makale mata kowa na baya baya da ita salon ta shafa mata wani cutar, ita dai Mayraah bata ce mata komai ba, bayan tafiyar Hajiya Amina ne ta hauro sama ta shigo part din Ammi, mikewa Mayraah tayi after some minutes, Ammi na kallonta a hankali tace “Anjima idan na tashi ki zo in gyara maki gashin ki” Mayraah tace “Toh Ammi” Fita tayi daga dakin ta koma dakin da Badiyyah take, Badiyyah na kallonta da kyar tace “Baƙin sun tafi? Ina son in je parlor na gaji da nan din” Mayraah tace “Eh sun tafi” Ita kanta Badiyyah yau ta ɗan samu sukuni tunda ba ayi neglecting dinta as always ba, yau gashi har ruwan wanka sai da Mayraah ta tara mata ta samu tayi wanka, hatta Ammi bata bi ta kanta a gidan iyaka ta ajiye mata abinci in ta ga dama ta ci, wanka ma idan ta ga dama taje ta tara ruwa tayi, sai kuma Maheer da ta saka yake bata medication shi ma yana ajiye mata magani yake fita, Mama Ladi kuwa sai dai bata kyallara ido ta ganta ba, munanan kalamu sai wanda ta manta ne bata sakar mata, hakan kuma ke sa Badiyyar kuka sosai taji kamar ta mutu ta huta kawai, yau kuwa tun da Mayraah ta dawo take by her side even if she is not saying anything to her, Mayraah tace “Sun tafi, za ki iya saukowa, ba kowa a parlon” Da kyar ta lallaba suka koma downstairs ta kwanta nan tsakar carpet, sabuwar mai aikin gidan ce ta kira Mayraah da ladabi tace “Hajiya ta hanata saukowa ta kwanta nan saboda baƙi masu shigowa fa” a hankali Mayraah tace “Ba jimawa zata yi a nan ba” Suna cikin magana Haseenah ta leko Parlon don tabbatar da Mama Ladi bata ciki kafin ta shigo, tana ganin bata parlon ta shigo zata kitchen ta debi abincin rana, dama yanzu ko gas bata kunnawa sai an girka a nan ta faki idon mama Ladi ta shigo ta diba tunda ba wai kanta ya gama healing bane ita ma har yanzu jinya take, tana kyallara ido taga Badiyyah ta fara wakar habaici tana taunar cingam wai wata tayi cikin shege don ta ci ragon suna…. Can kuma ta hango Mayraah wani matsiyacin kallo ta mata ta shige kitchen bata fasa wakar da take ma Badiyyah ba, Mayraah dai ta bi ta da kallo, ita dai Badiyyah dama ko kallon direction dinta bata yi ba don duk haduwar da za su yi da Haseenah a gidan wakar da take mata kenan, to tana fama da kanta ina taga ta kulata. Washegari wajen karfe goma na safe Mayraah ta tashi daga baccin da take, har ta mance rabon da tayi bacci peacefully kuma me tsayi haka, wanka tayi ta shirya sannan ta gyara ma Ammi dakinta ta fito parlor, Maheer ta gani zaune parlon shi kadai, ta karasa kusa da shi ta zauna kasa tace “Yaya ina kwana?” Yana kallonta yace “How was ur night?” Tace “Alhamdulillah” Yace “Kan ya daina ciwo?” Ta ɗan buda ido sannan ta cire dankwalin kanta don gashinta suka zubo kasa tace “Ya daina” Tun jiya da Ammi tayi mata kitson kalaba take complain din ciwon kai don ta dade bata yi kitso ba, hakan ma yasa ta kwanta da wuri jiya da daddare, yanzu kuma da ta tashi taji babu ciwon, yana kallon kitson nata yace “Yayi kyau” Murmushi tayi tace “Thank you, yaya result dinmu fa?” Sai bayan da tayi tambayar gabanta ya fadi sosai she can’t imagine her spilling, ya ɗan yi shiru yana kallonta, nan da nan hawaye ya cika idonta, yanzu gaba daya hawaye baya mata wahala nan da nan take hawaye, cikin rawan murya tace “I had issues ko?” Yace “Nasan tsohon saurayinki ya gaya maki ai” Har sannan gabanta na faduwa tace “Wallahi yaya A’a, babu ta inda zai yi accessing dina ya gaya min” Yace “Ai na zata kin ga result din naki tuntuni” Ta girgiza masa kai tayi narai narai da ido, yace “To bari in nuna maki, but….” Hankali tashe tace “But what yaya??” Yace “Promise me u will be calm ko me zaki gani, kuma ki gode Allah” Wasu hawayen ne suka taru idonta, yace “Toh shikenan” Da sauri ta goge idonta tace “I will be calm plss” Yace “Good, dawo nan” Mikewa tayi ta koma gefensa da ya nuna mata ta zauna sai tsuru tsuru take da ido, ya shiga WhatsApp dinsa ya nemo chat dinsa da Hamidah da ta turo masa result din, Mayraah da duk jikinta ke bari don bata san me zata gani ba ta rufe fuskarta da kujera, ya dubo result din da Hamidah ta turo masa sannan yace “Here….” Ƙin dagowa tayi tace “Kawai ka gaya min plss” Yace “Toh shikenan bari in ajiye wayar” Dagowa tayi da sauri ta amshi wayar cikin dakiya tana kallon screen din, wani kara tayi ganin pass, ta maida dubanta da sauri gun CGPA dinta kawai taga da first class dinta ta fita, ai bata san sanda ta rungumesa ba cike da farin ciki, ya ɗan buda ido yace “Ke… baki da hankali ne” She was soo happy ta zamo kasa tace “Alhamdulillah” Sai kuma tayi sujud shukr, yace “To abinda ya kamata kiyi kenan kike shirme” Mayraah ta dade bata yi farin cikin da tayi a moment din nan ba, amma fa can kasar zuciyarta tunanin ta yanda za ace ta fita da first class take, ita fa tasan abinda tayi a exams din, how comes Kuma ta fito da first class dinta still, but all the same she is soo Happy, mikewa tayi ta dawo gefen Maheer ta zauna tace “Yaya how about sis Badiyyah’s result?” Yace “She was expelled” Jikin Mayraah yayi sanyi tayi shiru tana kallon sa, shi ma kallonta yake, can ta sunkuyar da kanta, yayi kasa da murya yace “Je ki amso breakfast dinki” Mikewa tayi ta fita daga parlon ya bi ta da kallo. Bayan 4 days da dawowan Mayraah tana kwance dakin Ammi da rana wayarta ya fara vibrate, dubawa tayi taga Dr Khalil ne ke kiranta tunda ta dawo sau daya ya kirata sai yanzu kuma, dagawa tayi ta kai kunne tayi masa sallama, bayan ya amsa ta gaishesa, yace “Ya kike ya gida?” Tace “Alhamdulillah, ya Ashnaah da Ashfah” Yace “They are fine, kin koma gida kin mance mutane ko” Murmushi tayi tace “Aa ni ban manta ka ba….” Yace “Gashi nan ko hello babu” Tace “Ai bana son in kiraka ne saboda mom twins” Yace “I understand Mayraah, ya Umminki?” Tace “She is fine Alhamdulillah” Yace “Ranan ai Barrister ya hadani da ita mun gaisa” Tace “Da gaske??” Shiru Dr Khalil yayi saboda bude office dinsa da aka yi, ganin wanda ya shigo yace “I will call u back” Daga haka ya katse wayar ya ajiye, Files din hannunsa yayi dropping masa kan table yace “I will be flying to Adamawa later, attend to this files and submit them to me before evening” Dr Khalil yace “Ohk sir, zaka je wajensu Mama kenan” Bai ce masa komai ba yana duba wani textbook dake kan table dinsa, Shi dai Dr Khalil kallonsa kawai yake, after checking the textbook ya daga kai ya kalli Dr Khalil yace “At last ka hakura ka samar mata aikin a wani asibitin kenan, but i was surprise da naga baka yi resigning ka bi ta can ba” Dr Khalil yayi kamar bai gane maganar da yake ba yace “Wa kenan?” MD na kallonsa yace “Ka fi ni sani” Dr Khalil ya fashe da dariya yace “Wait!!! Are you trying to ask for her whereabout in disguise?” MD ya hade rai kafin yace komai Dr Khalil yayi saurin cewa “She is being sick, very sick, ko picking call bata yi…. Kuma as our boss ya kamata kai da any other Dr or Nurse including me mu je mu dubata, she is seriously sick, an tafi da ita kano gun iyayenta….” Juyawa MD yayi ya fita daga office din, Dr Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi. Bayan magrib Mayraah ta sauko downstairs ta shiga kitchen don dafa ma Ammi shayin da ta saba yi mata, bayan ta daura tea din ta zuba duk kayan kamshin da zata saka aka bude kofar kitchen din ta juya da sauri, ya shigo kitchen din suna hada ido tace “Ina yini” Bai sake kallonta ba yace “Lafiya lau” Rabonta da ganinsa tun jiya da safe, plate ya dauka zai debi abinci ta bi sa da kallo jin yanda yake wani kamshi tace “Yaya Maleeha fa?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Wacece haka?” Ta wara ido tace “Ita Maleehar ce baka sani ba?” Yace “Tuna min dai” Dariya ta fara yi sosai, ya juya yana kallonta tayi dariyar me isarta tayi shiru, still shi dai kallonta yake, tace “Kilan ma daga wajenta kake yanzu haka yanda naji kana kamshi shine kake min pretending” Yace “Haba” Ta kara kyalkyala dariya tace “I am sure” Yace “Aa sai dai ki rakani mu je yanzu” Da sauri tace “To don Allah mu je, bari inyi sauri in gama yi ma Ammi shayi sai in kai mata kafin nan ka gama cin abincin sai mu tafi” Yana kallonta ya mayar da abincin da ya fara diba a warmer yace “Sai mun dawo zan ci” Ta ɗan buda ido tace “Toh kaci ko kadan ne mana” Girgiza mata kai yayi without saying anything, tace “Toh bari in baka shayin Ammi kadan ka sha” Daga haka ta maida hankalinta kan shayin da take, shi dai yana tsaye yana kallonta, cikin few minutes ta gama dafa shayin ta dauko karamin tea cup da saucer dinsa ta fara zuba masa, sannan ta nufesa tana kallonsa kamar yanda shi ma yake kallonta, mika masa tayi a hankali tace “Here” taga bai amsa ba kuma kallonta yake, tace “Yaya” Sai da ta sake kiransa yayi saurin mika hannu ya karba, tace “Why are u absentminded? Tunanin me kake yi” Bai sake kallonta ba yace “Nothing, idan kin gama ina jiranki” Daga haka ya fita daga kitchen din ta bi sa da kallo, wani mug ta dauka ta zuba ma Ammi shayin bayan ta kashe gas din ta goge wajen ta fita daga kitchen din, tana ajiye ma Ammi shayin tace “Ammi gashi na gama” a hankali Ammi tace “Allah maki albarka” Mayraah tayi murmushi ta mike tace “Ammi zan raka ya Usman wajen wata frnd dinsa yanzu” Ammi ta kalli agogo tace “Frnd kuma?” Dariya tayi tace “Eh” Ammi tace “Toh sai kun dawo amma plss kar ku jima dare yayi” Hijab Mayraah ta shiga dakin Ammi ta dauka, sai da ta fara shafa turare a jikinta, har ta mance rabon da tayi amfani da wannan special turaren nata tun kafin a fasa aurenta ta daina amfani da turaren sai yau kuma da ta daukosa cikin kayanta, bayan ta gama shafa turaren ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita tayi ma Ammi sallama, sai da ta fara shiga dakin da Badiyyah take ta sameta tana bacci, abincin da ta kawo mata ma kadan ta samu ta ci, Mayraah ta rufe sauran sannan ta fita downstairs, zaune ta tadda Usman a parlon yana jiranta ga tea cup din da ta zuba masa shayi ya sha rabi ya ajiye sauran, tana kallon sauran shayin a hankali tace “Yaya bai maka dadi bane?” Yana kallonta yace “Yayi” Tace “To naga baka shanye ba” Yace “Ya isa” Karasawa tayi ta duka gabansa ta dau sauran shayin ta wuce kitchen ya bi ta da kallo, Mayraah na shiga kitchen din ta shanye sauran shayin ta wanke cup din da sauce ta ajiye inda sauran suke sannan ta fito, tana kallonsa tace “Yaya mu je” Mikewa yayi ya nufi kofa ta bi bayansa. Suna fita compound din bayan sun bar anguwan taji yace “Kar ki sake saka turaren da kika saka yanzu” Mayraah ta juya tana kallonsa da mamaki, can tace “Saboda me yaya?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Kar ki sake kawai nace” shiru tayi bata ce komai ba, bata ce masa komai ba, ita dai tana ta zuba ido ta ga ta inda za su billo gidansu Maleeha tunda ta san gidan kuma taga sun wuce hanyar gidan, bayan sun yi nisa sosai da anguwan ta kasa daurewa ta juya tana kallonsa tace “Yaya sun tashi ne daga gidansu?” Yace “Ehh” Tace “Ayya, i was wondering naga mun wuce unguwan tun dazu” Ya juya ya kalleta yace “Kin taɓa zuwa ne?” Ta zaro ido tace “Gaya min fa tayi” Yace “Ohk” after almost 30mins ride ta gansu a wani anguwa na masu shegen kudi, ta dinga bin manyan gidajen da kallo har taga yayi horn bakin wani gate mai gadi na lekowa ya gansa ya buda gate din ya shiga yayi parking yana kashe motar ya sauka, Mayraah ma ta sauka ya kulle motarsa, ganin ya nufi entrance din gidan da sauri tace “Yaya ba kiranta zaka yi ba tukun” Yace “Na kirata ai” Bin bayansa tayi har suka iso kofar shiga cikin gidan, Mayraah was shock ganin Hajiya Amina ta bude masu kofa, da fara’a take masu sannu da zuwa, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, da tasan nan Ya Usman zai kawota da babu abinda zai sa ta biyo sa, haka nan dai ta zauna kan kujera ta gaisheta, Hajiya Amina ta amsa da murmushi tana tambayarta Ammi Mayraah bata dago kanta ba tace “Tana nan lafiya” Hajiya Amina ta kalli Usman tace “Kwana biyu shiru baka billo ba Barrister” Sai kuma da sauri tace “Au na tuna Yallabai yace min kaje kaduna, to ya aikin?” Yace “Alhamdulillah” mikewa yayi yace “Zan shiga masallaci inyi sallah” Tace “Toh shkkn” Daga haka ya fita parlor zai tafi masallacin dake jikin gidan daga gefe wanda Abba ya gina, Hajiya Amina na kallon Mayraah tace “Mu je Abban naki na sama a parlor ki gaishesa” Mayraah ta mike har a sannan fuskarta babu wani walwala ta bi bayanta zuwa upstairs, Abba yayi farin cikin kawo Mayraah da Usman yayi, dama yana ta son ce ma Ammi a kawota gidan ko yini ne tayi amma ya bar ma zuciyarsa don bai san yanda Ammi zata dau batun ba, liyafar abincin da Hajiya Amina ta ajiye masa ya zuba masu tare da Mayraah, Hajiya Amina tace “Je ki ga ko yayan naki ya dawo masallaci ya zo ya ci abinci” Mikewa Mayraah tayi ta fita daga dakin ta sauka downstairs, Zaunawa tayi kan kujera ganin Usman bai shigo ba, bayan some minutes sai ga shi ya shigo parlon, ta tashi tana kallonsa tace “Yaya wai kaje sama inji Abba, pls yaya kana gama cin abincin ka maida ni gida plsss don Allah” Sosai ta marairaice masa don har ga Allah gida kawai take son ta ganta, Yace “Nan din ba gida bane?” Ta wani hade rai tace “Ni dai pls mu tafi gida” Sama ya wuce ta bi bayansa har zuwa parlon Abba, kusan duk bayan kwana biyu sai Usman ya zo gidan sai in baya gari, Maheer ne dai tun ranan da Abba ya kirasa ya zo bai sake bin hanyar gidan ba har yau, Da kyar Mayraah ke cin abincin da Abba ya zuba masu, Hajiya Amina na zaune parlon tana kallon TV, har daga karshe Mayraah ta mike tace ta koshi, Hajiya Amina tace “To mu je kiyi sallan isha” Babu yanda Mayraah ta iya haka ta mike ta bi bayanta suka fita parlon zuwa part dinta, bayan tafiyarsu with few minutes Usman ya ajiye spoon din hannunsa, Abba yace “Are you satisfied” Usman bai yarda ya kallesa ba, kansa na kasa yace “Sure… dama Abba akwai maganar da nake son zan yi maka” Abba na kallonsa yace “Ohk, i am all ears barrister” Ganin yayi shiru kamar me tunanin ta inda zai fara maganar Abba yace “Ina jin ka Usman, tell me what is it” Usman ya daga kai a hankali ya kalli Abba…..
Shiru Abba yayi yana ta kallon Usman, can ya ɗan yi murmushi yace “Did you say this to anybody? I mean did u discuss it to anyone?” Usman ya girgiza masa kai without looking at him, Abba ya sauke ajiyar zuciya, bayan few seconds yace “Not even her?” Usman yace “Eh” Abba na gyada kai yace “Gaskiya nayi farin ciki da wannan batun Usman, i am so happy about it, and this is what i wished for few months back, but….” Usman ya daga kai ya kalli Abba, calmly Abba yace “I want u to let ur intentions be known to her before anything….” Usman ya girgiza kai da sauri yace “Abba kawai ba sae nayi hakan ba, kawai dai…” Sai kuma yayi shiru, Abba yace “You have to Usman, kwanaki i wasn’t willing to give her an alternative cause tunanina hakan kadae ne mafita gare mu da ita baki daya, and i understand you too then da kayi declining… But yanzu i don’t think i will do anything without her consent, say ur mind to her, go on a courtship with her….” Kallon Abba kawai yake baya ko kifta ido, Abba jinjina masa kai giving him assurance yace “Ko nan da sati daya ne in dai da consent dinta you gat my back son” Usman bai iya yace komai ba ya sauke kansa, Abba dai sae kallonsa yake, bude kofar parlon aka yi Mayraah ta shigo da sallama, Abba ne kawai ke kallonta, Usman kam bai daga kai ba, har ta karaso ta zauna gefensa tana kallonsa tace “Yaya na gama mu tafi gida” Abba yace “Nan din ba gida bane?” Ta kallesa ta ɗan yi murmushin karfin hali tace “Abba ae ban ce ma Ammi zamu kwana ba shi yasa” Abba ya gyada kai yace “Toh in kin ce mata sai ki zo kiyi weekend a nan din” Mayraah dai bata ce komai ba ta mike tana kallon Usman tace “Yaya Ammi fa tace kar dare yayi sosai” Sai a sannan ya daga kai ya kalleta yace “To ba yanzu zan tafi ba” Ta marairaice tana kallonsa, mikewa Abba yayi yace “Naga ko karfe tara bai karasa ba ai Mimi, so there is still time, bari inje inyi sallah” Fita yayi daga parlon, Mayraah ta zauna kusa da shi kamar zata yi kuka tace “Yaya pls kaga dai Ammi bata san za mu zo nan ba ko, kuma ce min kayi wajen Maleeha fa za mu je, ni dai ka tashi mu tafi gida don Allah” jin yayi shiru ta ɓata fuska tace “Ka ji mana yaya” Sai a sannan ya juya ya kalleta yace “Nan din daji ne?” Ta turo baki ta koma ta jingina jikin kujera tana kallonsa fuskarta a daure, har bayan minti sha biyar bai ce mata ba, ita ma bata ce masa ba a parlon, lkci lkci take turo baki duk yana lura da ita, can ya mike tsaye, tana ganin haka ita ma ta tashi, ya kalleta yace “Ke a nan fa za ki kwana” Ko rufe baki bai yi ba tace “Wallahi bazan kwana ba” Tana fadin haka ta nufi kofa yace “Kar ki fita” Dawowa tayi tana kallonsa kiris ya rage ta fashe da kuka, ya koma ya zauna kan kujera, a hankali yace “Now tell me, me yasa baza ki kwana nan ba?” Ta zauna kasa daga gefensa tace “Kawai wajen Ammi zan tafi” Jin bai ce komai ba ta daga kai suka hada ido, tace “Pls mu tafi yaya” Hajiya Amina ce ta shigo parlon tana kallon sauran abincin da ba a taɓa ba tace “Ka ci abincin kuwa barrister?” Yace “Eh na ci, za mu tafi ne” Hajiya Amina tace “Ina ce ai a nan Mayraah zata kwana” Usman yace “Bata zo da shirin kwana ba” Hajiya Amina tace “Toh shikenan, ko weekend ne sai ta zo” Mayraah ta sauke wani ajiyar zuciyar relieve sanda taga sun bar gidan. Sai da suka yi nisa sosai ta kallesa tace “Yaya baza mu siya ma Ammi Apples da watermelon ba?” Yace “Ok za ki siya mata?” Tayi er dariya tace “I am not together with my Atm?” Ya ɗan kalleta yace “Nawa za a ara maki?” Ta langwabar da kai tace “Like 10k” Yace “Ohk” gun da ake siyar da fruits yayi parking ta juya ta kallesa tana jiran ya bata kudin taje ta siyo, bude motar yayi ya sauka ta bi sa da kallo, bayan wasu mintuna ya dawo ya ajiye mata ledan kan kafarta yace “15k, sai ki biya yaushe?” Dariya tayi tace “Muna isa gida” Yace “Alright” Suna isa gida bayan yayi parking ta bude motar ta sauka ta jira shi ma ya sauka, bayan ya rufe motar ya jingina jiki folding his arms yace “Mun iso gida” Bata san sanda ta fashe da dariya ba tace “Yaya ko ciki fa bamu shiga ba” Yace “Toh” Daga haka ya nufi cikin gidan, ta bi bayansa tana murmushi, suna shiga parlor Maheer kadai ne zaune yana danna wayarsa, sau daya Usman ya kallesa ya wuce sama, Mayraah na ganin Maheer ta nufi kujeran da yake ta zauna kasa ta ajiye ledan hannunta tana kallonsa tace “Ina yini yaya” Yace “Ina ku ka je?” Ta buda ido tace “Yaya ce min fa yayi wajen budurwarsa zai je shine ya kai ni Miller road, ashe wajen Abba zai je” Maheer ya maida dubansa kan waya yace “Ohk” Tace “Yaya ka ara min 15k cash pls” ya kalleta yace “Me za ki yi da 15k?” Tana murmushi tace “Just borrow me pls” Yace “Sai ki maida yaushe” Dariya ne ya taho mata tace “Gobe da safe” Yace “Ohk, mu je in baki” yana fadin haka ya mike, tashi tayi ita ma ganin ya nufi kofar fita tace “Aa yaya zan jira a nan ka kawo min pls” Ya juya yana kallonta yace “Why?” Shiru tayi bata ce komai ba, ya karasa kusa da ita, still looking at her yace “Why?” Ta sauke ajiyar zuciya tace “I am not going there because of ur wife” Yace “Do not call her my wife again Mimi, Haseenah is not my wife” Ita dai bata ce komai ba, yace “Mu je” a hankali ta fara tafiya tana biye da shi a baya, sai da suka iso chalet din tace “Amma bazan shiga ba, i will wait outside Yaya” Tana fadin haka ta tsaya dai dai stairs din chalet din, shi ma bai yi forcing dinta ta shiga ba, yana bude kofa Haseenah dake zaune kan kujera tana waya ta katse wayar tana goge hawayen idonta tana kallonsa, ko kallonta bai yi ba ya bar kofar a bude ya wuce daki, kamshin turaren da ta dinga ji na shigowa parlon ya sa ta mike ta taho bakin kofa don jikinta ya bata da mutum a wajen, tana ganin Mayraah bata bari sun hada ido ba ta koma inda take ta zauna, ba a dau lokaci ba Maheer ya fito da cash din a hannu, ya mika ma Mayraah ta amsa tace “Thank you Yaya” Shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, ta juya ta sauka daga chalet din ta koma main building din gidan da sauri, ledan fruits din ta dauko sai da ta fara zuwa dakin Usman tayi knocking ya bude kofar ganinta ya koma ciki ya zauna, ta bi bayansa tana murmushi tace “Ga kudin” Amsa yayi ya ajiye gefensa, ta juya ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Washegari Mayraah na idar da sallan asuba bayan ta gama azkar ta shiga dakin da Badiyyah take, zaune ta sameta kasa, Mayraah ta zauna tana kallonta tace “Ya jikin?” Badiyyah ta gyada mata kai, Mayraah tace “In kawo maki kunun ko shayi” Badiyyah tace “Ko wanne” Mikewa Mayraah tayi ta fita, Bangaren Ammi ta fara tafiya don ta gaisheta, tana shiga ta tadda Mama Ladi na minshari kan darduman da tayi sallah, dakin Ammi ta karasa tayi sallama, Ammi ta amsa mata, ta shiga dakin… Maheer na zaune gefen Ammi, ita kuma tana zaune kan darduma, Mayraah ta duka kusa da Ammi ta gaisheta, Ammi tace “Kin tashi lafiya” Mayraah tace “Alhmdlh” Kallon Maheer dake kallonta tayi tace “Ina kwana yaya” Yace “Lafiya lau” Mikewa tayi tace “Zan dawo Ammi” Daga haka ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, sai kuma ta kalli Maheer a hankali tace “We will continue later Maheer” Bai bari sun hada ido ba yace “Ohk” daga haka ya mike ya fita daga dakin. The next day friday Mayraah na dakin Badiyyah da yamma Mama Ladi ta shigo, Mama Ladi tayi tagumi daga tsayen da take tace “Naga abinda ya isheni ni Ladiyo, Wato ke dai Mera baza ki ji shawaran da nake baki ba ko? Baki da aiki sai makale ma wannan mata kamar almajira, nace ki fita hanyarta kiyi ta kanki kin ki, me yasa kike cusa kanki a abinda bai shafeki bane? yarinyar da kowa yasan ba sonki take ba tun asali, yarinyar da saboda ita kiri kiri aka fasa aurenki da ɗan matsiyatan can, ko ke baki lura alhakinki ke bin ta ba? Ko wani me ciki za ki ganta fes fes gwanin sha’awa amma Badiyyah kamar sabuwar almajirar kana rod dake garin kaduna, ke ko don kar kije ki shaƙi wata cutar baza ki kama kanki daga zuwa inda Badiyyah take ba? To ni dai ba ruwana Mamuda na kiranki, yana can parlon Ammi yace ki je” Daga haka Mama Ladi ta fice daga dakin tana toshe hanci, Mayraah ta kalli Badiyyah da hawaye ya cika idonta, kasa ce mata komai tayi amma har cikin ranta bata son abinda Mama Ladi ke yi ma Badiyyah a gidan, abun yayi yawa, mikewa tayi ta fita daga dakin ta tafi bangaren Ammi, Abba na zaune parlorn Ammi, Ammi kuma na ta harkan gabanta, Mayraah ta zauna ta gaida Abba, Abba ya amsa yace “Anjima Usman zai kai ki can gidan Hajiya Amina kiyi weekend, mai aikinta bata nan” Sai a sannan Ammi ta juya ta kalli Abba, Mayraah dai ta kasa cewa komai tana kallon Abba, Abba yace “Sai ki dau kayan da za ki tafi da su” Ammi na kallon Abba cikin karfin hali tace “Mamuda kawai fitowa za kayi kace min kana son ta koma gidan matarka, ba sai ka yi wani corner corner ba, just go straight to the point” Mayraah ta sunkuyar da kanta lokaci daya har hawaye ya kawo idonta, Abba na kallon Mayraah yace “Tashi ki tafi kiyi abinda nace maki” Mayraah ta mike ta juya ta nufi kowa hawayen dake makale idonta ya zubo fuskarta ta fita daga parlon, sai a sannan Ammi ta fashe da kuka ta nufi dakinta, Abba ya bi ta da kallo, sai kuma ya tashi ya bi bayanta, kuka sosai ya sameta tana yi, ya zauna gefen gado yace “Kin ga, babu ta yanda za ayi kice zan raba ki da Mayraah, Mayraah is staying there for just 2 days ta dawo nan…” Cikin kuka Ammi ta katse sa tace “To ban amince ba Mamuda, kuma bazan taɓa amincewa ba, babu inda Mayraah za ta je ai ba wani ɗan iskan ya rainan min ita har zuwa yau ba, ba wani ya sha min wahalanta ba, ba wani ya….” Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai zuciyarta na mata zafi tace “Mamuda kar ka sa inji ina dana sanin aurenka, abinda ban taɓa yi ba sai yanzu da aurenmu ya doshi shekaru arba’in, wahalan da na ci a gidanka da irin sadaukarwa ta da abinda zaka biya ni kenan? Is this what i deserve Mamuda? Is this how to pay me? Ko me zan maka na cancanci haka? Me yasa zaka yi saurin mance halacci na gareka? After all my sacrifice yanzu wata from no where zata zo ta fi ni ƙima da mutunci a idonka, wata ce zata zo tayi reaping where she never sowed, ban taɓa zaton haka daga gareka ba Mamuda, kuma a duk zaman mu in dai na cuceka….” Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai ta mike ta bar masa dakin kawai, ya sake tashi ya bi ta parlor. Mayraah na dakinta bayan ta ci kukanta Abba ya kwankwasa kofar ya bude, mikewa tayi daga zaunen da take tana kallonsa, Abba yace “Dauko kayanki” Yana fadin haka ya bar bakin kofar, jikin Mayraah yayi sanyi sosai, fitowa tayi daga dakin ta tafi bangaren Ammi, a bedroom dinta ta sameta, Mayraah ta karasa kusa da ita ta zauna ta ma rasa abinda zata ce, Ammi tayi karfin halin cewa “Ki je kiyi yanda Abbanki yace Mayraah” Mayraah ta fashe da kuka tace “Ammi ni bana son in je gidan” Ammi tace “Ran sunday za ki dawo in sha Allah, in ma ba a dawo dake ba zan sa Maheer yaje ya dauko ki, be a good girl kije ki dau kayanki kala biyu” Kuka kawai Mayraah take, Ammi tace “Tashi ki je my dear” Mikewa tayi tana goge hawayen idonta ta tafi ta dau kayan nata kala biyu a karamin jakanta, tana dawowa bangaren Ammi ta tadda Abba a parlon, hakan ya sa ta juya ta fita ta sauka downstairs kawai, bayan kusan minti sha biyar Abba ya sauko yace “Je ki mata sallama ki zo mu tafi, i don’t want go miss my flight” A hankali Mayraah ta mike ta wuce sama zuwa part din Ammi, a parlor ta sameta still a zaune, Mayraah ta zauna kasa tana kallonta cikin sanyin murya tace “Ammi don Allah kiyi hakuri…” Sai kuma ta fashe da kuka, Ammi ta dafa kanta tace “Kar ki damu daughter, u are not to be blame, ba komai, ranan lahadi Maheer zai je ya dauko ki” Mayraah ta gyada mata kai hawaye na sauka idonta, Ammi tace “Tashi ki je, idan yayi dropping dinki airport zai wuce” Mayraah ta mike tana goge hawayenta ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo tana kokarin ganin hawayen da ya taru idonta bai zubo mata ba, Sai da Mayraah ta fara shiga dakin da Badiyyah take, ta duka gabanta tace “Zan je Miller road” Da sauri Badiyyah ta mike zaune ganin jakar hannunta cike da karfin hali tace “Yaushe za ki dawo?” Tana fadin haka hawaye ya cika idonta, Mayraah ta kwantar da murya tace “On Sunday in sha Allah, ba dadewa zan yi ba” Kai kawai Badiyyah ta gyada mata hawaye na sauka idonta, Mayraah ta mike ta fita daga dakin duk jikinta yayi sanyi. Suna isa gidan a waje Abba yayi parking suka shiga ciki, Hajiya Amina tayi farin cikin ganin Mayraah sosai, ganin yanda ta makale bakin kofa tace karaso ciki mana, sai a sannan ta karasa ciki ta xauna, sallama kawai Abba yayi ma Hajiya Amina, tayi amsa addu’an Allah ya tsare ta rakasa har compound ita dai Mayraah na zaune kan kujera makale da jakarta, sabon drivern da Abba ya dauka a gidan shi yayi driving dinsa zuwa airport, Hajiya Amina ta dawo parlor tana kallon Mayraah tace “Tashi mu je ki ga dakin ki” Mikewa Mayraah tayi ta bi bayanta suka tafi sama, Hajiya Amina ta bude mata dakin tace “This is ur room” Mayraah ta dinga kallon dakin ganin tsadaddun furnitures din ciki kamar dakin amarya, sauke kanta tayi kasa ta karasa cikin dakin. Bayan isha Mayraah na daki tana kokarin dialing number Dr Khalil saboda miss calls dinsa da ta gani Hajiya Amina ta shigo, hakan yasa ta fasa kiran, zaunawa gefen gadon Hajiya Amina tayi tana kallonta tace “Abincin ya isheki?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Na koshi” Hajiya Amina tace “To maa sha Allah, ya kika baro su Amminku?” Mayraah tace “Lafiya lau, tana gaisheki” Hajiya Amina tace “Ina amsawa, chatting kike ne” Mayraah ta girgiza mata kai tace “Aa” Hajiya Amina tayi murmushi tace “To yanzu waye surkin namu ne?” Mayraah ta ɗan kalleta sai kuma ta sunkuyar da kai, Hajiya Amina na murmushi tace “Feel free to talk to me dear, i am also ur mother” Mayraah ta ɗan kirkiri murmushi da kyar tace “Aa ba kowa” Hajiya Amina tace “Are you sure?” Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina tayi shiru tana kallonta, can a hankali tace “Ni kuma kin san wa nake maki sha’awa Mayraah?” Mayraah ta daga kai ta kalleta ba tare da ta shirya yin hakan ba, Hajiya Amina tayi kasa da murya tace “Yayanki” Mayraah dai ta dinga kallonta tana imagining wani yayan take nufi har ranta bata kawo su Maheer ba fa tunda ita dai tasan ba aure tsakaninsu a mentality dinta, Hajiya Amina tace “Kin ga ya san halinki, ya san wacece ke, kema kuma kin san halinsa kilan har littafi sai ki iya rubutawa akan halayyarsa, you 2 will make a perfect couple Mayraah, beside he is a calm and gentleman” Mayraah ta sunkuyar da kai feeling uncomfortable with the conversation, har cikin ranta bata san wani yayan take nufi ba fa ita, Hajiya Amina tace “Kin dai ga abinda ya faru akan aurenki kwanaki, so hakan kadai shine rufin asirinmu gaba daya” Hajiya Amina ta kalli wayar hannunta dake ring ta mike tace “Bari in amsa waya” Daga haka ta nufi kofar Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita…
Wajen karfe goma Mayraah na kwance sai juye juye take, har a lokacin maganganun Hajiya Amina sun kasa fita daga ranta, tayi kokarin gano wani yayan nata take nufi amma taki bari zuciyarta ya kai tunanin ta kan brothers dinta she just believe ba su bane and she is sure of that, wayarta ne ya fara vibrate, ta jawo a hankali tana kallon me kiran, Dr Khalil ta gani da kamar bazata daga ba sai kuma tayi picking ta kai kunne, gaisawa suka yi yace “Ina kika shiga yau baki picking call?» A hankali tace “Bana jin dadi ne” Yace “Subhanallah, what’s wrong with you?” Tace “Kawai kamar zazzabi ne” Yace “Allah ya sauke” Tace
“Ameen thank you” Yace “Dama za mu shigo kano gobe, kinga if it’s okay we can come over mu duba ki kafin mu koma Abuja” Mayraah tayi shiru, can tace “Kai da wa?” Yace “Dr Balogun da Hamid, mun shigo wani program ne” Mayraah tace “Toh shikenan Allah ya kai mu” Yace “Ameen, Allah ya kara lafiya” Tace “Ameen Nagode sosai’ Yace “Kinsan Ceo din ma ta koma tun last week but nan da few days zata shigo saboda workshop da za ayi” Mayraah tace “Ohk, Allah ya kai mu” Yace “Ameen, till tomorrow, in mun shigo kafin zan kira ki in sha Allah” Tace “To a gaida min twins” Yace “Za su ji” Daga haka ya katse wayar, mikewa zaune tayi tana tunanin yanda zata samu gobe ta koma gida wajen Ammi in ma Dr Khalil za su zo gwara suje can din su sameta a gidansu, don ita dai tasan nan ba gidansu bane, wayarta ta sake daukowa tayi dialing number Maheer, yana fara ringing ya daga a hankali tace “Yaya” Yace “Mimi” tace “Good evening” Yace
“So u still have my digit” Tayi murmushi kamar yana ganinta, yace “To ya aka yi?” Tace “Yaya plss i want to come back home tomorrow” Yace “Da gobe da jibi duk daya ne Mimi, just be patient, or is there any problem?” Ta girgiza kai tace
‘I am not comfortable” shiru yayi, sae kuma yace “Kiyi hakuri ki bari har jibin sae ki dawo gida kar Abba yayi fushi” Bata sake cewa komai ba, yace “Are you there?” Cikin sanyin murya tace “Na ji” yace “Good gal” Tace “Zan kwanta” Yace
“Ohk sleep tight, kin ci abinci?” Ta gyada masa kai vace “To sai da safe” katse wayar tayi ta ajiye ta rufe ido. Washegari da yamma Mayraah na kitchen tana girkin da Hajiya Amina ta sa tayi masu, two ne da vegetable soup tace tayi,
Mayraah har ta mance rabon da tayi girki, bata fito kitchen din ba sae kusan karfe biyar bayan ta gama komai, zaune taga Usman parlor, ta dan buda do tace “Lah yaya yaushe ka zo?” Ya kalleta sannan ya ci gaba da danna wayarsa yace “Now” tace “Ina yini” yace “Lafiya lau” Tace “Ya Ammi fa?” Yace “She’s fine” tace “In kawo maka tuwon na gama” Yace “Na ci abinci “Na ci abinci a gida” tace “Ohk” karasowa cikin parlon tayi tana kallonsa ta zauna gefensa tayi murmushi tace “You look cute” ya daga kai ya kalleta yace “Really” ta gyada masa kai still looking at him, yace “Ke ma”ta zaro ido tace “Nima me?” Yace “Abinda kika ce min” ta kyalkyale da dariya tace
“Ae ka fi ni kyau, shi yasa Maleeha take ji da kai” shi dai kallonta kawai yake, sai kuma ya kamo hannunta calmly yace “Ke kuma kin fi Maleehar kyau ai” Mayraah tayi shiru jin abinda yace, Ikci daya ya saketa ya ciro wayarsa zai fara dannawa, tayi kasa da murya tace “Yaya don Allah in zaka tafi zan iya bin ka?” Yace “Abba yace sai gobe” Hajiya Amina ce ta sakko downstairs gain Usman tace “Yaushe ka shigo barrister?” Yace “Yanzu” mikewa Mayraah tayi Hajiya Amina tace “Har kin gama girkin kenan?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Na gama” Hajiya Amina tace “To Sannu da aiki” Mayraah ta dan yi murmushi ta wuce sama Usman ya bi ta da ido, Hajiya Amina ta karaso ta zauna tana kallonsa tace “Ya gidan?” Yace
“Alhamdulillah” Mayraah na shiga daki ta dau wayarta taga kiran Dr Khalil har uku an hour ago, zaro ido tayi don ta mance yace mata za su zo yau, kiransa ta fara yi, yana fara ring ya daga yace “Bacci kike ne?” Tace “Aa ina kasa ne, ina yini?” Yace
“Lafiya lau, ya jiki?” Tace “Alhmdh naji sauki” vace “Ba don an daga flight dinmu ba ae kilan da yanxu muna Abuja, sae 8pm Flight din, so now…. ina ne anguwan naku?” Ta dan yi shiru sae kuma tace ” will call you back in few minutes time” yace “Ohk then” katse wayar tayi ta sauka downstairs, gun Usman ta nufa don
Hajiya Amina ta shiga kitchen, ta zauna kasa daga gefensa tana kallonsa tace
“Yaya wannan Dr din nan ne za su zo su nan wai sun shigo kano wani program, can they?” Usman yace “It’s okay… Mun yi Mun yi waya da shi ae daxu na tambavesa ko zai karaso yace min babu time saboda flight dinsu 3pm ne” Mayraah tace “Eh yace min an daga flight din sai dare, i just saw his call” Usman yace “Ohk send him the address” Tace “Ai ban sani ba to, gashi kayi masa sending…”
” Tana fadin haka ta
mika masa wayarta, Amsan wayar yayi ya rubuta address din gidan ya bata tayi sending ma Dr Khalil, sai ga kiransa ya shigo wayarta ta daga yace “Ohk expect us in 30mins time” Tace “To Allah ya kai mu” katse wayar tayi ta ajiye tana kallon Usman dake kallonta yace “Kije ki gaya mata za ki yi baki” Mayraah tayi shiru, sai ga Hajiya Amina ta shigo parlon da abinci ta debo masa, ya kalleta yace “Na fa ci abinci a gida” Tace “Ko kadan ne ka ci” Mayraah dai ta mike zata wuce sama don taje tayi wanka Hajiya Amina tace “Kema naga ba ki wani son cin abinci, dawo sai ku ci tare” Mayraah ta kalli Usman da Usman da
ya kalleta shi ma, Hajiya Amina ta ajiye
masu tuwo da vegetable soup tace “Taho
ku ci Hajiya” Mayraah tavi murmushin
karfin hali kawai ta koma ta zauna, Hajiya
Amina tayi wucewar ta sama, tuwon
Mayraah ta fara ci ba tare da ta jira sa
ba, bayan few minutes ya sakko kasa
shi ma ya dau spoon ya fara cin tuwon,
tana kallonsa tace “Is it sweet?” Yace
“‘Wa yayi?” Ta langwabar da kai tace “Ni mana” Yace “Bari in gama tukun sae
¡inji ko yayi” Dariya tayi ta ci gaba da cin tuwon ta, bata wani ci da yawa ba ta tashi ta bar masa ta wuce sama, sai da ta fara zuwa dakin Hajiya Amina ta sanar
mata da zuwansu Dr Khalil sannan ta
koma dakinta tayi wanka ta shirya, jikin windown dakin ta tsaya tana viewing din
unguwan that’s beautiful, sai abun yake
mata kamar ta taba zuwa anguwan nan,
ko ma dai ba shi ba ita dai tasan ta zo
area kamar haka, Lkci daya Musharraf fado mata, ta zaro ido gabanta na
faduwa, kamar unguwan da ta taba zuwa
ta samesa fa, tana cikin wannan tunanin
wayarta dake kan gado yayi vibrate ta
juya ta dauko wayar ta daga ganin Dr
Khalil ne, yayi mata sallama yace “To, ga mu a house number din” A hankali
tace “Ohk” Katse wayar tayi ta dau veil
dinta ta fita, bata tadda Usman a parlor
ba, hakan ya bata mamaki, sai ta koma
sama ta gaya ma Hajiya Amina bakin
sun iso, Hajiya Amina tace “Ba sai kin fita
ba bari zan kira mai gadi ya bude masu
gate din kawai” Mayraah tace “To, yaya
ya tafi ne?” Hajiya Amina tace “Eh dama
Daura zai tafi, kuma ya wuce” Mayraah
tayi shiru, sai kuma tace “Bai ce min zai
tafi ba” Hajiya Amina tace “Ai na zata
kun yi sallama” Mayraah bata sake cewa
komai ba Hajiya Amina ta kira mai gadi
tace ya bude ma baki gate, Mayraah
ta juya ta fita daga dakin. Bayan some mintues ta sauka Downstairs don bude masu kofa, tana bude kofar taga Dr Khalil, murmushi tayi masa tace “Sannu da zuwa Baban twins” har cikin parlon tayi masa iso bayan sun gaisa ta kawo masa ruwa da lemo, yace “Ya jikin?” Tace
“Naji sauki, kace har da su Dr Hamid” yace “Ohh su mota za su bi zuwa kd sannan su dau train, sun wuce tun dazu, nima hakan na so yi but it’s not possible” Mayraah tace “Allah sarki” Hajiya Amina ta shigo parlon suka gaisa da khalil da fara’a sannan ta koma sama, Dr Khalil yace “Ita ce Ammin?” Murmushi kawai Mayraah tayi, yace “I spoke to ur brother, the Barrister, about ur work…. he said he will get back to me idan yayi magana da Abbanku, that was today in the morning so ban san ya za su yi ba, ina dae jiran kiransa” Mayraah tayi shiru tana kallonsa, yace “So duk yanda Abbanku yace haka za ayi, i hope za su bar ki kiyi aikin, in aikin, in future za ki ji dadin hakan, no matter how wealthy ur parents are yana da kyau ace kai ma kana da source of naka income din” Mavraah tavi murmushin karfin hali bayan ta tuna she is just an abandoned orphan warce ko gadon wa enda take ma kallon iyayenta bata da shi, tunanin hakan ba karamin distablizing dinta yayi ba a lokacin, Dr Khalil yace “I think zan zo in tafi airport kar in yi missing flight…” A hankali tace “Baka sha ruwan ba ai” yace
‘ am okay, i just ate” tace “Toh shikenan” ya mike yace “Kiyi ma Ammi sallama pls” tace “In sha Allah” rakasa tayi bakin kofar parlon, yace “Baza ki rakani har waje ba kenan” tayi murmushi tace “Zan raka ka” A tare suka nufi gate din gidan suka fita har kofar gida, ya kalli Mayraah yace “Mu je ku gaisa da wani Dr, kin dai san sa… tace “Ohk” karasawa gun motar tayi Dr Khalil ya bude kujera me zaman banza, turus Mayraah tavi tana kallon wanda ke zaune, shi ma tunda ya kalleta sau daya ya dauke idonsa yana ci gaba da kallon abinda yake yi a waya ya wani keeping serious face, ta kalli Dr Khalil da yayi mata alama da she should greet him, hakan yasa a takaice tace “Good day” ko jira ya amsa bata yi ba ta bar wajen, bata san shi ma bayi da niyyar amsawa ba, tana kallon Dr khalil tace “To Dr Allah ya tsare, a gaida min twins” Dr Khalil ya girgiza kai yana kara jinjina halinta, ta sakar masa murmushi tavi wucewarta cikin gida, Ta madubi MD ya bi ta da kallo har ta shige gidan, sae kuma ya kalli Dr Khalil yace “Wanna fitsararriyar yarinyar kake dagewa in shiga cikin gidan in duba ko? Does she even look like someone that is sick at all? Wallahi idan na maka
Allah ya isa bata min lokaci da kayi sai Allah ya kama ka, what nonsense, yanzu meye amfanin nan din da ka kawo mu?” Dr Khalil ya kasa rike dariyarsa don daga Dr Khalil ya kasa rike dariyarsa don daga
Mayraahn har MD din ba karamin dariva suka basa ba, Dr Khalil ya zagaya ya shiga driver seat, MD yace “Allah bazan yafe maka ba, haka kawai kayi forcing dina mun zo nan yarinya ta fito ta min rashin kunya? Do you have any grudges against me Khalil?” Dr Khalil na danne dariyarsa yace “Oga boss i never forced u, kai da kace zaka Yola meye na biyo mu kano program din da kafi karfin attending, da ba sae ka tafi yolan ba kawai, sai dai in sharri zaka min sir, kuma fa ta ce maka good day” a fusace MD yace “Da na buge mata baki zata san good day, ni sa’anta ne da zata ce min good day, do i look like her mate ko an gaya mata Ina harka da yara, wannan fa bata wuce 16 years ba idan aka duba real date of birth dinta” Dr Khalil ya tada motar suka bar layin, MD ya gyara zama yace “Nonsense, saboda suna common Miller road shine take tunanin kowa sa’anta ne?” Dr Khalil saboda suna common Miller road shine take tunanin kowa sa’anta ne?” Dr Khalil yace “Yanzu dai ba Ghetto ka ganta ba balle ka samu abun fade” MD yace “Muna komawa Abuja zan yi erazing data din da ka bani, she should come for interview…
Dr Khalil dai murmushi kawai yake yana driving dinsa, can dai yace “Kai fa Dr ko manyan likitoci ba harkansu kake shiga ba, sabgar gabanka kawai kake baka da lokacin su balle wanna yarinyar da kace shekaranta 16, naga ita dai ta samu time dinka sosai”
Comments.
Ranan Lahadi karfe sha daya Mayraah ta gama shiryawa ta rufe karamin jakarta, sannan ta dau wayarta ta kira Maheer, yana fara ring ya daga, yace “Mimi” Tace “Ina kwana yaya” Yace “Lafiya lau, how was ur night” Tace “Alhmdlh, dama ce maka zan yi na shirya” Yace “But ai sai da yamma Mimi” Ta ɓata fuska tace “Don Allah yaya ka zo ka tafi da ni gida, yau fa Abba yace, it doesn’t matter ko da safe ne ko da yamma” Yace “Toh kin ga ina wajen aiki yanzu, after work sai in biyo in dauke ki, be patient please” Ji tayi kamar ta fashe da kuka, yace “Are you there?” da kyar tace “Na ji” Daga haka ta katse wayarta tana turo baki, bude kofar aka yi ta juya, Hajiya Amina ta shigo tace “Mu je ki rakani gidan makotanmu in masu gaisuwa, they lost their daughter 4 days ago” Mayraah tace “Toh” Mikewa tayi ta ciro Hijab dinta ta saka sannan ta bi Hajiya Amina suka fita, gidan dake kusa da na Abba suka shiga, Bayan Hajiya Amina tayi masu gaisuwa ta gabatar masu da kanta a matsayin neighbor dinsu don tun zuwanta anguwan ba gidan wanda ta shiga, godiya suka mata sosai, Ita dai Mayraah na zaune, bayan ɗan lokaci Hajiya Amina tace “Toh bari mu koma, Allah ya gafarta mata, ya bada hakurin rashi” Suka mata godiya sosai sannan ta fita parlon da Mayraah, suna fita gate din gidan Mayraah ta dinga kallon motar dake tafiya duk da ya wuce gidan da suka fito, Hajiya Amina tace “Kinsan wanda ke cikin motar ne irin wannan kallo haka” Mayraah ta girgiza kai da sauri tace “Aa” Daga haka ta bi ta suka shiga cikin gida, tana komawa dakinta ta dau wayarta, dialing number dinsa tayi da ainahin sim da take using yanzu, har ya katse bai daga ba, ta sake kira sai ya daga, shiru tayi, yana jin haka yace “Mayraah” Ta sauke idonta kasa a hankali tace “Good morning Sir” Yace “Me yasa kika daina kunna line din da kika kirani da shi kwanaki, pls me yasa kike min haka Mayraah, is it because i care? Is it because i love you” Nan da nan jikin Mayraah yayi sanyi jin yanda yake maganar, a hankali yace “Mayraah” Cike da karfin hali tace “Ina ji… naga ka fito gida yanzu, ina za ka?” Musharraf ya kalli inda yayi parking a anguwan, everywhere was so silent balle ace ta ji hayaniyar mota or so, yace “Did u just guess?” Tayi murmushi tace “I saw you…. But in my dream” cikin sanyin murya yace “Mayraah my life isn’t the same again ever since you left me, ban san haka so yake ba i wouldn’t have started wllh, ni ban gujeki ba duk situation din da ya faru ke kika gujeni, da na sani da na ci gaba da zamana ban fara relationship ba, i had no luck in relationship kuma tsakanina da Allah na so ki ba da wani nufi ba, i resigned lecturing few weeks back, lecturing caused me all what i am going through now, i regret it, assuming a asibiti nake aiki may be sau daya zan ganki ki tafi shikenan ba lallai ki sake dawowa in ganki ba, amma as a lecturer, seeing you everyday made me fell in love with you without me realizing that, i never bargained for all this Mayraah, i am still yet to recover fully from the death of my father and only sister, then all of a sudden you….” Kasa ci gaba yayi, nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah jikinta yayi sanyi sosai ta kasa ce masa komai, ya katse wayar kawai, ta fashe da kuka, har ranta tasan she still loves Musharraf but su Abba baza su bari ta auresa ba, likewise his parent baza su bari ya aureta ba, kwanciya tayi tana kukan tausayin kanta. Wajen karfe hudu Maheer ya kirata, ta daga wayar tayi shiru, yace “Can i come over now?” A hankali tace “Yaya can i leave it tomorrow pls” Da mamaki yace “Why tomorrow?” Ta mike zaune tana dafe kanta dake mata ciwo tace “Kawai naji ina son in bari sai gobe da safe, ban san me yasa ba” Maheer yace “But are you okay?” Ta gyada masa kai tace “Ehh but deep down i want to leave tomorrow instead of today” Yace “Ohk then, zan gaya ma Ammi” Da sauri tace “How will you tell her?” Yace “Don’t worry Mimi, zan ce mata ban baro asibiti da wuri ba” Tace “Yauwa yaya” Yace “Bacci kika yi ne?” Tace “Yanzu na tashi” Yace “Ohk, to bari in yi sallah it’s almost time” Tace “Toh sai Anjima” Daga haka ya katse wayar ita ma ta mike ta shiga bandaki. Tana idar da sallah ta sake dialing number Musharraf, yana ta ring har ta fidda ran zai daga sai gashi ya daga, a hankali tace “When are you coming back?” Yace “To where?” Tace “Gidanka” Yace “I am home ae” tace “Naga ka fita dazu around 11:30” ya ɗan yi shiru, sai kuma yace “How?” Tace “In ur white car, u were on either black or navy Blue polo” Musharraf that was very surprise yace “Wait! How did you know?” Tayi murmushi cikin sanyin murya tace “That shows i am with you now and always” Musharraf yayi shiru, can yace “I believe kin zo anguwan ne” Tace “Not at all” Yayi kasa murya yace “Pls Mayraah, for the sake of the love i have for you tell me where are you now? Ina kika tafi” Tace “Ina Miller road” Musharraf yace “Miller road? I don’t understand” Tace “Yea” Yace “Wajen wa?” Tace “My aunt” Yace “But i am not too far from Miller, just few streets away” A hankali tace “I know” A bit confused yace “But which of ur aunt?” Tace “Baka san ta ba” Musharraf yace “Don Allah in da gaske kike send me the house address, don Allah ba don ni ba, don’t play with my feelings Mayraah” Ta ɗan yi murmushi tace “I will send u the address” Daga haka ta katse wayar ta masa fowarding address da ta tura ma Dr Khalil jiya, tana tura masa ya kirata yace “Don girman Allah da gaske kike Mayraah” Tace “Toh shikenan” Yace “Ohk, ok i am on my way now, right away” Daga haka taji ya kashe wayar, nan gabanta ya fara faduwa, to wa zata ce ma Hajiya Amina zai zo, what if yana zuwa Maheer ko Usman suka zo fa, ko kuma Abba ya dawo, ya zata yi? wannan tunanin yasa taji hankalinta ya tashi sosai, tasan babu wani nisa daga gidansa zuwa nan, ta mike da sauri ta tafi ta samu Hajiya Amina, Hajiya Amina tace “What will u be making for dinner?” Mayraah tace “Akwai sauran abincin Aunty” Hajiya Amina tace “Toh shikenan” Sunkuyar da kai Mayraah tayi tace “Dama Aunty wani coursemate dina ne…” Sai kuma tayi shiru, Hajiya Amina tace “Feel free” Mayraah tace “Yana nan anguwan ne, zai zo mu gaisa” Hajiya Amina tace “It’s okay, sai ki shigo da shi parlor ku gaisa ba komai” Mayraah ta girgiza kai da sauri tace “Aa za mu zauna a compound” Hajiya Amina tace “Toh shikenan” Mayraah har ta juya sai kuma ta sake dawowa tace “Aunty ai Abba bazai dawo ba yau ko?” Hajiya Amina tayi murmushi tace “Bazai dawo ba, kar ki damu” Mayraah ta juya ta fita daga parlon, tana komawa dakinta taga miss calls din Musharraf har 4, Hijab ta sa ta sauka downstairs, tana isa gate bayan mai gadi ya bude mata ta gansa tsaye jikin motarsa, kallonta yake babu ko kiftawa kamar yanda ita ma take kallonsa, she just can’t explain how she felt seeing him at the same time sai taga ya rame, kana ganinsa kasan ba shi da rest of mind, tayi karfin halin cewa “Ka shigo” Ya nufota har sannan yana kallonta, ta juya ta koma cikin gidan, wajen shan iska ta tafi yana biye da ita ta zauna, shi ma ya zauna yana facing dinta, a sanyaye tace “Good evening sir” kasa amsawa yayi ya dafe kansa, ta sauke idonta tana goge hawayen da ya fara taruwa da yatsunta, cikin rawan murya tace “Kayi hakuri, this our destiny” Yace “What is our destiny Mayraah?” Ta daga kai ta kallesa tace “Allah bai rubuta za mu yi aure yanzu ba” Yace “Sai yaushe?” Tayi karfin halin cewa “May be years to come, in dai da rabon za mu yi aure babu wani abu da zai hana hakan amma a yanzu kam ban ga alaman za mu yi ba” Yana gyada kai yace “Sai yanzu na sake tabbatar da baki so na Mayraah, i now believe ni ne kawai nake son ki, ni ne kawai nake bata lokacina” Ta fashe da kuka tace “Saboda me zaka ce haka? Iyayenka baza su yarda ka aureni ba, nima iyayena baza su yarda in aureka ba bayan duk abubuwan nan da suka faru a dalilin wedding dinmu that never occurred, and ah baya da nake tunanin zan iya bin ka mu tafi mu yi aurenmu a wani waje may be ban zauna nayi tunani da kyau bane a kan hakan, i get to understand that it’s the biggest mistake da ni da kai za mu yi making idan mun yi hakan, aure babu albarkan iyayenmu bazai mana lasting ba, daga karshe duk za mu zo muna da na sani ne, but keep in mind sir, you still remain my first love, a kanka na fara soyayya akan ka nasan menene so ina alfahari da hakan, sannan kayi min so na tsakani da Allah, kayi min so na aure, kuma har gobe bazan taɓa daina sonka ba sai ma sonka ya karu a zuciyata, kawai mu jira lokaci Sir, ina ji a jikina we are meant for each other kuma za mu yi aure amma ba yanzu ba, may be sai a gaba ta yanda bamu yi zato ba, but for now let act just like frnds mu ci gaba da zumuncinmu da communication don mu samu sauki a ranmu….” Ya ɗan yi murmushi ya mike, a hankali yana kallonta yace “Thank you Mayraah” kallonsa kawai take ganin yanda idonsa ya kada, ya juya ya nufi gate, mikewa tayi da sauri tace “Sir…” Ko waiwayowa bai yi ba har ya isa gate din ya bude ya fita, wasu hawaye ne suka dinga sauka idonta ta koma ta zauna ta hade kanta da table tana kuka a hankali….. Ammi na zaune parlon Abba tana xuba masa abinci bayan magrib, bayan ya kunna TV yace “Mayraan bata dawo ba yau ne?” Ammi tace “Maheer din yace bai baro asibiti da wuri ba sai gobe” Yace “Ohk…” Bayan ta gama zuba masa zata fita ya bi ta da kallo yace “Za mu yi magana ne idan na gama” Tace “Ka kirani in ka gama” Daga haka ta fita daga Parlon, duk kwanan nan ko zama part din nasa bata son yi unlike before, iyaka ta shigo ta basa abinci ta koma bangarenta, ko kwana ta daina yi a part din, yana gama cin abincin ya kirata, bayan ta dawo parlon ta zauna, yace “Duk kwanan nan ina lura kin maida bangaren nan baƙon ki” ta wani hade rai tace “Don Allah bana son wannan maganar… In wata magana ce ka min amma ba wannan ba” Ya ɗan yi murmushi yace “Ohk” Ajiye ruwan hannunsa yayi yana kallonta, bayan few seconds yace “Akan Usman ne….” Ammi ta maida hankali kansa tana sauraronsa, cikin few minutes Abba ya gaya mata maganar da Usman ya samesa da shi, Ammi sai kallon Abba take without blinking, can ta girgiza kai tace “I will prefer Maheer, don ya fi sa sanyin hali da sanin ya kamata, kuma nayi magana da shi akan hakan few days back, don haka ka bar maganar Usman” Abba dake ta kallonta da mamaki yace “But Usman showed interest first, saboda me za ki ce Maheer? Saboda me zan bar maganar Usman?” Ammi tace “Eh Maheer nace, saboda duk nasan halinsu ai, ita ma kuma nasan halinta da wanda zai iya hakuri da ita, ya kuma fi sanin ciwonta….” Abba yace “To tunda haka ne duk a bar zancen, daga Usman din har Maheer nayi cancelling maganar, tunda naga abun naki kamar son kai ne” Ammi tace “Babu batun son kai, future din yarinyata nake dubawa da inda zata samu kwanciyar hankali… Kuma duk yaran nan dai naga nawa ne babu wanda zai ce ya fini sanin halinsu gaba daya su ukun, kuma kayi hakuri zance dai baza a bar shi ba Yallabai, dama Maheer din ba wai yayi dacen mata bane, Mayraah kuma zata fi dacewa da shi don ina ga ko ni ban san halinta yanda Maheer ya sani ba” Mikewa Abba yayi ya bar mata parlon ya shige daki don baya son biye ta, ta kwashe warmer din abincin ta fita ita ma. Karfe tara na safe Mayraah ta sakko downstairs da jakarta, Hajiya Amina dake ta kallonta tace “Ko dai baki jin dadi ne, tun jiya naga you are not ur self, is anything wrong?” Mayraah tayi murmushin karfin hali tace “Ba komai Aunty, ciwon kai ne amma yayi sauki yau da safe” Hajiya Amina tace “Maheer din na waje ne” Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina ta dau ledan dake gefenta ta mika mata tace “Ga su nan turarruka ne, though they are not much” Mayraah ta risina ta amsa tace “Nagode Aunty” Hajiya Amina tayi mata murmushi tace “You are welcome, ki gaida Amminku da Mama” Mayraah tace “To za su ji in sha Allah” Daga haka ta nufi kofa ta fita, tana isowa kofar gida ta tadda Maheer a mota, ta karasa ta bude front seat ta zauna tana kallonsa tace “Ina kwana” Yace “Lafiya lau” A hankali tace “Yaya baza ka shiga ka gaisheta ba” Ya ɗan yi murmushi yace “Kin ga na makara, sai naje nayi dropping dinki sannan in tafi aiki” Mayraah tace “Just 2 minutes fa is enough yaya, kuma tasan kai ne ka zo daukata” Yace “Ohk i will do that next time in sha Allah” Bude motar tayi ta sauka tace “Ni dai sauko kaje ka gaisheta sai ka fito mu tafi” Shiru yayi yana kallonta, can ya kashe motar ya bude ya sauka ya zagayo, tana murmushi tace “Yauwa ko kai fa” Hancinta ya ja sannan ya shiga cikin gidan ta bi bayansa, har sannan Hajiya Amina tana zaune parlor tana kallo, Maheer ya karasa ciki bayan ta amsa sallamarsa, ya zauna sannan ya gaisheta ta amsa da fara’a tace “Ya aikin Dr” Yace “Alhmdlh” Tace “To maa sha Allah, ya su Ammi da Mama” Yace “Suna nan lafiya” Ta mike tace “Bari a hado maka breakfast” Yace “Aa i am okay, aiki zan tafi” Daga haka ya mike, Tace “Toh shikenan, Nagode kwarai, Allah ya tsare” Yace “Ameen” har balcony ta rakasa ya mata godiya ya sauka, Mayraah dake zaune inda ake shan iska ta mike ganin ya fito, ta jira har ya karaso inda take suka fita gate din a tare, suna barin anguwan tana kallonsa tace “Yaya” Ya juya ya kalleta sannan ya ci gaba da driving dinsa yace “Mimi” a hankali tace “You know what?” Yace “No Mimi” Tace “Kwanan nan naga u are somehow, is there anything wrong? You are not longer lively like before, baka magana sosai, you are always silent, why is that?” Maheer ya kalleta yace “Ba komai, i will be fine in sha Allah, stress din aiki ne” Mayraah tace “Ko har da na matarka?” Ya girgiza kai yace “Not at all, ai bana shiga harkanta, i have nothing to do with her, i am just waiting for time” Mayraah tace “To koma menene yasa kake zama silent kayi hakuri ka ji” Yayi murmushi yace “You are funny Mimi, ba komai kawai yanayin aiki ne” Murmushin tayi ita ma duk da nata damuwar da yayi mata yawa a zuciya ɗon ko baccin kirki bata yi ba jiya saboda tunanin Musharraf amma tun dawowarta gida bata jin dadin yanda ta lura Maheer bai cika son magana ba unlike before, she missed the old him, a haka har suka iso gida wanda in da ne ko bata basa labari ba shi zai dinga bata har su isa inda za su, bayan yayi parking kofar gida ta juya tana kallonsa tace “Take care of ur self” Yace “Toh Mimi” Bude motar tayi ta sauka ta dau jakarta a back seat sannan ta shiga cikin gidan, yayi reverse ya bar anguwan.
Abba na zaune parlon Ammi tare da Usman da Maheer, sai Ammi da Mama Ladi dake parlon su ma, Mayraah ce ta shigo karshe bayan Mama Ladi taje ta kirata a wajen Badiyyah, Mayraah ta zauna kasa kusa da Ammi wondering why she saw everyone sitted kamar ana meeting, Mama Ladi tace “To kai yanzu Mamuda a ina ka taɓa jin an bar ya mace tayi aiki? Ni dai tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin haka ba gaskiya, kyan ya mace ai dakin mijinta, sannan kace Habuja kana nufin mu sake sakinta kamar akuya ta koma Habujan kenan, abinda fa hankali zai dauka shi ake yi Mamuda, ya mace take faa” Maheer dake ta kallon Mama Ladi yace “Wa yace maki mace bata aiki?” Mama Ladi tace “Aa ba ruwana, ba a pamilyn mu ba wallahi, yanzu duk abun magana ai kamata yayi mu gujesa, har yanzu fa bamu gama farfadowa daga bakin fentin da Badiyyah ta goga ma pamilyn mu ba, in ku kun farfado ni ban farfado ba wllhi, tunda gashi har yau bana iya fita sai ina boye fuska kar a danganta ni da Badiyyah” Shi dai Usman bai ce komai ba, Ammi ma tayi shiru amma kana ganin mood dinta kasan batun aikin bai mata dadi ba ko kadan duk da Maheer ya mata maganar jiya, Abba ya sauke ajiyar zuciya yace “Duk abinda kika fada gaskiya ne Mama, amma dama ai baza ta fara aiki haka kawai bata da kowa a garin Abuja ba, duk sai da na gama tsarina da Usman sannan na tara ku a nan….” Ammi ta daga kai tana kallon Abba, Abba ya ci gaba yace “Babban asibiti ne kuma sananne a Nigeria, ba kowa ake bama aiki a asibitin ba, na taɓa wani aboki likita yayi aiki a asibitin shi ma kafin ya koma kasar waje, shi yasa naji bazan bari damar nan ta subuce ma Mayraah ba….” Mama Ladi tace “Naga abinda ya isheni, to me zata yi da aiki? Ba ci ta rasa ba, ba sutura ba, ba komai ba” Abba yace “Aa zata yi aikinta in sha Allah….” Mama Ladi tace “Toh aure fa? Kana ta maganar aiki kamar wasu kafurai, haka za mu sa ta gaba sai ta tsofe a gida mu shiga uku Mamuda, aure fa shine martabar ya mace ina tunatar da kai” Abba yace “Aure ai lokaci ne Mama, wuyarta lokacin ya iso za ayi, aiki kuma baya hana aure, mutane da yawa na neman aikin basu samu ba” Mama Ladi ta kyabe baki tana girgiza kafa alamar ita fa batun aikin bai gamsar da ita ba, Abba yace “Saboda haka na yanke shawaran Amminta zata koma Abuja da zama gaba daya, don har na siya gida a can an zuba komai, tarewa kawai ya rage, tun da idan nace a fara ginin filina dake can din zai iya daukar lokaci kuma Mayraah zata yi resuming aiki next week” Mama Ladi dake gwalo ido tace “Ka siya sabon gida a Habuja Mamuda?” Kabbara Mama Ladi ta saki cike da farin ciki sannan tace “Alhamdulillahi, dama ance mahakurci mawadaci, shikenan Ammi zata koma er Habuja duk me son ganinta sai ya shirya nan kuwa ko wani kare da doki shigowa yake, dama Allah na tuba anguwan nan in ba dole ba me mutum zai yi da shi duk ɗoyin ƙwata, duk lungun da ka bi warin ƙwata, kai maa sha Allah amma nayi farin ciki da wannan labarin kuma ka kyauta Mamuda” Abba ya ciro wayarsa dake ringing yayi picking call din abokinsa, Mama Ladi da farin cikinta ya kasa boyuwa ta mike ta lallaba ta tafi kusa da Maheer tace “Mashir a ina zaka samo min wani akwatin wallahi na gaji da wannan dama” Maheer yayi murmushi yace “Usman ne yasan inda ake siyarwa” Zata koma gun Usman taga Abba ya gama wayar da yake ta koma da sauri ta zauna tana washe baki, Abba ya ajiye wayarsa yace “Amma magana ta gaskiya Mama baza ayi tafiyar nan da Badiyyah ba, tun da can kadunan ance Hajjan ba lafiya to ina ga in zaki koma Karaye zaki koma can tare da ita kawai, don zuwa jibi za su bi jirgi in sha Allah, kayan sawansu kawai za su dauka…” Sake baki Mama Ladi tayi tana kallon Abba bata ko kiftawa.
Mama Ladi na gyara shimfidar da zata kwanta bayan ta ci kukanta ta gode Allah tace “Toh ma sai kace wata gantalalliyar tsohuwa mara makabuli ina ni ina bin ku wani Habuja, sai kace ban san me nake ba da zan kwashi kafa in bi ku kamar a garin gaba gaba, ai da wayo na kuma ni ba mahaukaciya bace nasan me nake, amma abinda yayi min ciwo har na zubda hawaye dalilin da zai sa Mamuda yace in dauki Badiyyah mu tafi karaye, a dubi girman Allah a gaya min me na hada da Badiyyah da Mamuda zai ce min haka? To wannan cin mutuncin da yayi min shi ya min ciwo har nake ta kuka amma ba wani abu ba” Ammi dai dake zaune parlon ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba, Mama Ladi tace “Kuma a gaskiya ni ba a taba ci mun mutunci irin yau ba ma tunda uwata ta haifeni, wai in tafi da Badiyyah karaye ashe ma ni na mata cikin, to wallahi ki ja masa kunne ya fita harkata ya bar hada ni da Badiyyah, babu abinda na hada da ita haduwar bariki rabuwar bariki, kakarta ce fa yayata amma ko a lahira ni bazan ga Badiyyah ba, in zuciyata ta debeni sai in iya ja masu Allah ya isa daga
Mamudan har shegiyar Badiyyan da yake hada ni da”
Daga haka tayi kwanciyarta tana matsar wasu sababbin kwallan tace “Dama da asussuba Mashir ya zo ya kai ni tasha, maganina ma kenan da nayi ta zama nan kamar wata mara galihu” Ammi tace “Kiyi hakuri Mama Ladi duk bai kai…” A fusace Mama Ladi ta mike zaune tace “Rufe min baki, ke da kika ji yana cewa in koma karaye baki da bakin magana ne? Ni na cancanci Mamuda yayi watsi da ni? Da ba don ni ba ai gidansa fanko ya so komawa amma dan Adam me mance alkhairi, kullum fa sai an bugo min waya daga karaye ana tambayar Baaba ladi yaushe za ki dawo, da gata na kaca kaca a can, to kafin ku tattara ku koma Habujan ni gobe da Asuba zan bar gidan, kuma ki mayar masa da shegen kudinsa da ya bani bana bukata, ban rasa komai ba a karaye wallahi” Daga haka ta sake komawa ta kwanta tana matsar sabbin kwalla, Mikewa Ammi tayi ta shiga bedroom dinta don for almost an hour Mama Ladi ke ta mita da koke koke ita dai hakuri kawai take bata, wajen karfe sha daya da rabi ta sake fitowa paron rike da wayarta ta ga Mama Ladi kwance ido biyu, Mama Ladi da bata wuce karte tara da rabi da ta ci ta koshi take bacci, Ammi dai bata ce mata komai ba ta fita daga parlon ta sauka downstairs, Maheer ta ganin kwance kan 3 seater idonsa rufe, Ammi ta karasa kusa da shi ta tabasa tace “Maheer” Bude ido yayi, ya mike zaune tace “Baka tafi ka kwanta ba kake bacci a nan” Ya kalli agogo sannan ya mike zaune, Ammi ta zauna daga side dinsa tana kallonsa tace “Ka ci abincin ma kuwa?” Yace “Na ci” Sai kuma ya mike yayi mata sai da safe ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita, Number Aunty Mariya ta fara dialing sanin mijinta baya gari, yana fara ring kuwa ta daga, tace “Baki yi bacci ba Ammi” Ammi tace “Ban yi ba” Aunty Mariya tace “To ya gidan? Ya su Mayraah?” Ammi tace
“Alhamdulillahi” Shiru Aunty Mariya tayi tana sauraren dalilin kiran Ammi don tasan tunda ta kirata by this time akwai magana ne, Ammi ta sauke ajiyar zuciya ta sanar ma Aunty Mariya abinda ake ciki, Aunty Mariya tayi farin ciki da samun aikin Mayraah da kuma garin Abuja da za su koma, she was so happy, tace “To yanzu Ammi ya za ayi da Mama Ladi?” Ammi tace
“Mama Ladi? Badiyyah dai… tambaya za kiyi ya za ayi da Badiyyah tunda ita Mama Ladi tana da inda za ta, Shi kuma yace babu inda za aje masa da Badiyyah, i am confuse ban san ya zan yi ba kuma” Aunty Mariya tayi shiru, can ta sauke ajiyar zuciya tace “Amma dai Ammi shawaran da aka yanke tun farko shine a kai ta Bichi….” Ammi tace “To bari kiji tunda na kirasu na sanar masu abinda ke faruwa buden bakin shi yayan baban nata wai sun kwana biyu su basa Bichin sunyi tafiya, ita kuwa autars baban nata ita ma da na kirata bayan kwana biyu ce min tayi tana wajen mijinta a portharcourt yaranta ma na gun kakarsu, Kinga ai sun hada baki kenan, ni kuma gaskiya ban wani ga laifinsu ba, babu wanda zai karbi Badiyyah ko waye ma haka zai yi, ko don na bar zancen ban gaya maku ba? ita kanta Mama Ladi bata san yanda muka yi da yan Bichin ba ai har yau, to yanzu ga abinda Mai gidan yace i don’t want to have any issues with him, don da farko cewa ma yayi Mama Ladi ta koma karaye da ita shine ta dinga rusa kuka wai an cuceta an hadata da Badiyyah” Aunty Mariya tace “Kinsan me zai faru Ammi, ai Hajjan yanzu jikinta da sauki don ko jiya naje gidan Baaba Yahanasun dubata don haka kawai ki tattara Badiyyar ki sa ta a mota ta koma can wajensu ai ta san gidan, kuma ba sai kin gaya ma kowa ba kawai su ganta, idan ya so ki kashe wayarki kawai, ni dai Hajja bazata fara cewa Badiyyah ta zo wajena ba tunda tasan yanda yanayin gidan nan yake, in kuma kince ba haka ba to ni kam ban san yanda za ayi ba kuma” Ammi tayi shiru tana nazari, Aunty Mariya tace
“That is the only way out fa, infact don ma mun samu Abbansu Maheer din ne amma wallahi ba ko wani namiji ne zai yi tolerating haka ba, ko mai gidana nasan bazai fara yarda Badiyyah ta zauna gidana ba, dama Mama Ladin ce dai dai tafiya da ita karaye ni ko nasan ko daura ma Mama Ladi Badiyyah aka yi a kafa sai ta kunceta” a hankali Ammi tace “To shikenan, zan sa Maheer ya kai ta tasha gobe ya saka ta a motar Kadunan tunda babu wani mafita bayan wannan” Aunty Mariya tace “Shine kawai magana, yanzu yaushe za ku koma Abujan?” Ammi tace “Ya ce jibi…” Aunty Mariya tace “Kai maa sha Allah, wallahi nayi murna sosai Ammi Allah ya sanya alkhairi, dama duk mahakurci bazai taba tabewa ba, sannan Ammi ina ta son zan maki magana akan matar Maheer, yanzu shikenan ana nufin haka zai ci gaba da zama da ita?
Wato ta ci bulus duk abubuwan nan da suka faru uwa uba ga bin bokaye da malamai, asiri har a dakinki?” Ammi tace “Mariya, the girl is pregnant” Sai da Aunty Mariya ta mike zaune daga kwancen da take, tace
“Pregnant kuma Ammi?” Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace “Har wata uku kuwa, shi dai yace bai san da shi ba, shine Abban nasu yace a jira ta haihu ayi DNA, wannan dalilin yasa muka hanasa sakinta tukunna, yanzu ma nasan kawai suna zaune under same roof ne babu yanda zai yi tunda kinsan baya ketare maganata amma ba da son ransa suke waje daya ba, ai ko da dan sa ne ni bazan i supporting ya ci gaba da zama da ita ba wallahi, for now dai we just have to be patient a fira ta hainu ayi DNA din, kinji dalilin da yasa take gidan nan har yanzu” Aunty Mariya jikinta yayi sanyi, a ranta kuwa har ta fara addu’a Allah sa Maheer have nothing to do with the baby, Allah ya rabasa hada zuri’a da irin Haseenah, can dai tace
“Amma Ammi an tabbatar kuwa, anje anyi scan ko kawai da baki ta fadi? Yarinyar nan fa makira ce babu abinda bazata iya aikatawa ba wilhi, sai ta iya forging cikin ma ko a asibiti” Ammi tace “Kin manta shi likita ne Mariya? Anyi scan, ai shine nace maki har wata uku with few days” Aunty Mariya ta tabe baki tace “Ai shikenan, amma what if the DNA result comes out negative after still keeping her for 7 months Ammi?” Ammi tace “Ta cuci kanta ba mu ba” Aunty Mariya ta girgiza kai tace “Allah Ubangiji ya shirya mana zuri’a” Ammi tace “Ameen, sai da safe” Sallama suka yi
Ammi ta katse wayar ta wuce sama zuwa part dinta, har a sannan Mama Ladi bata yi bacci ba, Ammi ta kalli agogo da mamaki tace “Baki yi bacci ba Mama Ladi?” Banza Mama Ladi ta mata, Ammi ta karasa cikin bedroom dinta. Washegari da sassafe Ammi ta kira Maheer ta sanar masa yanda suka yi da Aunty Mariya kan cewar ya dau Badiyyah ya kai ta tasha, shi dai yayi shiru yana kallonta, tace “Ko ya ka ga Maheer?” Maheer yace “To ya za ayi dama, tunda relatives din babanta na denying dinta and they are not to be blamed, kawai hakan shine mafita” Ammi tace “Dama nima ban yi blaming dinsu ba” Maheer bai sake cewa komai ba, Ammi tayi kasa da murya tace “Da zaka taimaka ma tunda yau Saturday da kayi dropping dinta a kadunan saboda situation dinta”
Maheer yace “Ai yau din ma ina zuwa aiki Ammi, kawai dai ina dawowa da wuri ne” Ammi tayi shiru, sai kuma tace “Toh shikenan” Yace “In ba dai Barrister za ki ma magana ba tunda yana nan” Ammi ta rike haba tace “Wani Barrister din?” Maheer yace “Usman mana, shi da ya maida zuwa kaduna kamar zuwa cikin gari” Ammi ta tabe baki tayi murmushi kawai bata ce komai ba, Maheer ya mike yace “Ko ni sai inje in masa magana yanzu” Ammi tace “Ka dai san dama ba Badiyyah bace, amma ko me zaka ce masa in dai
Badiyyah ce bazai je ba” Usman ne ya sauko downstairs zai je kitchen ya hado shayi, Ammi ta bi sa da kallo, ya karaso ya gaisheta ta amsa, ya kalli
Maheer yace “Bonjour” Maheer ya daga kai ya kallesa yace “Morning” Zai tafi kitchen Ammi tace “Usman zaka je kaduna ne yau?” Ya juyo ya kalleta yace “Eh”
Tace “Kamar yaushe?” Yace “Zuwa karfe goma in sha
Allah” Ammi tayi kasa da murya tace “Dama wai taimakawa zaka yi ka ajiye Badiyyah a gidan Baaba Yahanasu” Kallonta Usman ya tsaya yi, can yace “Duk da dai ban tabbatar da tafiyar ba tukunna” Ammi ta dan kalli Maheer da yayi murmushi kawai, Ammi tace
“Toh shikenan” Juyawa Usman yayi ya shiga kitchen,
Maheer yace “Zan dau excuse wajen aiki sai in ajiyeta in sha Allah” A hankali Ammi tace “Allah maka albarka, sai ku je da Mayraah to keep u company, kafin yamma kun dawo in sha Allah, amma sai kun fita da wuri” Karfe tara Maheer ya shirya ya yafi bangaren Ammi, tuni Ammi ta kira Mayraah ta sanar mata tafiyar da za su yi Kaduna, jikin Mayraah yayi sanyi don tausayin Badiyyah take har cikin ranta, Ammi ta sa taje ta hada mata kayanta duk a akwati, Mayraah na hada kayan Badiyyah dake ta bin ta da kallo tace
“Me yasa kike hada kayan Mayraah?” Mayraah ta kasa kallonta, har sai da Badiyyah ta sake mata tambayar, ba tare da Mayraah ta kalleta ba tace “Za mu je kaduna ne?” Badiyyah ta mike zaune da kyar tace “Kaduna kuma? Wajen wa a kaduna?” Mayraah tace “Nima ban sani ba, Ya Maheer ne zai kai mu” Shiru Badiyyah tayi amma haka nan taji hankalinta ya tashi sosai, cikin karfin hali tace “Har da Ammi?”
Mayraah ta girgiza kai tace “Aa” Daga haka ta mike ta fita daga dakin, tana share hawayen da ya makale idonta ta kulle kofar ta jingina jiki, Usman ne ya fito daga dakinsa ta juya ta kallesa sai kuma ta sunkuyar da kai, har ya karaso inda take tsaye bai daina kallonta ba, jin bai ce komai ba ta daga kai ta kallesa, a hankali tace “Ina kwana?” Yace “Why are you crying?” kamar jira take ta fashe da kuka, ya bi wajen da kallo sannan ya matso kusa da ita ya kamo hannunta da mamaki yace “What happened?” Cikin rawan murya tace “They are taking Badiyyah to kaduna, Yaya idan taje can babu wanda zai kula da ita and she needs care in this her condition, this is her destiny we are not suppose to neglect her..” Usman yace “Is that why u are crying?” Ta gyada masa kai, yace “Did anyone help u carry ur own destiny with you? I mean… did anyone partner with u in all what u went through this pass months?” Mayraah ta dinga kallonsa hawaye na sauka idonta, yace “So she should carry her cross alone” Yana fadin haka ya kai fingers dinsa yana share mata hawayen fuskarta, Mayraah couldn’t stop looking at him, she doesn’t even understand if she is surprise or Shock at his action, kuma bai fasa kallon kwayar idonta ba while wiping away her tears. Ammi ce ta fito daga part dinta, tunda ta kallesu sau daya daga nesa bata sake kallon direction din ba, Mayraah ta matsa daga kusa da shi da sauri, har dai Ammi ta karaso tace “Kin gama hada kayan ne Mayraah?” Mayraah ta gyada kai tace “Na gama” Ammi ta kalli Usman da ya juya zai sauka downstairs tace “Kai kayi breakfast din ne?” Ba tare da ya juyo ba yace “Na yi” Ammi ta maida dubanta kan Mayraah tace “Shiga ki fito da akwatin ki kai motar yayanku, yana waje yana jiranku” Mayraah ta bude kofar dakin ta shiga, Ammi kuma ta koma part dinta, Mayraah na sauka downstairs da akwatin Usman yace “where are you taking it to?” Tace
“Motar ya Maheer, Ammi tace shi zai kai mu” Usman ya gyada kai without saying anything, tana jan akwatin ta fita compound, Maheer na jingine jikin motarsa ya hango Mayraah, ya nufeta ya amshi akwatin, tace “Yaya ina kwana?” Yace “Lafiya lau, how was ur night?” Tace “Alhamdulillah” tare suka karasa gun motarsa ya bude booth ya saka akwatin yace “Ina take?” A hankali Mayraah tace “She is inside” Daga haka ta juya ta koma cikin gidan, duk Haseenah na lekosu ta window with so many thoughts running her mind, can ta dan yi murmushi ta juya ta bar bakin windan. Ammi ta shiga dakin da Badiyyah take, ta sameta zaune kana ganinta kaga tashin hankali a fuskarta, a takaice Ammi tace
“Maheer zai kai ki Kaduna, za muyi tafiya da Abba, kinga babu kowa gidan, Mama Ladi kuma zata tafi karaye, mai aikin zata tafi garinsu, Mayraah ta samu aiki a Abuja she will be traveling too” Badiyyah ta fashe da matsanancin kuka tace “Ammi ko ni kadai ce don Allah a bar ni zan zauna wallahi, don Allah ku rufa min asiri” Ammi tace “Kulle gidan za ayi, haka zaki hakura ki tafi kadunan sai sanda Allah yayi mana dawowa gaba daya” Tana kuka sosai tace “Ammi wajen wa a Kaduna?” Ammi tace “In an je za ki gani, ki dauko hijabinki ki fito lokaci na wucewa” Daga haka Ammi ta bar dakin, Badiyyah ta tashi tana kuka sosai ta dau hijab ta saka ta fito, dubu ashirin Ammi ta bata ta amsa tana kuka har suka sauko downstairs, har sannan Usman na zaune Ammi ta raka Badiyyah bakin kofar parlon, Mayraah ta dinga kallonta cike da tausayi har ta karaso parking space ta bude mata mota ta shiga ta kulle sannan ta tafi front seat don Maheer na cikin motar a zaune, babu bata lokaci suka bar gidan. Hira Mayraah take ta yi ma Maheer dake sauraronta bayan sun dau hanya, Badiyyah dake zaune a baya tayi nisa cikin tunanin da take gaba daya bata ma cikin hayyacinta bata san me suke cewa ba duniya ta mata zafi, after an hour drive Mayraah ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Maheer tace “Ni kadai nake ta labarina” Yace “No, ina jin ki mana Mimi, what were you even saying?” Kin cewa komai tayi ta hade rai tana kallon titin gabansu, ya dan yi murmushi yace “So now sai monday zaki amshi statement of result dinki kafin ku tafi Abuja?
Since u will be going for interview on Tuesday…” Mayraah ta gyada masa kai kawai, yana murmushi yace “C’mon Mimi, i am sorry” Ta dan turo baki, yace
“Baxa ki hakura ba” Tace “Na hakura but yaya ni tsoron interview din nake, MD din bashi da mutunci kwata kwata wallahi, yana da anger issues, sannan he is rude and arrogant, infact he is so loud for my liking komai masifa da jaraba” Maheer na gyada kai yace
“Duk shi kadai?” Mayraah tace “Wallahi, just my few days in that hospital the experience was horrible, har bana son tunawa, wilh he is rude Yaya” Maheer na gyada kai yace “I trust you idan ya maki interview din ma you will only leave him with mouth agape, did u know that ur intelligence is extra ordinary lil sis? I am always amazed with ur intelligence, you graduated with first class, nursing science, ai shima sai yayi mamakin result dinki wallahi, shi kansa ba lallai yayi graduating da first class ba idan nursing science yayi….” Mayraah dai sai murmushi take saboda kodatan da yayan nata yake, kafin su isa kaduna Badiyya tayi amai yafi a kirga, suna isa kofar gidan Yahanasu Badiyyah ta fashe da kuka a galabaice, Maheer dai ya sauka ya fiddo mata akwatinta ya kira almajiri, jikin Mayraah yayi sanyi ta kasa sauka daga cikin motar, nan da nan hawaye ya cika idonta, Maheer ya bude ma Badiyyah bayan motar yana kallonta yace “Sauko” Saukowa tayi tana kuka sosai tace “Yaya don girman Allah ku taimakeni ku rufa min asiri, bani da kowa….” Maheer ya katseta yace “Ва Ammi tace maki tafiya za su yi ba, in kin shiga ciki sai ki gaya masu, duk sanda ta dawo sai ki koma kanon ai” Daga haka ya kulle motarsa ya zaga ya shiga driver seat, hawaye kawai Mayraah take tana kallon Badiyyah dake kuka kamar ranta zai fita, Maneer ya ja motarsa ya bar kofar gidan.

Sai kusan karfe hudu Mayraah suka iso kano daga kaduna, Mayraah ta kalli Maheer tace “Alhamdulillah for journey mercies” Kai kawai ya gyada mata, tace
“What should I cook for u idan muka isa gida, kaga kai baka ci abinci ba, ni kuma ka siya min a Zaria” Ya dan kalleta yace “Baki gaji ba?” Er dariya tayi tace
“Bayan ba nice ke driving din ba, i slept all through fa” Ba don yayi missing girkinta ba da bazai bari tayl girkin ba but he is craving her cooking, jin yayi shiru yana driving dinsa tace “Ko baka so?” Yace “Gani nake za kiyi stressing kanki after this long journey, kamata yayi muna komawa gida yanzu kiyi wanka kiyi sallan Asr ki kwanta ki huta” Mayraah ta dan vi murmushi bata ce masa komai ba, ya juya ya kalleta jin tayi shiru, sai kuma ya maida dubansa kan titi yace
“Ko ba haka ba Mimi?” Tayi wani murmushin tace
“Naga kamar u are avoiding me this days, baka son muna magana da yawa, i don’t know! u are just being unusual, we weren’t like this before” Maheer ya buda ido sosai, babu abinda ya fado masa rai sai lokacin da ita ma ta dinga kokarin avoiding dinsa 3 months back after finding out they are not blood, yasan she is talking about kafin su san matsayinsu ne, yana murmushi yace “Avoiding my lil sis? Kema kin san hakan bazai yiwu ba…” Tace “Then if u are not avoiding me kana da damuwa ne da baka son ka gaya min?” Ya dan kalleta yayi murmushi yace “You caught me” Tace “I definitely know there is something, yaya na fa san ka nasan halin ka, i know there is something bothering you, amma shine kake boye min whereas before baka boye min komai” A hankali yace “I will tell u Lil sis, but yanzu ina bukatar in huta na gaji” Tace
“Tohm shikenan, and again yaya me yasa baza ka dau transfer ba kai ma ka koma Abuja, naga kuna da Branch a can ai” Maheer yace “Kin manta daga
Abujan na nemi transfer na dawo kano, it will be a bit hard to get another transfer back to Abuja” A hankali tace “Try yaya, we will miss u idan muka tafi ba tare da kai ba, kaga shi Ya Usman dama yafi aiki a Abuja and kaduna, nasan he is going back to Abuja too” Maheer yayi murmushi yace “I will try” The rest of the journey was silent har suka iso gida, bayan yayl parking tace “Idan nayi sallah zan maka girkin” Yace
“Toh Nagode Mimi” Tayi murmushi ta bude motar ta sauka ta nufi cikin gidan. Mayraah na shiga parlon Ammi ta tadda Mama Ladi kwance ta lullube da bargo, Mayraah ta karasa kusa da ita ta duka tana kallonta da mamaki tace “Baki da lafiya ne Mama?” Mama Ladi tayi kasa da murya tace “Ae tun asuba da na tashi naji kafafuwana sun kasa daukata nasan da matsala, to ilai kuwa gashi” Mayraah tace “Ayya, to Allah ya sauwake, kin sha magani?” Mama Ladi tace
“Wa zai bani er nan? Ai yanda kika gan ni a nan tun dazu a haka nake” Mayraah tace “To zuwa anjima sai in fita in amso maki maganin idan nayi sallah” Daga haka Mayraah ta mike ta karasa dakin Ammi, kaya ta sameta tana ta hadawa a akwatuna, Ammi tace “Ya hanya Mimi?” Mayraah tace “Alhamduillah, ina yini Ammi” Ammi tace “Lafiya lau, ina yayan naki?” Mayraah tace “Kamar ya shiga gida” Ammi tace “Toh kiyi sallah ga abinci can na maku ki duba kitchen” Mayraah tace “Toh Ammi” Ta juya ta nufi kofa Ammi tace “Ki fito da kayanki gaba daya daga press din dakin ki ajiye kan gado, zan jera maki a akwati, amma sai kin ci abinci in kinyi sallah” Mayraah tace “Toh Ammi” Daga haka ta fita daga dakin, tana komawa dakinta tayi wanka sannan ta dauro alwala, bayan ta idar da sallah ta sauka downstairs ta shiga kitchen, duba abinda Ammi ta girka masu tayi, sai kuma ta fita ta koma ta dauko wayarta ta dawo parlon ta zauna tayi dialing number Maheer, yana fara ring Maheer dake kwance ya mike zaune ya daga yace “Mimi” Tace “Yaya me kake son ka ci?” Yace “Koma me kika girka zan ci” Tace “Ohk” Daga haka ta katse wayar, Haseenah dake kitchen din dake Chalet zata zubo masa abinci duk da tasan ba ci zai yi ba, tana jin wayar da yayi da Mayraah ta dan yi wani murmushi ta mayar da abincinta cikin warmer ta fito daga kitchen din ta wuce daki, dama girkin da Ammin tayi ne taje kitchen ta debo ba wai ita ta girka ba, Mayraah na kitchen tana ma Maheer girkin da tasan ya fi so wajen karfe biyar da wani abu aka bude kofar kitchen din ta juya, suna hada ido tace “Ina yini Yaya” Yace “Lafiya lau” Karasawa cikin kitchen din yayi yace “Babu abincin ne?” Tace “Aa akwai, Ya Maheer nake ma girki” Ya gyada kai ya dau plate zai debi abinci tace
“Ko zaka ci wannan da nake yi” Yace “Aa akwai me shi ae” Tayi dariya tace “Ai zan iya tsam maka kadan a ciki” Bai sake kallonta ba ya debi abincin da zai diba ya fita daga kitchen, Ammi na shigowa kitchen zata hada ma Mama Ladi shayi tace “Mimi baki son abincin ne?” Mayraah ta kalleta tace “Aa Ammi yaya nake girka ma favorite dinsa” Ammi tace “Tohh ai shikenan nawa bai yi dadi ba kenan” Dariya Mayraah tayi tace “Aa ko dandanawa bai yi ba fa Ammi, kawai favorite dinsa nake masa saboda nasan ya gaji” Murmushi kawai Ammi tayi, ta hada shayin da ya shigo da ita ta fita daga kitchen din, Mayraah na gamawa ta fito parlor ta dau wayarta tana kallon Usman dake zaune kan kujera yana kallo a laptop, Maheer ta kira ta sanar masa ta gama, a hankali yace
“Ki kawo min nan Chalet Mimi” Ta dan buda ido tace
“Chalet kuma? Aa yaya kawai ka daure ka zo ka amsa” Yace “Na gaji ne” Ta dan yi shiru, sai kuma yace “Ki bar shi kitchen din idan na shigo zan dauka” Tace “Bari in kawo maka yaya” Daga haka ta ajiye wayar ta nufi kitchen, Usman ya bi ta da kallo, daukan abincin tayi ta dawo parlor tace “Yaya kace baza ka ci ba ko?” Yace “Eh” Kofa ta nufa ta fita zuwa Chalet, tana knocking kofar yace “Come in” Ta bude ta shiga sannan ta karasa inda yake kwance, tun da Haseenah ta ji yayi waya da Mayraah ta kawo masa abinci ta sake fitowa Parlon ta zauna, Mayraah bata yarda ta kalli direction dinta ba balle har hakan yasa sai ta gaisheta, she pretends bata ma san tana wajen ba a zaune, tana ajiye masa abincin tace “Ga abincin yaya” Yace “Thank you Mimi” Tayi murmushi ta mike ta nufi kofa ta fita, Haseenah ta bi ta da ido. Ko da Mayraah ta koma sama ta tarar Ammi na ta hada mata kayanta cikin set din akwatunanta, Mayraah tace “Ammi ki bari in karasa” Ammi tace “Aa bar shi ai na kusa gamawa kije kiyi alwala kawai, it’s almost Magrib” Bandaki Mayraah ta shiga don yin alwala…. Da daddare Ammi na dakinta tare da Mayraah, Mama Ladi kuma na kwance har sannan cikin bargo Maheer ya shigo parlon, ya zauna ya gaida Mama Ladi ta gyada masa kai kawai, yace “Mama ba lafiya ne?” Mama Ladi tace “Ai tunda na tashi da asuba na ji jikina na rawa nasan da magana, to ilai ga ni nan rai a hannun Allah” Maheer yace “Subhanallah, to kin sha magani?” Mama Ladi tace “Mera ta samo min wani gantalalle na hadiya dazu, amma ba sauki” Maheer yace “Zuwa karfe sha daya kafin kiyi bacci sai ki kara sha, in sha Allah za ki ji sauki” Daga haka ya mike ya karasa Bedroom din Ammi yayi sallama, sai da ta amsa ya shiga, Ammi tace “Ya gajiyan hanya?” Ya zauna yace “Alhamdulillah, ina wuni” tace “Lafiya lau” Wayarsa ya mika mata yace “Aunty Mariya zata maki magana” Sai da gaban Ammi ya fadi, tun barin su kano da safe ta kashe wayarta har yanzu ta ki kunnawa, dazu ma sai wayar Usman ta amsa ta kira Abba, Ammi ta amshi wayar, yace “Ki kirata” Daga haka ya mike ya fita daga dakin, Ammi tayi dialing number Aunty Mariya yana fara ring Aunty Mariya ta daga, Ammi tayi mata sallama, Aunty Mariya ta amsa ta gaisheta sai kuma ta ja wani dogon numfashi tace
“Ammi Hajja fa tana gidana yanzu haka” shiru Ammi tayi don tasan kwanan zancen dama, Aunty Mariya tace “Yanzu fisabilillahi ina take son Badiyyah ta tafi?
Ta dai san ba zaman kanmu muke ba balle ace lallai mu rike Badiyyah a wannan halin da take ciki, wata dayan da tayi gidanki ma abun a jinjina ma Alhaji ne wilhi, Sanda muke kokarin saita Badiyyah ba duk ita ke tabarbara komai ba take goyon bayanta akan duk wasu mugayen halayyan da take, saboda me kuma yanzu har da ita a gudun Badiyyah? Ai in kowa ya guji Badiyyah to banda Hajja tunda ita ce root din duk abinda ya samu Badiyyah” Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace “Ban san me zance ba Mariya, bana son magana shi yasa ma kika ji wayata a kashe, i am tired wilhi” Aunty Mariya tace “To kuwa wallahi Baaba Yahanasu bazata yarda a makala mata Badiyyah ba tana fama da kanta tunda ga Hajjan har ta bar gidan ta dawo nan, ina me tabbatar maki in dai Baaba Yahanasu ce gobe zata kamo hannun Badiyyah ta kawo ta gidan nan ba wai karamin aikinta bane, kuma Ammi kece babba ke ya kamata ki gaya ma Hajja bata da wani Hujjan gudun Badiyyah don ita ce silar duk abinda ya sameta, wallahi ita ce sila, da ta bar mu mun mata tarbiyan da ya kamata da duk haka bai faru ba amma tayi kane kane kan lamarin Badiyyah tana ga kamar ba sonta muke ba, ta dauki kalman maraici ta hure kunnen yarinyar da shi yarinya tayi ta iskancin da ta ga dama babu me ce mata don me, kuma yanzu tace bata da makiyiya sama da Badiyyah, ai bazai yiwu bane, a gabanta ya kamata Badiyyah tayi jinya ba a wani waje ba” Ammi tace “Rufa min asiri, kema zaki iya gaya mata hakan Mariya ba kince tana gidanki ba, sai ki buda mata komai babu boye boye” Aunty Mariya tace “Wai kin ma ji maganganun da ta dinga yi ne ma kuwa, cewa tayi fa mun tura Badiyyah gidan Yahanasu ta karasa ta, idan bamu yi hankali ba wallahi Nijar zata shiga gun er uwarta, wai Bilkisu ce er uwarta yau, ni gaskiya ina ga zan kira kawu Rabi’u in sanar masa duk abinda ke faruwa, kawai Hajja tayi hakuri ta rungumi kaddarars ita da Badiyyah ta dauketa su koma kaduna su ci gaba da zamansu har Allah ya sauketa” Ammi tace “Kirasa ki sanar masa….”
Aunty Mariya tayi mata sallama ta katse wayarta.
Washegari Mayraah ta shirya da wuri zata shiga school ta amso statement of result dinta, flight din nasu na karfe hudun yamma ne, so bata san how long zata gama clearance before collecting the result statement ba shi yasa ma ta shirya da wuri, tana shiga parlon Ammi ta tadda Usman zaune yana kallon Mama Ladi dake hadiyan paracetamol, ta karasa ta duka gaban Mama Ladi tace “Ina kwana Mama?” Mama Ladi tace “Ke ban cika son magana ba fa” Mayraah tace “To Allah ya sauwake” Kallon Usman dake kallonta tayi tace “Ina kwana?” Yace “Ina za ki je?” Tace “Zan shiga School inyi clearance ne sai in amshi statement of result, ko zaka yi dropping dina yaya?” Ya mike yace “Mu je” Tace “Toh bari in gaya ma Ammi” Daga haka ta shiga dakin Ammi shi kuma ya fita daga parlon, Usman na dropping dinta a school din yace “Ki kirani idan kin gama” Tace “Toh” Daga haka ya bar school din, sai kusan karfe sha biyu Mayraah ta amshi result din nata sannan ta kirasa, bai wani bata lokaci ba ya shigo school din ya dauketa suka koma gida. Maheer na zaune parlor wajen karfe biyu yana jiran Ammi da ta kirasa sai ga ta ta sauko downstairs, ta zauna tana kallonsa tace “Maheer ya zan yi da wancan tsohuwar?” Maheer ya dan yi dariya yace “Wai har yanzu tana kwancen ne?” Ammi tace
“Wallahi sai kara lullubewa take fa” Maheer yace “Kar ki damu ku dai ku shirya nan da karfe uku sai in kai ku airport din nasan yanda zan yi da ita” Ammi tace “Toh shikenan” Daga haka ta mike ta wuce sama, karfe biyu da rabi Maheer ya shigo bangaren Ammi, har sannan Mama Ladi na kwance cikin bargo, Maheer na kallonta yace “Sannu Mama” Ta gyada masa kai kawai, yace “Ko za mu koma can bangaren ne Kinga za su tafi airport ne yanzu” Mama Ladi ta ki kulasa, yace “In kuma kin fi son nan din to….” A mugun fusace tace “Kai dalla rabu da ni inji da cutar dake damuna, ko don ba kai ne ke jin jiki ba?” Maheer yace
“Shine nace ma Ammi da naga ta dage a tafi Abuja dake nace mata baxa ki iya ba kina jin jiki, zaman jirgi sai me lafiya…” Mama Ladi na kallonsa tace “Ni muka yi haka da kai Mashir?” Maheer yace “Toh ai basa barin mara lafiya ya hau jirgi shine dama matsalar” Mama Ladi ta mike zaune tace “Ciwon kan ne ma kawai ya saka ni gaba amma ni kaina nasan jikina da sauki bana jin komai wallahi” Maheer yace “Sai dai in zan tafi mu je tare, tun da kin ga sati daya ake dauka kafin mutum ya samu kujeran jirgi don ba kullum jirgin ke tashi ba, wannan ma sai da Abba yayi sati biyu yana bi sannan ya samar masu kujeran” Mama Ladi ta koma ta kwanta, Mikewa yayi ya shiga dakin Ammi dake sauraronsu, yayi murmushi yana kallon Ammi yace “Bari in fita da akwatunan” Ammi dai bata ce komai ba tana mamakin Mama Ladi yanzu kawai sai ta kara kwasan jiki ta bi su Abuja, ina laifin ma ta bari sai bayan kwana biyu haka da komawars in ma zuwa zata yi, ai sai abun ya zama rashin hankali kuma, tun bikin Maheer fa take gidan, har Maheer ya kai akwatunan mota Mama Ladi na kwance ta maida bargon gefe daya, Ammi ta fito daga dakinta don karfe ukun ya kusa ta zauna tana kallon Mama Ladi tace “Toh Mama za mu tafi, idan ya so in Maheer zai je sai ku taho tare tunda kujera biyu kawai Abbansu ya samu…” Mama Ladi tace “Ai shikenan, banda ma jikina ya matsa min ai tun a shekaranjiyar nayi niyyar tafiya karaye, to kana naka ne Allah na nasa, ban yi zaton zan kai har yau a gidan nan ba” Ammi tace
“Haka ne kam, sai kun zo din dai, bari in je kar mu rasa jirgin” Mama Ladi bata kara tankata ba har ta fita daga Parlon, Maheer ya kai su airport din tare da Mayraah, bayan sun shiga departure ya koma gida….
Karfe biyar suka sauka airport din Abuja, sabon Driver da Abba ya dauka ne yaje airport din daukosu. Ammi bata taba zaton irin gidan da Abba ya siya ba kenan a Abuja, she never expect it, mansion ne na gani na fada a anguwa me kyau, kai kana ganin gidan kasan account yayi bala in girgiza, ga masu gadi biyu da ya saka a gidan da driver daya, har da me watering flowers da sharan babban compound din, abu daya ne babu a gidan wato swimming pool cause it won’t be of any use to them, tsabar farin ciki sai da Ammi tayi hawaye bayan ta shiga part dinta it was something she never saw coming, Bedroom din Mayraah yayi biyun wanda ta bari a kano, bandakin ma was very big, dakuna sun wadata sosai a gidan, tun daga sama har downstairs, wajen karfe shidda Abba ya shigo gidan don yana Abujan, Ammi na zaune Bedroom dinta ta ma kasa yin komai sai kallon Mayraah dake jera mata kayanta a press take, Abba na shigowa dakin yana kallon Ammi yace “Me ya samu wayarki ne” cikin sanyin murya Ammi tace “Ban cire a flight mode ba” Mayraah ta gaida Abba, Abba yace “Kema na kira baki daga ba” Mayraah tace
“Yana cikin handbag dina” Abba yace “Ohk” Mayraah na murmushi tace “Abba the house is so beautiful Allah ya sanya alkhairi, Allah ya kara maka budi da daukaka, Allah ya sa kafi haka” Abba ya dafa kanta yana murmushi yace “Ameen my Baby gal, hope u are prepared for ur interview tomorrow?” A hankali Mayraah ta gyada masa kai, yace “To maa sha Allah, i know u can do it, congratulations in advance daughter” Tana murmushi ta fita ta bar masu dakin, nan da nan hawaye ya cika idonta, tana komawa nata dakin ta fashe da kuka sosai, she knows she can never pay them in anyway, bata ta taba iya biyan duk abinda suka mata a rayuwar nan ba, even if she will how is she going to repay all this? with what will she repay? because of the genuine love they have for her they still have to relocate back to Abuja for the sake of her new work, Bayan Mayraah ta fita dakin Abba ya kalli Ammi da ta kasa dago kanta yace “Gidan ya maki ko a canza yan mata?”
Washegari karfe bakwai na safe Mayraah ta tashi ta sauka downstairs zuwa kitchen don girka masu
Breakfast, babu abinda babu a kitchen din na foodstuff, bayan ta gama girkin ta kai dinning table ta jera kan table din, Ammi ce ta sauko downstairs Mayraah ta karasa ta gaisheta da ladabi, Ammi tace
“How was ur night?” Tace “Alhamdulillah, Ammi ga breakfast na gama….” Ammi tayi murmushi tace “To sannu da aiki daughter, shiryawa za ki je kiyi yanzu ko? naga karfe takwas ya wuce kar ki makara”
Mayraah ta gyada mata kai tace “Eh yanzu zan je in shirya” Ammi tace “To kiyi maza” Mayraah ta wuce sama don yin wanka, sai karfe tara ta sake saukowa downstairs sanye cikin black Abaya da handbag dinta sai envelope me dauke da credentials dinta, har ta mance rabon da ta sa Abaya sai Hijab, she look so cute and stunning kuma Abayan ya haska farin fatarta ta dawo kamar wata balarabiya duk da bata yi make up ba sai eye pencil da ta sa a ido, da lip gloss da ta goga a lips dinta, Ammi da Abba na dinning area ta samesu, Ammi na ganinta dama ta fara hada mata tea, Mayraah ta durkusa ta gaida Abba ya amsa da murmushi yace “Kin tashi lafiya?” Tace
“Alhamdulillah” Yace “You look cute my dear”
Mayraah tayi murmushi tace “Thank you Abba” Ammi ta nuna mata kujera tace “Zauna kiyi breakfast, u are already late” Mayraah ta mike ta zauna sannan ta dau shayin da Ammi ta hada mata, Ammi ta ajiye mata plate din irish a gabanta, tace “Amma after the interview za ki dawo ai, nasan ba yau za ki yi resuming aikin ba dai” Mayraah ta gyada mata kai, Ammi tace “Sai dai a samu food warmer ki dinga tafiya da abinci saboda lunch” Mayraah ta zaro ido ta turo baki tace “Food warmer kuma Ammi kamar er yarinya” Ammi tace “To da yunwa zaki je kina aikin, don nasan ba siyan abinci zaki dinga yi ba”. Mayraah tace “To ai har na gama school bana zuwa da abinci fa” Abba dai yayi murmushi yace “In bazata dinga zuwa da shi ba sai drivern ya dinga kai mata abincin da rana kawai” Mayraah dai bata sake ce masu komai ba a ranta kuwa har ta gama deciding in dai drivern za a ce ya dinga kai mata abinci kawai ce masa zata yi yana fitowa ya cinye a hanya ya koma gida da warmer din don babu abinda zata yi da abinci a wajen aiki kamar wata baby, Tana gama breakfast din ta mike zata kai plate da cup din kitchen Ammi tace “Aa bar shi, lokaci ya wuce” Abba yace “Driver zai yi dropping dinki a asibitin, jiya a airport ai wayarki ya kira yaje ya dauko ku so i assume you have his number idan kin gama abinda kike yi sai ki kirasa yaje ya dauko ki, he is ur driver from henceforth” Mayraah tayi murmushi a hankali tace “Nagode Abba” Abba yace “You are welcome dear” Sallama tayi masu ta dau jakanta da Envelope, Ammi ta mike tace “Kiyi addu’a kafin ki fita” Mayraah ta gyada mata kai, har bakin kofar Ammi ta rakata tace “Allah ya bada sa’a daughter, stay safe pls” Mayraah ta ciro black glasses dinta ta saka tace “Ameen Ammi, in sha Allah” Murmushi Ammi tayi tace “Yau dai gayu kike ji daughter” Er dariya tayi ta fita compound din taga driver zaune yana jiran ta, ya sauko da sauri ya gaisheta da ladabi, maimakon ta amsa sai ta gaishesa ita ma sannan ta bude front seat ta shiga don bazata zama comfortable tana baya yana driving dinta ba, bayan sun bar gidan ganin ya kama hanya bai tambayeta inda zai kai ta ba sai kawai ta gaya masa, yayi kasa da kai yace “Ranki shi dade ai Alhaji ya sanar min tun a jiya, nasan asibitin ma, da yake na taba yin aikin Uber” Mayraah tace “Ohk” Agogon wrist dinta ta duba taga karfe tara da rabi, tafiyar minti talatin suka yi zuwa asibitin, Mayraah na fara hango babban building din hospital din ta ji gabanta ya fadi, yanzu zata je ta had da wancan jarababben mutumin ita wallahi ko irin farin cikin ta samu aiki a asibitin ma bata yi, she is not even excited don gaba daya ya sa taji bata son asibitin a ranta but bata son tayi shunning effort din Dr Khalil ga kuma Abbanta dake ta farin cikin ta samu aiki da ma brothers dinta, wnn ne kawai ya hanata cewa bata son aikin tun a kano, bayan drivern yayi parking dan gaba da gate din asibitin don kar yayi hindering masu shiga da mota, Mayraah ta bude motar ta sauka tace “Nagode, idan na gama zan kira ka” Yace “Toh Hajiya Allah ya bada sa’a” Tace “Ameen” Tana juyawa ta ga wani lafiyayyen mota ya taho zai shiga asibitin, tuni masu gadi suka bude gate din suka daga karfen gaban gate din inda motar zata wuce, bata ga wanda ke cikin motar ba don tinted glass ne, bayan motar ya shiga ta bi ta inda ake bi a shiga cikin asibitin da kafa, tana tafiya a hankali, Tana shiga reception din ta gaida nurse din dake wajen sannan ta tafi sama not minding yanda aka bi ta da kallo, ko basu ganeta bane oho, office din Dr Khalil ta nufa duk da bata ga motarsa ba a parking space, knocking tayi to be sure if he is around ya mata izinin shigowa ta bude kofar, yana ganinta ya mike tsaye cause da farko bai gane ta ba yace “Mayraah…” Ta dan yi murmushi ta karasa tace
“Ina kwana” Yana gyada kai yace “Lafiya lau, ashe haka kika iya gayu, ai ni ban gane ki ba wallahi” Murmushi kawai tayi ta zauna, yace “Maa sha Allah, you look cute, jiyan ku ka shigo kenan?” Mayraah ta gyada masa kai, yace “That’s good, Jiya Ceo ma ta shigo kasar, i think she will be around today kinsan gobe za mu je workshop din lagos” Mayraah tace “Oh ok, ya twins?” Yace “They are fine Alhamdulillah, are you together with the credentials?” Ta gyada masa kai yace “Ohk let me have a look first” Mika masa Envelope din tayi, ya amsa yana ciro takardun ciki yace “MD din ma yana nan ai, tare muka shigo dazu, sai da naje na daukosa a motar sa, shi yasa ban ma zo da tawa motar ba….” Statement of result dinta ya fara dubawa, ya dinga kallon result din babu ko Kiftawa, can ya nemi kujera ya zauna ya kalleta ya buda ido sosai da mamaki yace “Really?” Ita dai Mayraah tayi shiru bata ce komai ba, buda baki yayi yace “First class?” Still ta ki ce masa komai, Yace
“Ikon Allah.. this rare, are you this intelligent Mayraah? I am really surprise wallahi” Mayraah ta dan masa murmushi kawai, ya gyada kai yace “Maa sha Allah, i am really impressed, ai duk nan ina ga banda MD we don’t have any staff with first class na degree…” Sai kuma ya fara dariya kamar wanda ya tuna abu, Mayraah dai taki ce masa komai har da dan daure fuska, Dr Khalil ya duba other credential din nata sannan ya maida su cikin Envelope yana murmushi yace “Za mu shiga theatre nan da minti talatin, bari in samesa if u can go for the interview now, don banda shi za mu shiga theatre din” Mayraah ta gyada masa kai tace “Ohk” Ajiye envelope din yayi ya fita office din zuwa office din MD, a long pavement din saman ya samesa ya fito daga office din CEO walking towards his office, Dr Khalil ya jirasa
har ya iso MD yace “3 nurses, 5 Dr’s for tomorrow’s workshop, zaka yi booking flight din yau, 10 ticket in all” Dr Khalil dai na biye da shi har suka shiga office dinsa, MD ya zauna letting out a sigh yace “Yanzu zaka ga ta sake biyo ni nan” Dr Khalil yayi dariya yace
“Amma ana gama workshop din zata koma ne?” MD bai ce masa komai ba ya mike ya dau tea cup dinsa ya tafi ya wanke ya dawo ya zauna yace “Nan da sati biyu ne Conference din da tace a England ai, or is it even US, na dai manta” Har ya bude flask din sai kuma ya sake kallon cup din ya mike ya tafi ya kara wankewa ya dawo, Dr Khalil yace “Ohk ku biyu za ku yi attending Conference din kenan?” MD yace “No pls… Dr Balogun should go” Dr Khalil yace “Kai ma kasan she can’t do without u in anything ai” MD ya kalli wayarsa dake ring ya dauka yayi picking call din ya kai kunne, cikin minti biyu ya gama wayar ya ajiye, ya kalli Dr Khalil yace “What were u saying?” Dr Khalil ya kalli agogon office din saboda theatre da za su shiga he is cautious of time, MD ya sake tashi ya tafi ya wanke tea cup din hannunsa ya dawo, kiran Ceo ne ya shigo wayarsa ya zauna ya daga yana sauraronta, sai kuma yace “Ohk ma, i will bring them in 30 mins time” Bayan ya katse wayar ya tashi ya sake wanko cup din ya dawo, Dr Khalil ya tabe baki ya mike yace “Are you ready? Za ta shigo interview din yanzu, cause she is around” MD ya daga kai ya kallesa, sai kuma ya hade rai yace “Waye haka?” Dr Khalil yace “You insisted she should come for the interview last week, so she is around today” MD yace
“Ohh shine yasa CEO ke tambayana ita da naje office dinta yanzu kenan, ashe ta ganta ne, ita dai ta dage lallai sai tayi aiki a asibitin nan, ko dai mayya ce yarinyar nan?” Dr Khalil yace “Ga dai ta nan with her credentials kamar yanda ka bukata, so i will send her right away, don ni zan shiga theatre” Ko tankasa MD bai yi ba ya sake tafiya ya dauraye cup da zai sha coffee, kafin ya dawo har Dr Khalil ya fita daga office din, yana komawa nasa office din ya kalli Mayraah yace “You can go to his office, but piss Mayraah be a good girl, kiyi abinda ya kamata he is our boss, and he is employing you, speak to him with respect and calmness, kalmominki kar su wuce Yes sir, Ok sir, sorry sir, thank you sir” Murmushi Mayraah tayi tana kallonsa ta rasa dalilin da zai dinga cewa she should be a good gal in zata je gun jarababben mutumin can, to tayi kama da bad girl ne? Ta sunkuyar da kai tace
“Toh Dr” Yace “You can go now, yana jira” Mikewa tayi ta dau jakarta da Envelope din takardunta, ga cire glasses dinta zata saka a jaka, Dr Khalil yace “Me yasa kika cire, ki maida abun ki” Mayraah ta kallesa yace “Ki sa mana, ai ya maki kyau” Dan murmushi tayi ta maida glasses din sannan ta nufi kofa, har ta rike handle din sai kuma ta juyo tana kallonsa a hankali tace “But do u have any idea akan abinda zai tambayeni” Dr Khalil yace “Ki kwantar da hankalinki and be calm, ba wani tambayar da zai maki na sani, kawai zai duba takardunki sai kuma ya tambayeki informations dinki to be imputed, yana ganin result din ki ma nasan sai ya rasa tambayar da zai maki don mamaki…. So just go” da murmushi ya kare maganarsa, Mayraah ta sauke idonta kasa ta juya ta fita daga office din, last floor ta tafi zuwa office din MD, gently tayi knocking kofar har sai da ya amsa sannan ta bude ta shiga, Coffee dinsa yake sha bai kuma daga kai ba balle ya kalleta, ta karasa har gaban table dinsa ta tsaya calmly tace “Good morning sir” Dago kai yayi, kiris ya rage ya saki cup din coffee din hannunsa don har sai da ya dan zube masa a white shirt dinsa, mikewa yayi da sauri ya ajiye cup din yace
“Kee, why will u just badge into my office are you okay? Ance maki kasuwa ne nan?” Bai jira me zata ce ba ya shige Bedroom dinsa dake office din, Mayraah ta bi sa da kallo, can ta tabe baki a ranta tace kilan dai Dementia garesa, cause sai da tayi knocking ya bata permission din shigowa kafin ta shigo, tana ta tsaye har ya fito bayan minti biyar with another white shirt, ya wani daure fuska kamar bai taba ko murmushi ba, ita dai bata yarda ta kallesa ba har ya karaso table dinsa ya dau cup din coffee din ya tafi ya zubar ya dawo, still yaki kallonta yace “Me kike jira har yanzu?” Calmly tace “I came for the interview u ask me to come for, here are my credentials” Bata jira me zai ce ba ta ajiye envelope din kan table dinsa sannan ta koma gefe ta tsaya, yace “Ohk shi Khalil din ne yace maki kina zuwa ki ajiye CV din kan table dina?” Mayraah bata ce komai ba, ta dau envelope din ta nufesa ta tsaya a gabansa tana mika masa while looking at him, kin yarda ya kalleta yayi may be he wasn’t expecting that, kawai taga ya bar wajen ya koma seat dinsa ya zauna, ta juya tana kallonsa still ya ki kallonta, kwankwasa office din aka yi, ya mike da sauri duk tunaninsa Ceo ce, Dr Balogun ya bude office din ya shigo da wani file, yana ganin Mayraah yace “Ohh Madam, where have u been all this while?” Mayraah ta gaishesa da ladabi, ya amsa da hausansa irin na yoruba yace “Kwana biyu baki zo aiki ba, ina kika tafi?” Mayraah ta dan yi murmushi tace “Ya ce in zo interview ne tukunna kafin in ci gaba” Dr Balogun ya kalli MD that was unnecessary clearing stuffs off his table, Dr Balogun yace “Ohk MD in je in dawo kenan after the interview, dama akan aikin da za mu yi da daddare ne…” Sai a sannan MD ya daga kai a takaice yace “You can interview her Balogun, i am a bit busy…” Dr Balogun ya kalli Mayraah yace “Are you with ur CV?” Ta gyada masa kai ta mika masa Envelope din hannunta, zaunawa yayi kan kujera ya nuna mata kujeran dake kallon wanda ya zauna yace “Sit…” MD yace “Why should she sit? She should take off those glasses we are not doing fashion here” Dr Balogun ya kalli Mayraah da ta cire glasses din idonta, sai kuma ya fara fiddo da takardun, Mayraah ta wani harari MD dake kallonta ta gefen ido, Statement of result dinta Dr Balogun ya fara dubawa, sai kuma ya kalleta da sauri yace “Waow, first class from this prestigious university? It’s my alma mater also, nasan lecturers dinku sosai” Mika ma MD yayi, MD dake kallonsa yace “First class in Botany or what?” Dr Balogun ya zaro ido yace “Nursing Science Malam, ina jin fa department din nan rabon da a fita da first class zai kai shekara sha biyar ko ma ya fi, and she just graduated” MD dake ta kallonsa yace “Nursing Science?” Dr Balogun yace “Gashi ka duba” MD ya girgiza kai yace “Wani makaranta ne?” Dr Balogun ya gaya masa, MD yace “That’s a lie” Da mamaki Dr Balogun yace “Ka taba ganin anyi forging result a makarantar nan?” MD ya dau wayarsa yace “I have a frnd that is a Lecturer in the department, i will confirm it now” Shiru Dr Balogun yayi yana kallon MD da ya amshi result din yana dubawa sannan ya dau wayarsa ya fara dannawa, Ita dai Mayraah ko kallon inda yake bata sake yi ba, har cikin ranta bata taba jin ta tsani mutum irin yanda take jin tsanar mutumin nan ba, she detest him with passion, ji take kamar ta fice daga office din amma bazata yi haka ba sbda Dr Khalil, tana ta jiran taji ya kira wayar sai kuma bai vi ba, ya maida wayar ya ajiye yace “I will confirm that later, Dr Balogun you can leave, we will discuss the issue at hand later” Mikewa Dr Balogun yayi, har sannan kallon Mayraah yake don ko kadan bai ji shakkan result dinta ba, bayan fitar Dr Balogun ya jawo laptop dinsa after some minutes ba tare da ya kalleta ba yace “Ur name?” Sai a sannan Mayraah ta kallesa, a takaice tace “Mayraah Mahmud”. Ya hade rai ya kalleta yace “Kee sunanki zaki gaya min ba sunan gayunki ba, ko an gaya maki wajen wasa ne nan?” Tace “U can check the name in my result for ur self” ita kanta bata san sanda ta gaya masa haka ba, ya dinga kallonta, kawai ya rufe laptop dinsa yace
“Get out” Bude office din aka yi Ceo ta shigo, ya mike da sauri yace “U need something Ma?” Karasowa ciki tayi tana kallon Mayraah cikin sanyayyen muryarta tace “Hello, how are you, i just asked of u not long ago” Mayraah ta gaisheta da ladabi, MD dai kallonsu kawai yake, Ceo tayi mata side hug, sosai gaban Mayraah ya fadi, Ceo na kallonta with calmness tace
“Why are you not on scrub?” Mayraan ta kasa kallonta tace “I…” Sai kuma ta rasa me zata ce, Ceo ta kalli MD tace “Is there anything?” Da sauri yace “No, not really, just adjusting some mistakes in her data….
She is not on duty today” Ceo tayi murmushi tana kallon Mayraah a hankali tace “If he is done, Come make me coffee in my office Mary Ann” Mayraah ta gyada mata kai tace “Ok Ma” Daga haka ta ajiye takardun hannunta ta juya ta nufi kofa, Mayraah ta bi ta da kallo babu ko kiftawa, juyawa tayi suka hada ido da shi, Ikci daya ya mike ya dau wasu textbook zai kai Library dinsa na office din, tace “Can i take my leave?” Wani shegen kallo ya jefa mata, hakan yasa ta fara kokarin tattara takardunta yace “Hey get out” Juyawa tayi ta bar takardun ta fita daga office din…..
Mayraah na fitowa office din MD ta nufi office din Dr Khalil, zai fita suka hadu da shi a bakin kofa, yana kallonta yace “Har kun gama?” Mayraah ta tabe baki tace “Ni dai in kaje office din ka dauko min credentials dina pls” Dr Khalil na jin haka yasan an samu matsala, yace “Tell me, ya ku ka yi da shi?” Tace “Ni yanzu na fara masa uzuri gaskiya, kamar fa ba shi da lafiya ne, but seriously bai kamata ana bari yana fitowa gida a wannan yanayin ba, his parent are not doing him good” Dariya Dr Khalil yayi ba tare da ya shirya ba, Mayraah ta sauke ajiyar zuciya ta koma gefe ta tsaya, har a zuciyarta ta fara tunanin da gaske MD na da problem may be in his brain or so, to ko dai karatu ne ya fara taba masa kwakwalwa, Dr Khalil that was just laughing ya dake yace “Amma dai ya maki tambayoyin da zai maki?” Mayraah ta daga kai ta kallesa tace “He was just talking gibberish and finding fault where there is no fault….” Dr Khalil na murmushi yace “Za ki jira har mu fito theatre?” Mayraah tace “Zan je office din Ceo ne yanzu, i am dropping my handbag in ur office” Dr Khalil yace
“Kun hadu da ita ne?” Ta gyada masa kai tace “Ta shigo ne ta gan ni” Dr Khalil na murmushi yace “I love this bond that is forming gradually between u and Ceo, i like it, kuma fa bata da yarda matar, ke kuma gashi kamar taku ta zo daya, ko office dinta in ba MD din ba sai kilan Dr Ajay babu me zuwa, out of bound muke kiran wajen, you know she is so confidential…” Mayraan dai bata ce komai ba, ya mika mata makullin hannunsa yace “Idan kin ajiye jakan sai ki kulle min office” ta amsa tace “Ohk” Yana barin wajen ta shiga office dinsa ta ajiye jakarta sannan ta fito, ta kulle kotar ta tati sama zuwa office din Ceo, Dr Elliana Alfred… Haka Mayraah ta fada a zuciyarta bayan ta ga sunan manne jikin kofar office din, ta kai hannu zata yi knocking kofar kenan taga an bude, ido hudu suka yi da MD, ita ta fara sauke idonta ta bi ta getensa ta shiga cikin office din ta bar sa nan tsaye, kasa fita daga office din yayi, did he just open the door for this brat to come in? Kawai ya fice daga office din ya kulle kofar. Mayraah ta karasa har kusa da couch din da Ceo ke zaune da magazine a hannunta, har ta karaso kuma kallonta matar take, matar ta nuna mata inda zata tafi don making mata coffee din da coffee maker dake office din tace “The coffee maker is over there” Mayraah ta karasa wajen sai taga ba coffee powder a nan, dawowa tayl ta gaya mata, Ceo ta ajiye magazine din hannunta tace “Ki je office din Dr Aliyu ki amso, i took it home the last time i was here…” Mayraah tace “Ohk Ma” Daga haka ta juya ta fita, office din Dr Khalil ta tafi duk da tasan bazata gansa ba amma she wish he was there yaje ya dauko coffee din da kansa a wajen MD, ita dai bata son encounter da mutumin nan kwata kwata, avoiding dinsa ma ya kamata ta dinga yi don ta fara masa kallon mahaukaci, ganin babu wani alternative ta sake komawa sama zuwa office din MD din tunda babu yanda zata yi, tsaye tayi bakin kofar tayi knocking, taji yace “Who is there?” kawai ta bude office din a hankali ta shiga, tsaye ta samesa gaban table dinsa yana duba statement of result dinta, wasu takardu yayi saurin dauka a kan table din ya daura kan result din nata cikin few seconds, and she saw that, ta dai karasa cikin office din ba tare da ta bari ta kallesa ba tace “Ta ce wai ka bada coffee powder…” Shi ma without looking at her yace “Naga kamar kina nema ki dinga kawo min reni, don me za ki shigo min office kai tsaye kamar dakin ki? Are you okay?” calmly tace “I knocked first” ya kalleta a karo na farko fuska a daure yace “And who gave u the permission to come in?” Ita ma kallonsa take taki cewa komai, sai kuma ta hango coffee powder din da ya hada dazu a kan table dinsa, zagayawa tayi ta tafi zata dauka, ya bi ta da kallon mamaki, bayan ta dauka zata bar wajen bata lura da laptop dinsa da ke caji ba kawai katarta yayi tangling wayar chargern, force din ya jawo tsadadden laptop din tun daga kan table din har kasa, komawa baya tayi ta dinga kallon laptop din a tsorace, lokaci daya gabanta ya wani fadi, ta durkusa da sauri ta daga laptop din tana duddubawa, bayan few seconds ta mike tana kallonsa cike da karfin hali tace “I am.. am sorry….” Sai kuma ta ajiye laptop din tare da makullin hannunta ba tare da tasan tayi hakan ba kawai ta dau coffee powder din ta nufi kota ya bi ta da kallo, tana fita ta kulle office din ta sauke wani ajiyar zuciya har sannan gabanta na faduwa, ko dai bai ga abinda tayi ma laptop din bane, da sauri ta bar wajen ta koma office din Ceo, cikin minti kadan ta gama making mata coffee din, duk inda ta bi sai Ceo ta bi ta da kallo ta ma daina karatun magazine din da take, daga karshe Mayaah ta kai mata coffee din a Tea cup da saucer dinsa, Ceo ta nuna mata table din gabanta, Mayraah ta duka ta ajiye a hankali, Calmly Ceo tace “Thank you dear” Mayraah ta dan yi murmushi tace “You are welcome Ma” Ceo tace “Are your parent here in Abuja?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Yes Ma” Ceo tace “Mary Ann every movement of urs reminds me of my late friend, it’s been long i felt heartbroken this way, har na koma England kina raina ban san me yasa ba, i think i asked Aliyu about you twice or so” Mayraah ta sauke kanta kasa, wani bugawa zuciyarta yake da ita kanta bata gane dalilin sa ba, Ceo ta dauki cup din shayin tace
“You can take your leave, thank you dear” Mayraah ta kasa barin wajen, har sai da Ceo ta daga kai ta kalleta, sunkuyar da kanta tayi tace “But ma, kin ce za ki hada ni da relatives din friend din taki” Ceo ta dan yi murmushi tace “Sure i will, i am kinda busy now, gobe za mu je workshop Lagos, in 2 days time zan koma England ina da aiki a can” Mayraah ta gyada mata kai tace “Toh Nagode” Ceo tace “You are welcome” Daga haka Mayraah ta juya tana tafiya a hankali ta nufi kofa, matar ta bi ta da kallo babu ko kiftawa. Gaba daya Mayraah ta mance da batun makullin Dr Khalil har sai da ta sauko second floor ta lura she is not holding the key, nan hankalinta ya tashi don bata san inda ta bar makullin ba, ko a office din MD ko na Ceo, hango kofar office din tayi kamar a bude, hakan ya bata mamaki sosai ta dai karasa tana kallon kofar that was slightly opened, tura kofar tayi taga MD tsaye gaban table din Dr Khalil with her handbag in his hands, yana ganinta ya ajiye jakar keeping a straight face, ya kwashi wasu files kan table din Khalil, Mayraah ta kasa cewa komai don tsabar mamaki, to me yake nema a jakanta? Kofa taga ya nufo ta koma gefe tana kallonsa da mamaki tace
“Meye kake nema a jakana?” Yace “Ohh jakarki ne ashe, ai na zata na Khalil din ne” Daga haka ya fice daga office din ta bi sa da ido, da sauri ta tafi gun jakar nata ta bude tana duba ciki, wayarta ne a ciki sai Atm card da glasses dinta, with oil perfumes, to me yake nema, is he even okay? Zaunawa tayi still tana searching jakan har sannan mamaki ya kasa barin ta, kenan a office dinsa ta bar key din. Sai kusan karfe daya Dr Khalil ya shigo office dinsa, Mayraah ta mike tana kallonsa tace “Uhnn l’ve waited all day” Dr Khalil yace “Wallahi muna fitowa kuma MD ya kirani office dinsa, kin samu kin ci abinci ma kuwa?” Mayraah ta dau jakarta tace “Dama kai kawai nake jira driver har ya zo yana jirana a waje, idan naje gida zan ci” Yace
“Ohk, ina jin yayi imputing data dinki, so u are going to write me down ur account details, ur shift is from 8am to 6pm For now, resume work next week Monday” Mayraah na kallonsa tace “Ohk, thank you” Yace “Scrubs dinki kamar suna can gidan Ummi, so zan dauko maki a office din MD yanzu tunda kin ce driver yana jiranki….” Daga haka ya fita daga office din zuwa na MD, yana shiga MD dake tattara laptop dinsa da wasu textbooks yace “We are leaving together with Ceo now, idan an ajiyeta bazan dawo nan ba, sai after the workshop, na kai mata list din da muka yi creating na Dr’s da 3 nurses da za aje Lagos din gobe, pls ka taho min da motata gida anjima…
“
Dr Khalil yace “Kana gida ai da daddare?” MD ya kallesa yace “Ka manta za mu fita tare da daddaren zuwa hotel din da frnds dina turawa suka sauka, kasan ban cika son driving at night ba, sorry for always inconveniencing you pls” Dr Khalil yayi murmushi yace “Su abokan naka turawa me yasa basu sauka gidanka ba?” MD zai yi magana Ceo ta shigo da list din da ya kai mata tana mika masa ya taho ya amsa da ladabi, tace “I saw just 3 nurses in the list, why is that?” Ya sunkuyar da kai yace “We chose just them Ma’am” Tace “Why not make them 4, include Mary Ann to the list pls” Ya daga kai yana kallonta da sauri, sai kuma ya dan shafa kai yace “But Ma’am, babu ticket for that same flight… Sai dai wani jirgin, wannan da muka yi booking jirgin ya cika, sai ma da muka yi contacting dinsu suka soke wasu ticket din aka samar mana 10 din da muke bukata….
Dr Khalil ya saki baki yana kallon MD don ko booking ticket din basu kai ga yi ba tukunna, Ceo tace “Ohk, that’s fine” Daga haka ta juya ta fita daga office din, Dr Khalil na girgiza kai yace “Ka ji tsoron Allah Dr Aliyu, what’s there idan anje workshop din da ita, ai ire irensu ma ya kamata….” Dakatar da shi MD yayi yace “Baza ta je ba, yaushe ma aka bata cikakken aiki a nan din da zata je workshop din manyan likitoci a Lagos, wa enda suka yi shekara da shekaru a nan ma basu je ba sai ita mara kunya da ko fara aikin bata yi ba” Dr Khalil yace “Toh dai Ceo da kanta ai tace aje da ita kuma ta san sabuwa ce” MD yace “To ni kuma as the MD of this hospital nace banda ita, baxata je ba, kuma abinda baka sani ba ni ba full employment na bata a asibitin nan ba, she will just work as an Intern in here, not a staff, beside ko service fa bata yi ba daga amsan statement of result kawai sai aiki?” Dr Khalil yace “Thank God dai ba government hospital bane nan din balle kace, kuma wannan kamar bakin ciki kake mata….” MD yace “Shi din ne ma” Juyawa Dr Khalil yayi zai fita, MD yace “Book the flight immediately pls… 10 seats” Dr Khalil yace “Ohk” Daga haka ya fita ya kulle masa kota. Yana komawa office dinsa yace “Mayraah if it’s okay anjima idan na amso su daga gida Ummi ko da daddare ne sai in kai maki gida, cause kamar babu scrubs din available yanzu” Mayraah ta mike tace “Ohk nagode” Yace
“You are welcome, ki gaida su Ammi” Tace “Za su ji” Daga haka ta fita daga office din don tun dazu Drivernta ke waje. Wajen karte biyu Mayraah ta isa gida, tana bude kofar parlon ta ga Usman a zaune shi kadai, sau biyu yana daga kai yana kallonta wanting to be sure ita din ce, ta karaso parlon ta dan yi murmushi tace “Yaya yaushe ka zo?” Ya hade rai yace “Yaushe kika fara wannan dressing din in zaki fita?” Tayi kasake tana kallonsa, can ta zagaya inda yake zaune, ya dinga kallonta daga sama har kasa, tace “Yaya me ya faru da dressing din?” Yace
“Tambayata kike? Ok barin hijabs din naki kika yi a kano kenan?” Ta dan turo baki tace “Yaya Abaya ce fa ba wani abu ba, beside….” Calmly yayi shutting dinta yace “Keep quiet” Ammi ce ta fito daga kitchen ta tsaya tana kallonsu, A nutse yace “Kar ki sake wannan dressing din a gidan nan, were you trying to get someone impressed a hospital din?” Ammi tace
“Ban gane kar ta sake wannan dressing din ba, meye da shigar tata da bazata sake ba?” Ya dan daga kai ya kalli Ammi don bai ma san ta fito daga kitchen din ba, Mayraah dai sai turo baki take, can dai yace “To gidan biki za ta Ammi, haka ake zuwa interview dama?” Ammi tace “Aa ba ruwanka, let her dress the way she wants as far as ba wando ta saka ta fita ba, meye laifin Abaya?” Mikewa yayi ya bar parlon ya shige daki, Mayraah ta bi sa da kallo, Ammi tace “Rabu da shi ki tafi kije ki yi wanka ki sauko ga abinci na gama” Mayraah ta gaisheta a hankali sannan ta wuce sama, wajen karfe uku ta sake saukowa downstairs bayan tayi wanka tayi sallah sannan ta canza kayanta, dinning area ta tafi ta debi abincin da Ammi ta ajiye a nan, spoon daya ta ci, sai kuma kawai ta mike ta nufi dakin da taga Usman ya shiga dazu, a hankali tayi knocking kofar dakin, tana ta tsaye taji ya bude kofar ta daga kai tana kallonsa, sai kuma ta bi ta gefensa ta shiga cikin dakin ta juya tana kallonsa ta marairaice tace “Yaya did i dress indecent?” Kulle kofar yayi ya koma ya zauna, ta bi bayansa tana kallonsa, yace
“Amminki ta ce ba indecent bane… She gat your back” Murmushi tayi ta durkusa gabansa tace “Toh kayi hakuri yaya bazan sake ba, kuma ma ai uniform zan dinga sa wa ba kayan gida ba daga yau” shi dai kallonta kawai yake, ta mike tace “Have you eaten?” yace “Yeah” Tace “Toh zan je in ci abinci” Daga haka ta juya zata fita yace “Mayraah” Juyawa tayi ta kallesa, ba haka nan duk brothers dinta ke kiran sunanta kai tsaye ba, yace “In kin gama abinda kike yi da daddare ki shigo za mu yi magana” Da mamaki take kallonsa wondering maganar me za su yi, sai kawai tace “Toh in sha Allah” Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Bayan magrib Mayraah na zaune kan darduma wayarta ya fara vibrate ta dauko a zaton ta Maheer ne don tayi masa kira har biyu bai yi responding ba, Dr Khalil ne ke kiranta, ta daga kiran bayan sun gaisa yace “Na dauko maki Scrubs din a gidan Ummi, can i come over yanzu in kawo maki, kin san za mu je lagos gobe da safe and probably
monday za mu dawo” Mayraah tace “Ohk to Nagode” Yace “Address din fa?” Tace “Bari in tura maka” Katse wayar tayi ta tura masa address din, bayan minti sha biyar ya sake kiranta yace gashi a kofar gida, mikewa tayi sai da ta fara zuwa ta gaya ma Ammi sannan ta fito daga gidan sanye da hijab dinta har kasa, tana ta kallon motar wondering ko ya canza mota ne, ta dai karasa ya sauke glass din yana kallonta da murmushi yace “Good evening” MD ta gani zaune front seat ya wani hakikance, Dr Khalil ya sauko daga motar ya zagayo back seat ya dauko mata uniform din ya mika mata yace “Sai fa da yan sanda suka tsayar da mu kafin mu shigo nan, wai wajen wa za mu” Mayraah tayi murmushi tace “Sai kace masu wajena mana”
Dariya yayi yace “Eh lallai kam wajenki” can yayi kasa da murya yace “Baki gaida boss dinki ba Hajiya”
Mayraah ta sake kallon MD da yayi kasa da kai yana kallonta ta Mirror, don unguwan haske tarrr kamar da rana ko ina fitilu ne, yana ganin ta juyo ya dauke kai yana danna waya with a serious face, a takaice tace
“Ina yini” jin bai amsa ba Khalil ya karasa har kusa da door din motar yayi knocking yace “Ana gaisuwa Oga” MD yace “Dalla ka zo mu tafi kana bata min lokaci kasan ana jirana” Mayraah na kallon Dr Khalil tace “Nagode Dr sai da safe” Ya mata murmushi yace
“Ki gaida su Ammi” Tace “In sha Allah” Daga haka ta shige cikin gida, Dr Khalil ya zagaya ya shiga driver seat, MD ya kallesa yace “Burin ka kawai ka dinga ja mana raini wajen yarinyar nan, yanzu sai ta ga kamar biyo ka nayi fa in her stupid mentality, ji wani iyayi da take da kaudi, to meye da Unguwan nan?” Dr Khalil yace “Aa bawan Allah, sai da nace in ajiye ka eatry ka jirani in zo in kawo mata sakon kafin in koma in dauke ka muje inda za mu kace no way sai ka biyo ni” MD yace “To ni dan iska ne zan yarda ka ajiyeni eatry ba abinci nake ci a eatry ba?” Dariya Dr Khalil yayi yace
“To nan dai ne gidansu incase…..” MD ya kallesa yace
“Incase what?” Dr Khalil na murmushi yace “Incase Watarana mana” Mayraah na komawa dakinta ta dau wayarta taga miss calls din Maheer, murmushi tayi har zata kirasa sai kuma ta tuna za su yi magana da Ya Usman kamar yanda yace mata dazu, ta ajiye wayar with the intention of calling him back idan ta dawo, sannan ta sauka downstairs ko hija dinta bata cire ba ta nufi dakin da ta gansa ciki daxu.
Mayraah na isa kofar dakin tayi knocking, after a while ya bude kotar, shi in dai aka masa knocking baya bada izinin shigowa sai dai ya tafi da kansa ya bude kofar don bai fiye son ana shigo masa daki ba, she is already used to that, tana ganin ya bude kofar ta bi gefensa ta shiga ciki ya bi ta da kallo sai kuma ya kulle kofar ya karasa ciki yace “But i said later in the night” Mayraah ta zaro ido tace “To yanzu yaushe ne yaya? Everywhere is dark already” Zaunawa yayi yana ci gaba da abinda yake yi a laptop yace “Ai ba ayi isha ba” Ta turo baki tace “Yaya ni dai i am eager in ji maganar me zaka min, is it about my dressing dazu?” Ya kalleta yace “Ai Ammi tace dressing din ya maki kyau” Murmushi tayi tace “In dai shine ni dai kayi hakuri, nace maka bazan kara ba” Yace “Ba shi bane” Tayi shiru tana kallonsa, ya kashe laptop din ya ajiye yace “I just want to know what ur next plan is…. 2 years back kinyi saukan Al-qur’ani, this year kin yu graduating from university, immediately after graduation kin samu aiki, so what do u have in mind next?” Ta dan yi murmushi ta sunkuyar da kai tace
“Kamar me fa yaya?” Yace “Ko iyakar burinki kenan a rayuwa?” Ta daga kai a hankali ta kallesa, she wish zai gane yanda ta zama desperate ta hadu da nata relatives din ko da guda daya ne, bata son ta zama an ingrate shi yasa take kauda tunanin nan ko da yaushe a ranta bata basa mafaka ba balle ya dameta, amma God knows in this few months har cikin zuciyarta tana son sanin ko da mutum daya ne a jininta, sauke idonta tayi bata ce masa komai ba, a hankali yace “Kinyi shiru” Tayi gathering courage tace “Duk wani abun Alkhairi will always be among my wish everyday
Yaya, ba ni kadal ba kowa ma ina masa tatan abun alkhairi ya same sa kullum” Yace “Mayraah” Ta daga kai ta kallesa yace “So in ur wish there is nothing like marriage?” Ta dan buda ido, sai kuma tayi murmushi ta sunkuyar da kanta tace “Ai lokaci ne yaya, idan Allah ya kawo lokacin za ayi” Yace “Tell me the truth, is there anything between u and that Dr? I mean Dr Khalil” Mayraah ta zaro ido tace “Not at all wallahi, shi da yake da mata da yaransa biyu” Usman yace “Ohk ba a auren me mata?” Tayi dariya tace “Aa nima ban sani ba” Yace “Baza ki iya auren mai mata ba kenan?” Ta sunkuyar da kai tace “Ni dai ba ruwana” Yace
“Abokina me mata ya ga hotonki yace yana so yanzu baza ki iya aurensa ba kenan?” Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta turo baki bata ce komai ba, yace “Am serious” Shiru tayi tana kallon sa, ya sauke idonsa yace “Wasa nake bai da mata, he is single, a Barrister too, are u interested? maganar da za mu yi kenan dama” Nan da nan jikinta yayi sanyi don Musharraf ne ya fado mata, Shi dai Usman kallonta kawai yake examining her reaction at the same time, bayan few seconds tace “Yaya i don’t think i will love again….” Hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da sauri, shi dai yayi shiru yana kallonta, can yace “Mayraah” ta daga kai ta kallesa tana share idonta, yace “Why won’t u love again” Ta fashe da kuka tace “I don’t want to remember the pass, ko ma waye zai aureni yanzu dole sae ya fara sanin ko ni wacece, after that no parent will want their blood to marry me” Yana kallonta a hankali yace “Har Ammi da Abba?” Daga kai tayi ta kallesa as if trying to apprehend what he meant by so saying, Bai bata wannan space din ba yayi saurin cewa “Forget that pass u are talking about and concentrate on the future Mayraah” Ita dai bata ce komai ba sae kallonsa take, yace “So i will want you to give this guy a chance” Nan ma dai bata ce komai ba, yace “Banda kula kowa kuma” Tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba, yace
“Promise me that” Ta kallesa kamar yasan abinda ke running a mind dinta yace “Kin dai san bazan yi abinda zai cuceki ba ko?” Ta sauke idonta, yace “So now make that promise baza ki kula wasu ba” Ta gyada masa kai tace “In sha Allah” Yace “You can leave” Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita wasu hawayen na taruwa idonta ta koma dakinta. Wajen karfe tara bayan tayi wanka ta kira Maheer, Haseenah dake parlon ta mike jin wayarsa dake ajiye kan kujera na ring, shi kuma yana kitchen yana hada shayi, kallon screen din wayar ta dinga yi taga an sa Mimi with love emoji, ta dinga kallon wayar babu kyaftawa har ya fito daga kitchen, ta juya ta shige daki, ko kallon inda ta bi bai yi ba ya dau wayarsa bayan yayi picking Mayraah ta gaishesa, ya zauna yace “Ina kika shiga?” Tace
“Kai dai zan tambaya, bayan tun dazu nake ta kiran wayarka” Yayi murmushi yace “Wayar na silent kika kira dazu, ya kike?” Tace “Alhamdulillah, ya aiki” Yace
“Cool, kin je interview din yau?” Tace “Na je” Yace
“No issues?” Kai ta gyada masa kamar yana ganinta, sai kuma tace “Ka fara processing transfer din naka yaya?” Yace “Not yet” ta dan hade rai tace “Do it soon pls, ko baka missing dinmu” Yace “I will try Mimi, ina missing dinku mana, ina Ammi?” Tace “She is in her room, Mama Ladi ta tafi ne?” Er dariya yayi yace “Jiya na kai ta har karayen wai bazata iya zaman motar haya ba” Mayraah tayi murmushi tace “Ayya, yanzu yaya idan ina son magana da sis Badiyyah ta ina zan sameta?” Maheer yace “I don’t really know” Tace “I tried calling her lines severally amma duk a kashe” Yace “May be ta kashe wayar ne” Mayraah tayi shiru, shi ma haka, bayan few seconds tace “Pls try and request for the transfer kaji yaya” Yace “I will do so starting from tomorrow in sha Allah Mimi” Tana murmushi tace “Yauwa yayana, i want to go to bed now” a hankali yace “Alright Dear, sleep tight” Tace
“Bye” Daga haka ya katse wayar, ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, tun da suka koma Abuja sai dai ya sha tea ko coffee, idan ya fita kuma ya biya restaurant ya ci abinci, kana ganinsa kasan he is not himself, a da yayi niyyar ko zai nemi transfer din sai zuwa nan da wata biyu ko uku, amma yanzu kam yaji bazai iya ba, damuwa yayi masa yawa, ganin daga shi sai Haseenah na kara saka masa damuwar nan, don haka dole ma ya nemi transfer din nan ko ta yaya ne ya koma wajen family dinsa soon. Ranan Sunday da yamma Mayraah ta gama shiryawa ta fito daga dakinta zuwa parlon Ammi, Ammi dake zaune tana kallon TV ta kalleta tace “Ko dai mu bari zuwa gobe ko da daddare ne in kin dawo aiki mu je daughter?” Mayraah ta zauna gefenta tace “Aa Ammi mu je yau pis kin ga fa na riga nayi girkin, nasan goben a gajiye zan dawo” Ammi tace “Toh shikenan, mu je kawai…” Mikewa tayi ta shiga daki ta dauko gyalenta da jaka, sannan suka sauko downstairs, sai da Mayraah ta tara shiga kitchen ta dau warmer din two da miyar ganyen da tayi ta kai mota, driver na compound yana jiran fitowarsu, Mayraah ta sanar masa inda zai kai su sannan ta bude ma Ammi back seat ta jira har ta karaso ta shiga ta kulle motar sannan ta tafi front seat ta zauna, tafiyar kusan minti talatin da biyar suka yi suka iso gidan, Drivern yayi parking bakin gate, Mayraan ta sauka ta dauko warmers din biyu, Ammi ma ta sauko daga motar ta sanar masa jiransu zai yi sannan suka shiga cikin gidan, Karime ce ta bude masu kofar parlon tana ganin Mayraah ta rungumeta cike da farin cikin ganinta tace “Sannunku da zuwa…
Ku shigo” Mayraah na murmushi suka shiga parlon da Ammi, ta ajiye warmers din hannunta, bayan Karime sun gaisa da Ammi ta mike tace “Bari in yi ma Hajiyar magana tana daki” Ba a dau lokaci ba sai ga ta tare da Ummi, shigowa parlon Ummi tayi da fara’arta tana masu sannu da zuwa, Mayraah ta koma kusa da inda Ummi ta zauna ta gaisheta, Ummi ta amsa da fara’a tace “Kwana biyu ko leko mu kin ki yi Ilham, shine ranan Khalil ke ce min ai mamanki sun dawo Abujan ma gaba daya, ina jin ko kwana biyar ba ayi ba da ya gaya min haka” Mayraah na murmushi tace “Ai naje kano nayi sati biyu ne shi yasa Ummi” Ummi tace
“Maa sha Allah, Maman taki ce wannan ko” Ammi dai murmushi kawai take, Mayraah ta gyada kai tace “Ita ce” Suka kara gaisawa da Ammi, Ammi ta mata godiyan rikon Mayraah da tayi, Ummi tace “Kai haba babu komai, ai yi ma kai ne” Mayraah tace “Inna na daki?” Ummi tace “Tana ciki, ku shiga ku gaisa” Mayraah tace “Nayi mata girki ne” Ummi tace “Ai ko kin kyauta wallahi, Allah maki albarka” Mayraah ta mike tana kallon Ammi tace “Ammi mu je ku gaisa da Inna” Mikewa Ammi tayi ta bi bayan Mayraah zuwa dakin inna, karime ta dau warmers din ta bi su a baya zata kai dakin, Sosai inna tayi farin cikin ganin Mayraah bayan sun gaisa da Ammi tace “Kai amma wannan er taki er albarka ce warce bata mance alkhairi, na dade ban ga yarinya me hankali kamar ta ba, ki ji fa har da girki ta min abun sha’awa, yaushe ma na samu haka a gidan nan, doya ce fa yanka hudu suka hadani da shi dazu kamar a fursin wallahi” Ammi dai murmushi kawai take tana kallon Inna, su da suka yi niyyar barin gidan da wuri sai da inna ta ja Ammi da zance, su ne har kusan karfe shidda a gidan, Ummi ma tuni ta shigo dakin Inna ta zauna suna hiran gaba daya, magana daya biyu sai innan ta Gwale Ummi, Ummi dai ko bin ta kanta bata yi, a haka dal Ammi ta samu suka lallaba suka bar gidan inna na cewa tana nan zuwa zata sa Khalil ya kai ta, bayan sun kama hanya Mayraah na kallon Ammi tace “Kamar Mama Ladi ko Ammi” Dariya Ammi tayi tace “Wannan ai ta so ta fi mama Ladi, gaskiya Ummin na hakuri da ita…” Mayraah tace “Ai kam Ummi ba ruwanta bata biyeta” Washegari ko da Mayraah taje alki su Khalil basu dawo Lagos ba wai sai Tuesday, hankalinta kwance tayi aikinta a asibitin babu wanda ya takura ta, a ranta ta dinga fatan da ma kar su dawo da MD din nan, a rikesa a branch dinsu na can Lagos din ace an masa transfer. Da daddare Mayraah na shirin kwanciya kiran Maheer ya shigo wayarta, dauka tayl ta zauna geten gado sannan ta daga, bayan sun gaisa, a hankali tace “Was it successful yaya?” Yace “Nop Mimi, wai sai nan da wata uku” Lokaci daya jikin Mayraah yayi sanyi, for kusan 4 days yake ta kokarin ganin ya samu transfer din zuwa Abuja, har Abba sai da yayi intervening a issue din, duk hope dinta yau idan ya kirata zai ce an maidosa Abuja, jin bata ce komai ba yayi kasa da murya yace “Kin yi shiru” a hankali tace “To me zan ce?” Yayi murmushi yace “Ki ce min congratulations” Ta buda ido tace “Wai anyi Transferring dinka?” Yace “Yes Mimi” Ba karamin farin ciki Mayraah tayi ba, har sallan dare sai da tayi a yan kwanakin nan duk don ya samu transfer din sai gashi kuma ya samu, yace “But Abba ne fa yasan yanda ya bi aka yi Transterring dina, it won’t have been possible idan ba don shi ba” Mayraah tace “Maa sha Allah, congratulations yayana i am so happy with this news, yanzu yaushe zaka yi resuming aiki a nan?” Yace “Sai monday next week, but in sha Allah zuwa friday zan dawo Abujan” Tace “Toh Allah ya kai mu yayana” Tana son tambayarsa ko da Haseenahn za su taho amma dai tayi shiru bata yi tambayar ba, yace
“Bari in kira Ammi in gaya mata, i told u first before her” Mayraah na murmushi tace “To yaya, bye” Maheer na kiran Ammi bayan ita ma tayi farin ciki tace
“To yanzu ya za kayi da yarinyar nan?” Yace “Kawai ta tafi gidansu” Ammi tace “Aa babu wannan zancen Maheer, babu yanda muka iya haka zaka taho da ita nan, the chalet here is almost 2 times bigger than the one u are inside now, hakuri za kayi ku taho tare” Maheer yayi shiru don bai yi expecting Ammi zata ce haka ba, Cikin kwantar da murya tace “I understand you dear, amma kayi hakuri na dan lokaci ne, bazan taba goyon bayan ka ci gaba da zama da Haseenah ba yanzun ma kai ma kasan akwai dalili ne” Shi dai bai ce komai ba, don gaba daya mood dinsa har ya baci.
Ranan Wednesday Mayraah na shiga asibiti da safe bayan ta dubo wata patient a wani ward tana dawowa reception sai ga Dr Khalil ya shigo, tana hango wanda suka shigo tare kawai tayi saurin juya masu baya pretending bata gansu ba, da haka ta nufi wani ward da sauri ta shige ciki kamar zata je dubo wani patient, duk MD na kallonta, nurse din wajen ta gaishesu da ladabi, har MD din ya fara tafiya toward step sai kuma ya dawo ya cire glasses dinsa yana kallon nurse din da kyau yace “Anyi cleaning office dina yau?” Nurse din ta mike da ladabi tace “Yes sir, ai kullum sai cleaner din ya yi cleaning office din sannan ya maida ma secretary spare key… He does that every day ko baka nan” Yace “Fine, i need my library shelf carefully dusted and cleaned to my satisfaction today, Da muka shigo ai kamar ba ke kadai bace a nan” Ta gyada kai da sauri tace “Eh ni da nurse Ilham ce, amma ta shiga ward 3 zata dubo patient” Yace “Good, look for her ki gaya mata abinda nace don ita zata yi aikin ba wani ba, or you just tell her to meet me in my office immediately” Nurse din tace “Okay sir” shi dai Dr Khalil na tsaye yana kallon MD da mamaki, Nurse din ta tafi da sauri inda Mayraah ta shiga don kai mata sakon MD, Dr Khalil ya bi bayan
MD da ya nufi step yace “Dama nurse ta taba maka gyaran office Dr? We have more than enough cleaners in here” MD yace “Za a fara yau, kai baka ga duk ka sa yarinyar nan ta gama raina mu ba, wato tafi karfin ta tsaya ta gaishemu shine zata shige ward, to zata yi gyaran every nook and cranny na office dina yau kuwa, next time ma idan tayi repeating haka abinda zan yi mata kenan, silly girl” murmushi kawai
Dr Khalil yake yana biye da shi a baya. Mayraah ta dinga kallon nurse din da ta kawo mata sakon MD tace “In same sa a office kuma? Allura fa zan ma patient din nan idan ta gama cin abinci” Nurse din tace “| will handle that, kawai ki tafi ya ce yana jiran ki” Mayraah ta fita daga ward din ta tabe baki ta wuce sama, jiya da baya nan asibitin so conducive wallahi.
Knocking din office din nasa tayi tana hade rai, har sai da ta kwankwasa sau uku sannan taji yace a shigo, ta bude kofar ta shiga, gaban table dinsa ta tafi ta tsaya bata bari ta kallesa ba tace “Good morning sir” Bai amsa gaisuwar ba ya nuna mata direction da shelf din Libraryn nasa yake yace “Take out all those textbooks and articles, dust and clean, finish with that first….” Mayraah ta dinga kallonsa taki cewa komai, ya daga kai ya kalleta yace “What are you still waiting for?” Juyawa tayi ta nufi shelf din da ya nuna mata tuskarta a daure, ya bi ta da ido, tana isa nan ta fara sauke textbooks din daya bayan daya tana ajiyesu kasa, sai da ta sauke many of the textbooks ta fara jin kamar dust a hancinta, still dai ta ci gaba da fiddo su, tana ajiye na hannunta taji tari ya taho mata, da sauri ta rufe hancinta da hannunta, kamar tayi triggering tarin soda kuran dake hannun nata, ta durkusa nan kasa da sauri within few seconds she began gasping for breath, bai san sanda ya karasa inda take ba ya duka gabanta ya dago kanta da sauri yana kallonta yace “Are you Asthmatic?” Sai kuma ya janyeta daga wajen textbooks din ya zaunar da ita kan office chair dinsa trying to help her with first aid, amma numfashinta sai kokarin daukewa yake, Ikci daya duk ya daburce a wajen kamar bai taba zama likita ba a rayuwarsa, gashi dai bayan pills da injections har inhaler akwai a show glass din magunguna dake office din but he was just lost ya kasa yi mata komai, dai dai nan Dr Balogun ya shigo office din, da sauri ya nufosu lkci daya kuma yake tambayar me ya sameta, yana fahimtar Asthma ne ya fara mata abinda ya kamata a wajen, cikin kankanin lokaci ya dauko pills a show glass ya bude ya dau bottle water dake kan table ya bata, with his help ta hadiyi pill din, they were there for almost 15 mins yana kokarin calming dinta har ta fara sauke numfashi a hankali, MD was just standing like a quack Dr a wajen with no help, Dr Balogun ya dinga mata sannu, bayan some minutes yace “Are you okay now?” Ta daga idanuwanta da suka kada, duk da azaban da kirjinta ke mata ta gyada masa kai, yace “Ok now duk ward din da kika ga babu kowa a nan sama kije ki kwanta, get some rest” Tayi karfin halin mikewa tsaye Dr Balogun ya bata hanya yana mata sannu, tana tara tafiya ta ji kanta na juya mata tayi baya zata fadi, kafin ta kai kasa MD yayi saurin riketa, Dr Balogun yace
“Her Bp is low” kwantar da ita MD yayi kan examination bed dake office din nasa, Dr Balogun na kallonsa yace “Akwai coffee powder ayi making mata coffee ta sha?” MD ya dauko Tea cup dinsa yana wankewa sau daya ya kalli cikin cup din keenly, kafin yayi attempting sake komawa ya wanke Dr Balogun ya amshi cup din yace “I will do it…” Cikin mintuna kadan yayi making coffee a cup din ya mika masa yace “I have a patient in my office… I will be back idan na sallamesa yanzu” MD ya amshi Coffee din ya juya yana kallon Mayraah da idonta ke a rufe, Dr Balogun ya fita daga office din da sauri don dama tambaya ya shigo yayi masa….
Abba dake zaune parlon Ammi ya ajiye drink din hannunsa yana kallonta yace “Saboda ance za aje kasar waje da ita sai kice ta ajiye aiki Madam? Ai kamar this is a privilege for her, i see nothing wrong don asibiti ya zabe ta cikin wa enda za su je England conference….” A hankali Ammi tace “Gaskiya ni dai hankalina bai kwanta ba, of all the staffs in the hospital why her? Yaushe ta fara aikin har za a zabeta?” Abba ya kalli Maheer dake parlon yana kallonsu yace “Can you hear ur mother?” Murmushi yayi yace “Kuma conference din nasan bazai wuce kwana biyu zuwa uku ba fa Ammi” Ammi tace “Ko ma kwana daya ne ni dai kawai hankalina bai kwanta ba” Abba yace “Toh tunda haka ne sai Usman ya bi su England din, hope yanzu hankalinki ya kwanta?” Maheer ya juya yana kallon Abba, Ammi ma dai tayi shiru tana kallonsa, mikewa Abba yayi yace “Let me get some rest” Daga haka ya fita daga Parlon zuwa part dinsa, Ammi na kallon Maheer tace “Is there anyway da za a sanar ma asibitin a cire sunanta daga masu tafiyar pls? Wani Usman ne zai bi ta kanta in ma yaje England din, harkan gabansa kawai zai yi ya juyo ranan da yaji ance za su dawo” Maheer yace “Kawai Ki bari ta je Ammi, kamar yanda Abba ya fada it’s a privilege, don ba kowa ne zai samu hakan ba, may be ita me asibitin ta yaba da nutsuwarta ne sannan taga yanda take aiki, ko kin manta daughter din taki da first class ta fita? Did you know what that means? Kar kiji komai ana samun haka sosai, beside ba da ita kadai bane ai za aje dole da akwai staffs da aka zaba, it’s something we should be happy about” Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace “Toh shikenan tunda ka ce haka” Mayraah na dakinta da daddare bayan tayi shirin bacci Ammi ta shigo da sallama, zaunawa Ammi tayi gefen gadon tana kallonta tace “Ya ciwon kan?” Mayraah tace “Yayi sauki tun dazu Ammi” Sai kuma ta marairaice tace “Stress din aikin nan ne fa Ammi, kullum da sassafe mutum zai fita bazai dawo ba sai 6:30, and every day the hospital is always busy with patients, ko lokacin hutu fa mutum bashi da” Ammi tace “A haka nan zaki saba daughter” Mayraah ta girgiza kai tace “Gashi kusan 5 weeks har yanzu ban saba ba, meaning bazan iya sabawa ba” Ammi tayi murmushi don kusan kullum sai tayi complain din zuwa aikin nan, Ammi tace “Toh yanxu yaushe ne tafiyar ta ku? You said ur Visa is ready” Mayraah tace
“Nima ban sani ba, but naji kamar Dr Khalil yace next week” Ammi tace “To Allah ya kai mu, abincin da kika girka ma yayan naki ya kare ne?” Mayraah tace “Za ki ci ne Ammi?” Ammi tace “In zan samu ba” Murmushi Mayraah tayi tace “Akwai sauran kadan, bari in debo maki” Sauka tayi daga kan gadon ta fita daga dakin Ammi ta bi ta da ido, magana take son mata amma ta rasa ta inda zata tara, can ta sauke ajiyar zuciya still thinking of where to start from, Mayraah na sauka kasa taga Maheer parlon yana kallo, tun da ya dawo Abuja daga kano yau kusan 4 weeks kenan bacci ne kawai ke kai sa chalet shi ma wajen karfe dayan dare wani lokacin, yana dawowa aiki main building yake nutowa, komai a dakinsa da ke nan main building din yake yi, duk aka yi girki mai aikin Ammi ke kai ma Haseenah Chalet, wani Iken ta kan shigo babba parlon gidan wataran ma kwata kwata bata shigowa tana can chalet ita kadai, Mayraah na kallonsa tace
“Yaya ka sha shayin?” Yace “Na sha” Kitchen ta nufa ta zubo ma Ammi sauran abincin da ta dafa ma
Maneer dazu sannan ta dawo parlon, yace “Yaushe kika fara cin abinci haka Mimi?” Dariya tayi tace
“Ammi fa zan kai ma” Yace “Better” Murmushi tayi ta koma sama ta kai ma Ammi abincin, Ammi na amsa kawai ta mike don ta rasa ta inda zata fara mata maganar da ya kawo ta dakin, ta sa a rai zata bari in sun dawo daga England kawai. Yau tun da Mayraah ta tashi take dakinta a kwance bata fito ba, breakfast ma har Bedroom Ammi ta sa me aiki ta kai mata, it was a Friday kuma yau ne ranan tatiyar tasu zuwa Uk amma evening Flight, jin ana knocking kofarta ta kalli agogo dake nuna karfe uku na rana ta sauka daga kan gadon ta bude kofar, Maheer ne tsaye bakin kofar yana sanye da farin Gezna, daga sama har kasa take kallonsa, sai kuma tayi murmushi ta jingina da kofar a hankali tace “Good afternoon” Yace “Afternoon Mimi” Ta langwabar da kai tace “Kayi kyau kamar wani sabon ango, nasan yau mata suna ta kallon ka a hanya ko” Ya dan buda ido yace “Ango kuma” Tana murmushi tace “I am serious u look gorgeous” Bai kulata ba yace “Duk efizyn zaki je England ne yau ya sa kika ki fitowa parlor mu ganki?” Tayi dariya tace
“Yaya wallahi kamar a fasa tafiyar da ni, i wish kawai za ace banda ni, i am so tense” Yace “Why?” kamar zata yi kuka tace “Kawai haka nan, i don’t understand why i am tense” Ya sauke idonsa kasa yace “Sauko mu yi Lunch” a hankali tace “Ohk” Daga haka ya juya ya sauka kasa, ita kuma ta juya ta koma dakin zata dauko hular ta, suna zaune parlon su biyu kadai, eating from the same plate Haseenah ta shigo parlon, kamar hadin baki suka mata kallo daya suka dauke kai a tare, kitchen ta nufa ta je ajiye warmer din da za a sa mata abincin dare, tana fitowa bata ko kallesu ba ta fita daga parlon, Mayraah na gama cin abincin ta dinga ma Maheer hira a parlon tana basa labarin irin cases da take gani a asibiti, wanda kawai sauraronta yake a ransa kuma yana tunanin may be ta mance shi ma likita ne, a haka Ammi ta sauka downstairs ta samesu, ta kalli agogo tace “Ke ba karfe biyar bane Flight dinku kike nan zaune?” Sai da gaban Mayraah ya fadi don ita ko son a tuna mata da tafiyar nan bata yi, Maheer yace “Mimi that’s true ki je ki shirya da wuri, gwara ki jirasu da ace sun jiraki” A hankali ta mike ta wuce sama, bandaki ta shiga tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta idar da sallahn asr Ammi ta shigo dakin, tana kallonta tace “Kin sa kayan naki cikin akwati ne?” Girgiza kai tayi, Ammi tace “Ke dai komai kin fi son sai kinyi cikin kurarren lokaci, ance maki flight karfe biyar ya kamata ace kuna airport ma yanzu” Usman ne yayi knocking kofar dakin sannan ya bude, yana kallon Mayraah yace “Ina kika ajiye wayarki ake ta kiranki?” Ta dan buda ido da sauri ta nufi karkashin pillow da ta ajiye wayar dazu, miss calls din Dr Khalil ta gani har uku, ta kalli Usman dake mata wani kallo, Ammi ta fiddo mata wani abaya ta ajiye gefen gado tace “Gashi nan ki saka” Usman yace
“Kin bar su tun dazu a waje suna jiranki” Daga haka ya juya ya bar bakin kofar, Ammi ta bude baki tana kallon Mayraah da ta kasa tabuka komai, da kanta ta fara hada mata few clothes dinta da duk wani abu da zata bukata a akwati, bayan barin Usman wajen sai ga Maheer, a bakin kofa shi ma ya tsaya yace “Mimi they are waiting for u outside kiyi sauri….” Kayanta ta dauka ta fara sa wa, Ammi ta gama hada mata komanta a akwati, Maheer na kallon Ammi yace
“Akwai sanyi sosai Uk, she shouldn’t forget her jacket” Ammi ta kalli Mayraah tace “Rigunan sanyinki suna dakina kije ki dubo da sauri” Mayraah na fita daga dakin Maheer ya bi bayanta yace “Do not forget ur sanitary stuffs, hopefully har ki dawo kila….” Mayraah ta buda ido don har ta manta, sai bayan kusan minti goma Maheer ya sauka downstairs da akwatinta tana biye da shi a baya, Ammi ta rakasu har compound tana mata Allah ya tsare hanya, kana ganin Ammi kasan babu yanda ta ya ne da tafiyar Mayraah, suna fita kofar gida Mayraah ta ga mota anyi parking, Dr Khalil ya bude masu booth Maheer ya ajiye akwatin, tana kallon Maheer tace “Yaya gobe Ya Usman din zai je can?” Maheer ya gyada mata kai yace “In sha Allah” A hankali ta bude back seat ta shiga don ko ba a gaya mata ba taga alamar da mutum a front seat din, Dr Khalil suka yi sallama da Maheer sannan ya koma cikin motar, Mayraah ta daga ma yayan nata hannu kamar zata yi kuka, Dr Khalil yayi reverse suka bar anguwan. Tana daga kai suka hada ido da MD ta madubi, sauke idonta tayi murya can kasa tace “Good evening” ya ji ko bai ji ba oho, don bata ji ya amsa mata ba, Dr Khalil yace “Ina kika ajiye wayarki, kin kuma san karte nawa ne flight din naku” Tace “Shiryawa nake ne” Dr Khalil ya girgiza kai yace “Ku dai mata komai sai kun saka African time a ciki….” Mayraah dai ta ci gaba da danna wayarta bata ce masa komai ba, MD na kallon Khalil yace “Plss ka bi route din da za mu yi sauri, it’s easy to miss a flight..” Dr Khalil yace “In sha Allah baza ayi missing Flight din ba we will get there in time” Suna isa airport MD ya sauka, Dr Khalil ma ya sauka daga motar ya fiddo hand luggage din MD wanda jacket dinsa ne kadai a ciki sai textbooks, sannan ya ciro akwatin Mayraah ma, tuni MD ya shiga airport din don baya son ace sun yi missing jirgin, Mayraah dai sai zare ido take tana neman sauran da za su je Uk din tare, Kasa hakuri tayi bayan sun nufi cikin airport tare da Dr Khalil tace “To ina sauran sir?” Yace “Doctors biyu ne kuma suna lagos, daga can za su tafi” Mayraah ta zaro ido tace “Babu nurse ko daya??” Yace “Babu” Mayraah ta marairaice tana kallonsa, dariya ta basa amma ya dake yace “It’s fine Mayraah” Ta girgiza kai kamar xata yi kuka tace
“Yanzu ni da shi kadai za mu hau jirgin?” Dr Khalil yace “Eh mana, in kun je can za ku hadu da sauran” Ji tayi hankalinta ya tashi tace “Ni dai wallahi i don’t want to go with him” Dr Khalil yayi dariya yace “But he is not a monster Mayraah, look kin ga kun yi latti let’s be fast pls” Bin sa kawai take a baya with different thought a zuciyarta, duk traveling document dinta suna wajen MD din, bata kara shiga tashin hankali ba sai da taga sun gama check in, Dr Khalil na masu sallama bayan za su shiga departure lounge, dauke kanta tayi don yanzun nan sai ta iya fashewa da kuka. Sun shiga departure lounge din immediately aka fara boarding plane din nasu, ita dai bin sa kawai take gashi ya ki juyowa ma ya ga ko tana biye da shi a baya ko akasin haka, a haka har suka shiga plane din, yana isa seat dinsa ya ajiye hand luggage dinsa a sama sannan ya zauna, tana ganin haka kawai tayi assuming seat din ta ne gefen nasa, ita ma ta zauna tana satan kallonsa. 2 hours into the flight ta fara jin bacci amma tayi ta kokarin ganin bata yi ba, abincin da aka yi serving dinsu ma bata taba komai ba, a haka har baccin ya dauketa bata sani ba, she can’t tell for how long tayi baccin kawai ita dai kamshin turaren da ya cikata ne ya farkar da ita daga baccin bayan tayi isasshe, zaro ido tayi ganin inda tayi resting kanta, sai kuma ta daga kai da sauri ta kallesa, idonsa na kan wani littafi dake hannunsa, matsawa tayi tana gyara zamanta kamar munatuka, shi dai ko kallonta bai yi ba yana karatun book din hannunsa, ko gyangyadi Mayraah bata sake barin tayi ba har suka sauka UK, bayan ya cire seat belt dinsa ya mike ya dau hand luggage dinsa, ita dai kallonsa kawai take, ya bude karamar jakar tasa ya ciro jacket dinsa ya saka, tana ganin ya fara tafiya ta wani bi sa da harara sai kuma ta mike ko ruwa bata dauka a abincin da aka ajiye mata ba ta bi bayansa, suna sauka jirgin
Mayraah taji ta kamar a freezer, nan da nan hankalinta ya tashi, ko wani mutum ta gani a wajen da thick Jacket dinsa, wani mugun sanyi ta dinga ji amma a haka ta dinga bin sa a baya, ko kadan bata shiri da sanyi, yanzu nan sai yayi distablizing dinta nan da nan kuma zata fara mura da tari, har suka shiga airport din tana jiran akwatinta MD yaki kallon inda take don waje ma ya nema ya zauna yake danna wayarsa, atter many minutes of waiting akwatinta ya iso ta dauka ta kalli inda yake, kawai gani tayi ya mike ya fara tafiya, ta bi bayansa tana tafiya a hankali har suka fito daga wajen, she was just shivering daga inda take tsaye rike da akwatinta, shi kuma yana tsaye dan nesa da ita yana kiran Ceo don yaji hotel din da ta kama ma staffs din nata, tana dagawa tace zata kirasa sannan ta katse wayar, yasan yanzu sai su kai minti goma suna jiranta a haka, ya dan juya ya kalli direction din da Mayraan take ta wani takure saboda mugun sanyi, kasa ci gaba da jure sanyin tayi ga shi hankalinta bai je ta bude akwatinta ta ciro rigar sanyinta ba, she was shivering seriously, juyawa tayi da sauri jin mutum a kusa da ita ta kusa cin karo da shi, not minding that ya daura mata jacket dinsa a shoulders dinta sannan ya koma inda yake tsaye, ta kasa dago kanta, after few seconds ta daga kai a hankali ta kallesa, wrapping din jacket din tayi jikinta ba tare da ta saka ba, bayan kusan minti biyar Ceo ta kirasa tace kawai ya taho da ita gidanta, he was so surprise, don banda shi a duk staffs dinta infact har colleagues dinta na nan UK babu wanda yasan gidanta sai shi kadai, sai da ya sake tambayarta to be sure of what she said, ta kuma maimaita masa abinda tace, a hankali yace “Ok Ma’am” Daga haka ya katse wayar ya samu Cab din da zai kai su gidan nata, it’s almost 11pm na dare, Mayraah na ganin Cab din ta ja akwatinta duk da jacket din da ya sa mata bata daina jin sanyin ba don ya riga ya tara shigarta sanyin, ya dau akwatin ya sa a booth sannan ya bude back seat ya shiga, ita ma ta shiga, har suka isa gidan Ceo Mayraah was shivering a gefensa, wannan dalilin yasa shi daukan akwatinta daga booth din motar tana biye da shi, Ceo na bude kofar mansion dinta ta kallesa da mamaki tace “Why are you not on Jacket Aliyu?” Sai kuma taga Mayraah, bude kofar tayi da sauri tace “Come in my dear” Mayraah ta shiga parlon that was soo warm and smelling nice, shi ma ya shiga parlon with her box da hand luggage dinsa, Ganin yanda take rawan sanyi Ceo kawai ta wuce wani daki dake parlon da ita giving her a huge duvet to cover her self, sannan ta dawo parlor tana kallon MD tace “Go make ur self a cup of coffee Aliyu” Yace “Ma’am Idan naje gida zan sha….” Tace “Ohk then, akwatinta ne wannan?” Yace “Yes Ma’am nata ne” daukan akwatin tayi ta kai dakin da ta kai Mayraah, ya jira har ta fito sannan yayi mata sallama, tace “Let me get u my car key, gobe da safe sai ka dawo da shi” Ya sunkuyar da kansa yace “Ok Ma’am” Makullin motarta ta dauko masa hade da sabon jacket, ya amsa jacket din da makullin sannan ya saka jacket din yayi mata godiya ya bar gidan ya nufi garage dinta, kitchen ta tafi zata hado ma Mayraah hot chocolate, Mayraah dai ta takure cikin farin duvet din da ta bata ga kamshin turaren jacket dinsa da ya cikata.
Mayraah na sauka second floor ta had da Dr
Khalil ya fito office dinsa da was files, yana ganinta ya nufo ta da sauri yace “How are you feeling now?” Ta gyada masa kai a hankali tace
“Alhamdulillah, i am better now” yace “Ina za ki je?” Tace “Driver yana jirana a waje” Yace “Did he ask you to go home?” Ta gyada masa kai, yace “Alright, Allah ya kara lafiya” Tace “Ameen, Nagode” Downstairs suka sauka a tare, ta tafi ta dauka handbag dinta tayi ma Nurse Hafsat sallama sannan ta bar asibitin, tana isa gida
Ammi dake parlonta suna waya da Aunty Mariya ta kalli agogo sannan tayi ma Aunty Mariya sallama ta mike tana kallonta da mamaki tace
“Naga kin dawo da wuri” Mayraah ta kalli agogo dake nuna karfe biyu tace “Bana jin dadi ne”
Ammi ta nufeta da sauri tana taba iikinta tace
“Subhanallah, me ya sameki? Since when?”
Mayraah tace “I had an attack daxu da safe”
Ammi ta zaunar da ita kan kujera da damuwa tace
“Garin yaya ?” Mavraah ta sauke ajivar zuciva tace “Ina jin wajen kamar akwai kura ne, ni kuma ban sani ba, amma ai naji sauki yanzu, an bani magani na sha after sometime na dawo normal shine har nayi bacci” Ammi tace “Toh Allah ya sauwake, but duk in kika ga wajen da zai iya accommodating dust ki dinga saka nose mask Mimi, ki daina fita babu shi kin ji?” Mayraah tace “In sha Allah Ammi” Ammi tace “Bari in kawo maki abinci, kin yi sallah?” Ta gyada kai tace “Nayi” Ammi ta mike ta fita daga parlon zata je kawo mata abinci, Mayraah ta jinginar da kanta da kujera, bayan wani lokaci wayar Ammi ya fara ring,
Mayraah ta mike tana kallon wayar gain wanda ke kiranta ta karasa inda wayar yake ta dauka sannan tayi picking ta kai kunne, sallama yay ta amsa, a hankali tace “Good afternoon” Daga daya bangaren yace “Are you okay?” Murmushi tayi tace “Me yasa ka tambaya?” Yace “I sense that from ur voice, baki da lafiya ne?” Tace “Asthma dina ne ya tashi a asibiti” Yace “Subhanallah, how did that happen?” Tace “I am very fine now, naji sauki sosai, yaya hope dai ka gama shiryawa?
Kasan friday din ya kusa fa” Yace “Sure, Allah ya kai mu lafiya” Tace “Ameen” Yace “Kin sha magani amma?” Tace “Eh an ban a asibiti” Yace “Toh Allah kai mu lafiya” Tace “Ameen” Yace “Kin sha magani amma?” Tace “Eh an ban a asibiti” Yace “Toh Allah ya sauke, be careful pls Mimi always go around with ur nose mask to avoid such issues” Tace
“To yaya” Yace “Ammi fa?” Tace “Taje kitchen”
Yace “Ohk, i will call her back later, go and get some rest Mimi” a hankali tace “Bye” Washegari Wednesday Dr Khalil na office dinsa bayan fitar wata patient MD ya shigo, Dr Khalil ya daga kai yana kallonsa har ya karaso ya zauna vace “I just finish speaking with Ceo, tana son zata yi magana da yarinyar nan, kaga daga common Asthmatic attack jiya shine tayi taking advantage taki zuwa aikin yau, who does that pls, idan nayi magana kace i am not being considerate… Dr Khalil vace “Sai kace mata bata da lafiya mana…” MD yace “To dama idan ba haka ba me kake son in ce mata, imagine ceo fa, yarinyar da common workshop a lagos bata kai a fara zuwa da ita ba shine take tambayar ko tana da international passport, for what? ni ban ma san yanda zan mata bayani cewar ba a bisa ka’ida aka dauketa aiki a asibitin nan ba, idan ba ayi hankali ba fa sai ceo tace da ita za aje conference din nan” Dr Khalil yace “Nan din ba bakin ciki zaka mata sir?
Tun da kaga haka ceo din is gradually becoming fond of her, jininta ya hadu da ita ne, kai ne har yanzu ka ki kwantar da hankali ka lura how lovely the pretty girl is ba” MD yace “And how will dat add any impact to my life? That is not my problem Khalil, yanzu cewa tayi a kira ta a tambayeta ko tana da international passport, and i should feed her back immediately” Kallonsa kawai Dr Khalil yake, MD yace “So now after some minutes i will call and tell her tace bata da international passport..” Dr Khalil ya jawo wayarsa yayi dialing number yana fara ring ya sa a handsfree, ba a dau lokaci ba aka daga, murya can kasa tayi sallama, her voice was so cool and calm, MD ya masa wani kallo ya mike amma sai bai fita ba, Dr Khalil ya amsa gaisuwar da tayi masa yace
“Ya jikin?” Tace “Alhamdulillah” Yace “Me yasa baki zo aikin yau ba” Ta dan yi shiru, sai kuma a hankali tace “I am still recovering, kuma ni bana son a dinga min masifa anyhow” Dariya ta ba Dr Khalil, MD ko ya gyada kai bayan ya ji me tace, Dr Khalil yace “To wa ke maki masifa Mayraah?” Tace “MDn ku mana, he is always finding fault where there is none, ko gajiya baya yi da fada, energy da yake sakawa a fada da ma a field dinsa yake sakawa da ya fi, kuma gwara ni ranan allura ne kawai na dan zama confuse da zan ma yarinya, shi kuwa a whole asthmatic patient a gabansa babu abinda ya iya yi, just going up and down like a student, i nearly thought him to be quack wallahi, ko ni da nake nurse bazan yi haka ba…” Dr Khalil ya cire wayar a handsfree da sauri laughing out loud, kallon wayar MD ya dinga yi babu ko kiftawa, yana ganin Dr Khalil ya cire a handsfree ya fizge ya mayar handsfree din, Mayraah tace “It’s not funny fa, na dade ina mamaki da na dawo gida jiya, ko level 4 student a medicine bazai yi abinda yayi ba” Dr Khalil yace
“To ai shikenan. a takaice dai kin fi sa sanin aikin likitanci kike nufi kenan?” Without thinking twice tace “Na fi sa composure a aikin, may be because i don’t shout and Nag” Dr Khalil na dariya yace “To sai anjima, zan kira ki” Tace “Ohk” MD ya dinga kallon wayar hannunsa, ita kuwa ganin Dr Khalil bai katse ba sai ta katse kiran, MD ya ajiye masa wayar kan Table a takaice yace “Call her back tayi providing International passport dinta gobe” Dr Khalil yace “Aa kai da kace… MD ya katse sa yace “Instruction din da Ceo ta bani kenan, don haka kayi abinda nace maka” Yana kai wa nan ya fita daga office din, dariya kawai khalil yake don har cikin ransa yaji dadin maganganun da Mayraah tayi a kan kunnensa, shi kansa jiya da
Dr Balogun ke basa labari yay mamaki, MD da ko jUSI cOmmon AsInmatic attacK aa ya sameta jiya ya kasa tabuka komai ya dawo kamar learner, to in ba rami me ya kawo rami, daukar wayar yayi ya sake kiran Mayraah bayan ta daga yace “Kina da international passport?” Ta dan yi shiru, sai kuma tace “Eh” Yace “In za ki shigo gobe sai ki taho da shi” Da mamaki tace “Why?” Yace “Ceo ce ta ce a sanar maki haka” Mayraah was a bit confused, ta ma rasa tunanin da zata yi, to me za ayi da passport din nata, sallama Dr Khalil yayi ya katse wayar. Washegari da taje asibiti har rana MD bai shigo ba, tun da safe ta kai ma Dr Khalil passport din nata, wajen karfe biyu suka shiga theatre za su yi wani aiki da Dr Balogun da Dr Khalil, tana kokarin saka nose mask before putting on her sterilized hand gloves kamar ance ta juya suka yi ido hudu da MD, dauke kai tayi don bata ma san ya shigo ba and she felt unhappy after realizing tare da shi za ay aikin, yawanci aikinta a Operation theatre bai wuce ta dinga mika Sterilized Instruments ba sai kuma suture, MD zata dinga mika ma Instruments din kamar wancan ranan, tana mika masa abinda ya bukata na farko suka hada ido sai kawai ya fadi daga hannunsa, wata nurse ta dauko wani Sterilized Instrument din da sauri ta kawo masa, sau hudu suna haka da shi, it is either idan zai maido mata sai ya fadi a hannunsa, ko kuma idan ta mika masa zai amsa sai a samu matsala, ita dai she is calm, Dr Khalil ya dawo inda Mayraah take yayi kasa da murya yace “May be u are tired, just go, nurse Sadeeya will continue…” Ta dan kallesa a ranta tace ko dai MD dink is tired, duk fa sun ga shi ke contaminating Instruments din not her, daga hannunsa suke faduwa ba nata ba, juyawa tayi ta bar wajen, karfe shidda saura driver dinta ya zo ya mayar da ita gida. Ranan friday da yamma Maheer ya iso daga kano via flight, Mayraah was so happy seeing him don ita da driver ne ma suka je airport tarbo su, yana gama gaisawa da Ammi ta kai sa wani daki dake parlor da damuwa tace “Yaya naga ka rame, what’s happening?” Yace “Aiki mana, kema nan da kwana kadan zaki ga kin rame ba dai kin fara aikin ba” Mayraah bata yarda ba, ta dinga insisting ya gaya mata what the problem is, Haseenah dai tafi minti ashirin zaune ita kadai a parlorn, Ammi da ke kitchen tana karasa girkin da take ta fito Parlon ganinta ita kadai ta nufi dakin da Mayraah ta kai Maheer, Ammi kanta wasn’t happy with how she saw Maheer, tana kallonsu tace
“Ka tashi ga chalet din can a bude yake, kun bar ta ita kadai parlor, ya kamata taje ta huta ita ma, Mimi zata kai maku abincin yanzu” Shi gaba daya ya ma mance da wata Haseenah, bayan some minutes ya mike ya fita a dakin. Bayan minti sha biyar Mayraah ta kai masu abincin Chalet, Yana bedroom Haseenah kuma na zaune parlon ta bi ta da ido har ta ajiye abincin sannan ta fita… Ammi na zaune parlonta da Maheer sai Usman dake danna wayarsa, da damuwa tace “Gaskiya ni dai hankalina bai kwanta ba kwata kwata, yaushe ma ta fara aikin ta samu full experience har matar zata ce xa aje conference da ita England? Ina manyan likitoci da Nurses din asibitin, aa gaskiya bazata ba” Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace
“Kai ya ka gani Barrister?” Sai a sannan Usman ya daga kai ya kallesu yace “It’s weird gaskiya, daga fara aiki ko sati biyu bata yi ba a kawo maganar fita waje, irin wannan tafiyar ai da experienced staffs ake zuwa” Maheer yace “Haka ne, nima kuma nayi mamaki” Ammi da hankalinta ya tashi tace “Ni gaskiya aikin ma sai a bari, kuma fa matar ba musulma bace, gwara a samar mata a wani waie kawai ta hakura da wannan” Murmushi kawai Maheer yayi, Ammi tace “Abbanku da na dawowa yau zan gaya masa, aikin ya fita kai na gaba daya wallahi” Mikewa Usman yayi ya fita daga parlon, Ammi ma ta mike tace “Kasan zan yi bakuwa bari in je in ga ko me aikin ta gama abinda na sa ta” Yace “Ohk” Ammi na fita parlon Maheer ya mike ya tafi dakin Mayraah. Kusan karfe uku Hajiya Maimuna mahaiftyar Haseenah ta iso gidan, tun da ta shigo hankalin Haseenah ya ki kwanciya, kawai dai tana zaune parlorn ne tana yaken karfin hali, Ammi ta tarbeta sosai suka gaisa da fara’a, Mayraah ta kawo mata abincin da aka mata, Hajiya Maimuna tace “Kawai na ce ko a gurguje ne in zo in ga gida kafin in koma kano, gida kam Alhamdulillah yayi kyau Allah ya sanya alkhairi, Allah ya sa rai aka yi ma” Ammi tace “Ni da na zata kwana za ki yi Hajiya?” Hajiya Maimuna tace “Ai daga gidan nan airport zan tafi, biki muka shigo tun ran juma’a wallahi, to nayi niyyar zuwa jiya asabar sai Allah bai yi ba sai yanzu” Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace “Toh amma ai za ki ci abinci Hajiya” Hajiya Maimuna tace “Wallahi na ci abinci kafin in fito, Alhamdulillah” Ammi tace “Da kika kirani dazu da safe har nake tunanin in kin zo akwai maganganun da za mu yi Hajiya” Sosai gaban Haseenah yayi mugun faduwa jin abinda Ammi tace, Mayraah dai na zaune parion ita ma, Hajiya Maimuna tace “Flight din na dare ne Hajiya, ko yanzu za mu iya maganar, Allah dai ya sa lafiya” Ammi ta dan yi murmushi, sai kuma tace
“To gaskiya ba lafiya ba Hajiya” Hajiya Maimuna tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, ina ji Hajiya” Haseenah ta mike zata bar parlon, Ammi tace
“Aa ki dawo ki zauna Haseenah” Sunkuyar da kai tayi ta koma ta zauna, Nan Ammi ta fara yi ma Hajiya Maimuna bayanin duk abinda ke faruwa bata boye mata komai ba, Daga karshe Ammi tace “Nasan kin san was maganganun nan was kuma ba lallai ki sani ba… To kin ji abinda ake ciki Hajiya” Hajiya Maimuna da ta kasa dago kanta sai zufa take bayan few seconds, tace “Amma baki kyauta min ba Hajiya, wallahi baki kyauta min ba, yanzu duk abubuwan nan su far babu wanda ya sanar min, na kwanaki ma da tayi dambe da kawarta Badiyyah banda ta kira kannena suka je suka yi rashin mutuncin da suka yi babu yawuna wallahi ban sani ba Hajiya, ban san komai ba, yanzu ni Haseenah zata tona ma asiri ta kunyata ni a idon duniya duk zatona tana zaune lafiya gidan mijinta?” Sai kuma ta fashe da kuka ta mike tace “To wallahi Allah ya isa tsakanina dake Haseenah, kin cuceni don sai ace tarbiyar da na maki kenan, bayan Allah a gani nayi iya bakin kokarina ganin na maki tarbiyyar da ya kamata dai dai gwargwado” a fusace ta rufeta da marita ko ina tana zaginta, Ammi ta rikota da sauri tace
“Aa Hajiya ba sai kin doketa ba, don Allah kiyi hakuri…..” Hajiya Maimuna na huci tace “Wallahi dama in ta kashe auren ta nemi gidan wata uwar ba ni ba, kar ta kuskura ta nufo inda nake, da dadi ha dadi haka navi hakuri a aidan ubanta.
Mayraah ta daga kai a hankali jin an bude kofar dakin, Ceo ta karaso da cup din hot chocolate ta zauna gefenta tace “Here dear” Mikewa zaune tayi ta amshi cup din hade da sauce dinsa tace “Thank you Ma” Murmushi ta mata tana kallonta calmly tace “You are welcome” Mayraah ta fara shan chocolate din a hankali, Ceo ta mike ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo dakin da few pizza slices a plate ta ajiye mata tace “Will you be okay with this?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Thank you Ma” daga haka ta dau slice daya ta fara ci, after some minutes ceo ta mike ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita ta jawo mata kofar ta rufe, Mayraah ta sauke idonta tana ci gaba da cin pizza din, bayan ta gama ta dau handbag dinta ta ciro wayarta dake ciki, cikin minti kadan tayi activating international roaming sannan ta fara dialing number Maheer, yana fara ring ya daga, a hankali tace “Yaya” Yace “Mimi” Tace “Ka fara bacci ne?” Yace “No Mimi, was waiting for ur call, i couldn’t reach you… ya hanya?” Kamar zata yi kuka tace yaya it’s soo cold here, i am so cold” Murmushi yayi yace “Yeah i know, akwai sanyi sosai, hope you are on ur jacket?” Kallon jacket din MD dake jikinta tayi, ta kara lullube jikinta da shi murya can kasa tace “Yeah” Yace “kina ina yanzu?” Ta kalli babban dakin tace “Gidan Ceo din mu” Da mamaki Maheer yace “Ceo dinku kuma? Why? Where are ur colleagues?” Mayraah tace “Ni kadai ce dai a nan, su ba a nan suka sauka ba, may be they lodge in hotel, kasan duk maza ne” Maheer ya ɗan yi shiru, can kuma yace “But that’s weird, why will she keep u in her home? Any way it’s fine…” Mayraah tayi shiru, yace “Hope you are comfortable?” Mayraah ta gyada masa kai a hankali tace “Yeah” Yace “To abinci fa?” Tace “Ta bani har na ci” Da damuwa Maheer yace “Gashi har muryarki ya fara nuna alamar sanyi ya kamaki” Tayi murmushi tace “Yaya kasan fa bana son sanyi” Yace “I know Mimi, shi yasa nake tausayinki” Tace “But ta ban heavy duvet” Yace “To better” Tace “Yanzu Yaya tambayar ta inda zan kalla inyi sallah zan je in yi?” Maheer yace “But she is a Christian how will she know? Ke baza ki gane qibla ba?” a hankali tace “Bazan gane ba, i am confuse” Yace “Ohk try asking her… Meye ta baki kika ci?” Mayraah tace “Ta bani hot chocolate da pizza” Yace “Ohk to ki samu kiyi sallan, idan kin idar sai ki kirani” Tace “Toh” Daga haka ta katse wayar, tana sauka daga saman gadon duk da dumin dakin she was still feeling cold, a hankali ta saka hannunta a sleeve din jacket din MD sannan ta nufi kofa walking slowly ta bude kofar, tana shiga babban parlon gidan ta dinga bin ko ina da kallo sai kuma ta kalli sama, Muryar ceo ta ji ta juya da sauri ta ganta a study room dinta with heap of textbooks a gabanta, tasowa tayi ta shigo parlon calmly tace “You need anything Mary Ann?” Ta gyada kai da sauri tace “I want to pray Ma….” Ceo tace “Ohh kina tambayar gabas kenan ko?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Yes Ma” Kalle kallen Parlon ceo din ta shiga yi, can tace “I can’t really tell where Aliyu faces and pray whenever he is around, let me call him on the phone sai ya gaya maki inda zaki kalla” Mayraah tace “Okay Ma” Ta koma ta dauko cellphone dinta ta fara kiran MD, yana dagawa tace “Aliyu zaka gaya mata inda zata kalla tayi sallah” Daga haka ta mika ma Mayraah wayar, Mayraah ta amsa da ladabi ta kai kunne tayi shiru, jin shi ma yayi shiru tace “Ina ji” Sai a sannan yace “Baki da Google a wayarki ne?” Taki ce masa komai saboda ceo dake tsaye, yace “In rashin kunya ne ai ba sai kin jira wani ya gaya maki yanda za ki yi ba, ba ni kika ce ma Quack Doctor ba, za ki sani” Mayraah dai taki cewa komai, Yace “Install Qibla finder on ur phone and stop being a nuisance” Mayraah bata sake tsayawa ta sauraresa ba ta katse wayar ta mika ma Ceo, Ceo tace “Ya gaya maki ko?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Eh ya gaya min” Ceo tace “Ae kina da darduma?” Mayraah tace “Ina da shi” Ceo tace “Toh sai kiyi using warm water kiyi performing ablution din so u won’t catch cold” Yanda Ceo tace mata haka tayi da ta koma dakin tayi alwala da ruwan dumi bayan ta fito daga bandakin ta bude akwatinta ta ciro darduman da Ammi ta sa mata sannan ta tada sallan, tana idarwa ta kwanta ta kashe fitilar dakin sannan ta lullube da duvet nan da nan bacci ya dauketa ko Maheer din bata kira ba, cikin dare taji zazzabi ya rufeta ga tari da ta dinga yi, wajen karfe uku ceo ta bude kofar dakin ta shigo ta kunna wutan sannan ta karasa ta zauna gefen gadon ta cire duvet din jikinta tana feeling temperature dinta tace “Are you okay?” Mayraah ta mike zaune tana rawan sanyi, Ceo tace “You are running temperature dear” mikewa tayi ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo da magunguna da ruwan gora, bude maganin tayi ta ba Mayraah ta amsa ta hadiye da ruwan sannan ta koma ta kwanta ta takure waje daya, ceo ta lullubeta da duvet tace “Sannu kin ji….” Kafin gari ya waye ceo ta shigo dakin ya fi a kirga, da asuba haka Mayraah ta daure ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan ta koma ta kwanta…. duvet din da taji an cire jikinta ya sa ta bude ido a hankali, MD ta gani tsaye kanta, ta mike da sauri ta ja duvet din ta wani daure fuska tana kallonsa, sae kuma ta ga CEO tsaye a bayansa, sunkuyar da kai tayi, Calmly yace “How are you feeling?” Ta gyada kai a takaice tace “Fine” Ceo tace “Will u take noodles for breakfast?” Mayraah ta gyada mata kai, ceo ta juya ta fita daga dakin sai da yaji ta kulle kofa sannan yace “Cire min jacket dina” Wani kallo ta jefa masa ta sauka daga kan gadon ta bude akwatinta ta ciro towel din wankan ta da shower gel with sponge sai toothpaste and toothbrush tayi wucewarta bandaki ta bar sa wajen tsaye, ya bi ta da ido har ta kulle kofar ta sa makulli, Bayan kusan minti daya ya gyada kai ya juya ya fita daga dakin, Mayraah na fitowa wanka taji kamar zazzabin ya sake dawo mata, ta ajiye jacket din hannunta ta kwanta ta dukunkune cikin duvet ta fi minti goma a haka daga karshe ta daure ta mike ta shirya, ta dau jacket din tana kokarin sa wa Ceo ta shigo dakin tace “In kin gama ki fito kiyi breakfast” Tana fita Mayraah ta saka jacket din sannan ta fito parlor, dinning area ta nufa ta zauna kujeran dake facing na MD dake kallonta ganin she is still wearing his jacket, garnished noodles with chicken Ceo din tayi mash, MD dai na rike da spoon yana kallon plate din abincin, lokaci lokaci yake satan kallon Mayraah, Mayraah ta fara cin abincin haka ma ceo, bayan some seconds ceo ta kallesa amma bata ce komai ba, mikewa yayi ya wanke fork din da knife din hannunsa a washing hand basin dake dining area din ya dawo ya zauna, Ceo tace “Ya maganar Therapy da nayi maka kwanaki?” Karo na farko da Mayraah ta fara ganin murmushin sa, yace “Soon Ma’am” Ceo ta ci gaba da cin abincin ta a nutse, Mayraah sai kallonsa take kasa kasa without letting him notice, gaba daya he doesn’t look comfortable a wajen, kawai ta ga ya jawo wani clean plate din ya goge da tissue ya juye abincin a ciki, Ceo ta kallesa ta ci gaba da cin abincinta, sae a sannan ya fara cin abincin, Mayraah bata ci abincin da yawa ba duk da ɗan manna masu ceo tayi a plate kamar wasu turawa, cikin minti kadan ya gama cin abincin ya mike ya bar dinning area din, duk suka bi sa da kallo, dakin da Mayraah take ya shiga, Mayraah dae sai kallon ikon Allah take, ba a dau lokaci ba sai ga shi ya fito, kallonsa Mayraah ta dinga yi da mamaki ganin Jacket dinta a hannunsa, yana kallon Ceo da ladabi yace “I will take my leave now ma’am” CEO tace “Ohk” Daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga Parlon yana rike da jacket din, Mayraah ta mike zata kwashe plates din Ceo tace “Ki bar shi, yanzu mai aikin zata shigo” Mayraah tace “Toh” barin dinning area din tayi ta tafi daki, bayan ta kulle kofar ta dinga kallon akwatinta dake bude, ta wani hade rai, saboda me zai bude mata akwati, is he even okay?? tsaki ta ja ta karasa ta kulle box din, kwanciya tayi ta dau wayarta tayi dialing number Maheer har ya katse bai daga ba, ta ajiye wayar ta rufe jikinta da duvet. Har ta fara bacci Ceo ta shigo dakin cikin sparkling suit da skirt din da iyakarsa gwiwa, sosai tayi kyau kamar wata baturiya, tana kallon Mayraah tace “You just stay back and rest Mary Ann, za mu je conference din yanxu, it’s only for today and tomorrow…. if u need anything feel at home ki shiga kitchen” Mayraah tace “Ohk Ma, nagode” Ceo ta mata murmushi sannan ta juya ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da ido har ta fita ta kullo kofar, a hankali ta jawo wayarta tayi dialing number Amminta…. Karfe sha biyu saura kiran Usman ya shigo wayarta, ta mike zaune daga kwancen da take da kyar saboda mugun ciwon da kanta yake mata, picking call din tayi ta gaishesa ya amsa yace “Mura kike ne?” A hankali tace “Eh” yace “Kin sha magani?” Tace “Na sha daxu” yace “Where is ur location?” Tace “Nima ban sani ba yaya” Yace “Ask around you” tace “Ni kadae ce a gida, sun tafi conference, i am not too fine saboda muran da nake….” yace “Hotel ne?” Tace “Aa gidan ceo, idan sun dawo i will ask for the address” ya ɗan yi shiru, sai kuma yace “Gidan Ceo? How comes?” Bai jira tace komai ba ya kara da cewa “Ok then, I will be waiting for the address” a hankali tace “Ohk” katse wayar yayi ta ajiye, gaba daya mura ya sa ta gaba and it’s making her feel sick, tana ganin lkcn sllh yayi ta tashi taje tayi alwala, tana idar da slln ta kwanta, cikin bacci ta ji an bude kofar dakin ta bude ido taga Ceo, mikewa zaune tayi, Ceo tace “Baki yi lunch ba Mary Ann” Ta murza ido tace “I slept off” Ceo tace “This is pass 3, ki fito ki ci abinci” Daga haka ta juya ta fita, Mayraah ta sauka daga kan gadon ta tafi parlor. Karfe biyar saura Mayraah ta fito daga dakinta tana kallon Ceo dake parlor tace “Ma ya iso, yana waje” Ceo tace “Ohk, ba kince Yayanki bane?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Yayana ne” Ceo tace “Let him in, it’s cold outside” Mayraah tace “Ohk Ma” Fita tayi daga parlon, inda ta hangosa tsaye ta karasa, idonsa na kanta har ta karaso ta kara gaishesa tana murmushi tace “Yaya kai ma ashe kana jin sanyi naga ka sa Jacket?” Yace “Kema kika ji sanyi balle ni” Er dariya tayi tace “To ai ni dama kowa yasan bana son sanyi, kai kuma baka bacci sai da AC” Yana kallon rigar jikinta yace “I see, where did u get this designer jacket u are putting on?” Mayraah ta kalli Jacket din MD dake jikinta da sauri, sai kuma ta kirkiri murmushi ta dawo gefensa tace “Ceo ce ta bani” Ya daga kafada yace “Ok, but ai na maza ne, yana da tsada sosai” Mayraah dai sai murmushin karfin hali take, Ya rungume hannunsa yace “But why did she decide to lodge u in her home? Na zata hotel zata biya maku….” Mayraah tace “Eh sauran maza ne duk suna hotel, ni ce kawai a nan, yaya tace fa mu shiga ciki akwai sanyi… She said u are welcome” Ko rufe baki bata yi ba, Ta yi ido hudu da MD da yayi parking ya sauka daga mota wanda da alama tasa ce, Usman ma kallonsa yake ganin he is walking toward them, shi ko bai sake kallonsu ba har ya wucesu, Usman ya bi sa da kallo ganin gidan da Mayraah ta fito zai shiga, sai kuma ya kalleta da sauri yace “Who is he?” Ta ɗan buda ido tace “MD dinta ne, he is the MD of the hospital” Usman yace “MD?” Mayraah ta gyada masa kai, yace “Shi ma a gidan nata ya sauka kenan??” Da sauri ta girgiza kai tace “Aa fa yaya, kilan ta kirasa ne ta aikesa amma ba nan ya kwana ba wallahi” Usman dai yayi shiru yana kallonta, can yace “Why did u do as if baki san sa ba, shi ma haka?” Da mamaki ta zaro ido tace “Yaya ai ni ban wani san sa ba fa, ka manta ni new staff ce a asibitin? We are not use to each other” Yace “You are never meant to get use to ur boss ai dama, do u know who a boss is? but i am surprise yanda zaki ga boss dinki and not greet him just like that in dai ba akwai wani abu ba, ga dukkan alamu ya sake maki fuska da yawa ko kuma akwai wani abu between u two….” Mayraah ta turo baki tace “Wani abu kuma yaya? To yaushe ma na fara aiki a asibitin, abinda ma zan iya kirga sau nawa na gansa a asibitin, office dinsa ma fa ba kowa ke zuwa ba, and his office is at the last floor of the hospital building, kawai dai ya fiye takura ne da masifa shi sa nake avoiding dinsa, baka ga dauke kai nayi ba kar ma ya gan ni” Usman ya jingina da brick wall din wajen yana kallonta as if not convince, ita dai ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds yace “Yaushe tace zaku koma Nigeria?” Mayraah tace “She said gobe ko jibi” Yace “An gama conference din ai?” Tace “Aa gobe ne last day” Yace “Shi kuma da ya zo yanzu sai yaushe zai bar gidan?” Mayraah ta zaro ido tace “Yaya ai nima ban sani ba, kilan aiki zata sa shi…. And na manta tace mu shiga ciki saboda sanyi” A takaice yace “Bazan shiga ba, do u need anything?” Ta girgiza masa kai tace “Aa” Yace “I will be on my way” A hankali tace “Da wuri haka yaya?” Yace “In kina bukatan wani abu ki kirani” Ta gyada masa kai, Juyawa yayi har ya fara tafiya ya sake dawowa yace “Why don’t u tell her u prefer hotel?” Ta zaro ido tana kallonsa, yace “Ohk kin fi son zama under same roof da katti ko? U are comfortable” A hankali tace “Yaya ni da ita kadai ne a gidan wallahi, kuma ai it’s a privilege ajiyeni da tayi a gidanta a matsayina na karamar staff” Bai sake ce mata komai ba ya juya ya bar wajen ta bi sa da ido, sai kuma ita ma ta juya tana tafiya a hankali ta nufi cikin gidan, tana shiga parlor ta kulle kofa, MD kadai ne zaune parlon zata wuce dakin da ta sauka yace “Hey come back here” Juyawa tayi ta kallesa, ko damuwa da hade ran da yayi bata yi ba, ta dawo parlon tana kallonsa, ya mike yace “Halan an gaya maki wasa ya kawo ki UK? Idan kina son haduwa da wani namiji me yasa baki biya kudin jirgi kin biyosa ba? Wato ga opportunity kin samu? ko kin zata yawon bude ido kika zo nan? Saboda kin ga Ceo na lallabaki ta kawo ki gidanta ta ajiye ki ko conference din ma baki je ba shine bari ki kira saurayinki, to let me give u this last warning har mu bar kasar nan bana son in sake ganinki da wani namiji don ba abinda ya kawo ki ba kenan, any body that wants to meet with u should follow u to Nigeria” A takaice ta juya ido tace “Har yayana? Kuma ai dai ban fita ba sai da na nemi permission daga wajenta kuma ta bani izini, why didn’t u ask her before waiting for me?” Shiru tayi jin ana saukowa downstairs, Ceo tace “Ya tafi yayan naki ne?” Mayraah ta juya ta kalleta tace “Eh ya tafi” Ceo ta shigo parlon ta karaso ta mike ma MD takardun hannunta tace “Here” Juyawa Mayraah tayi ta nufi hanyar daki, magana ceo take masa amma hankalinsa na kan Mayraah har ta shiga daki. Da daddare Mayraah na kwance wajen karfe sha daya Maheer ya kirata, tana daga wayar ya ji muryarta yace “Me ya faru?” Ta mike zaune da kyar tace “Cikina” Maheer ya mike zaune daga kwancen da yake yace “When did it start?” Kamar zata yi kuka tace “Not long ago?” Yace “Did u take any drug?” Ta girgiza masa kai tace “Since 8 na bar parlon, ita ma kuma tace she will be going to bed early…. ” Yace “Ko za ki je ki mata knocking, if not nasan baza kiyi bacci ba” Tace “Ni bazan iya tashinta ba, though it’s not as if the pain is that much for now, kilan sai zuwa gobe da safe, i will try and sleep now” Yace “Are you sure” Tace “Yeah, yanzu ma ai na fara bacci ka kirani” Yace “Toh kiyi baccin Mimi, Allah ya sauwake, i pray bazai matsa maki ba anjima….” Ta ɗan yi murmushi tace “Bye” ta katse wayar ta koma ta kwanta, ba a wani dau lokaci ba bacci ya dauke ta, can cikin dare axaba ya tasheta ta sauko daga saman gadon duk da mugun sanyin da ake sai taji kamar zufa ma take, ta jawo wayarta da kyar ta duba agogo taga karfe biyu saura, ajiye wayar tayi, tun tana kokarin ganin ta jure kawai daga karshe ta mike zumbur ba tare da tasan ma tayi haka ba, ta murda makullin kofar ta bude da sauri ta fita, hasken reading lamp da ta gani study room dake parlon ya sa ta karasa can da sauri, tana isa ta durkushe wajen ta fashe da kuka ta ma kasa cewa komai, matsar da littafin gabansa yayi ya mike da sauri yana kallonta yace “Menene?” Cikin kuka tace “Wallahi cikina ciwo yake min ka taimaka min” Ya kunna wutan wajen ya durkusa gabanta da sauri yace “Ya yake maki?” Ta kasa ce masa komai, keenly yake kallonta seeing how she is reacting to the pain yace “Dysmenorrhea?” Gyada masa kai tayi da sauri, ya mike ya bar wajen, magani ya yafi ya dauko mata da ruwa a glass cup, hannunta na rawa ta amsa ta sha, shi dai yana duke gabanta yana kallonta, don bata daina kukan da take ba, bayan kusan minti goma yace “Tashi ki koma daki…” Ko rufe baki bai yi ba cikin rawan murya tace “Aa wallahi bai daina ba, kilan allura zaka min, dama allura ake min” Daga sama har kasa ya kalleta seeing how confident she still is in between pains, Bai yi niyyar mata alluran ba saboda ta riga da ta sha drugs, but ganin she is still in pain har karfe uku kawai ya hada alluran ya mata, nan parlon ta fara bacci ya tasheta ta wuce daki. Washegari har karfe takwas bata tashi ba, har sai da ceo ta shigo ta tashe ta, bayan ta fito daga wanka ta shirya sannan ta dau wani jacket dinta dake akwati ta sa sannan ta fita parlor, Ceo na kallonta tace “Breakfast yana dinning table” Mayraah ta nufi dinning din ta zauna. Wajen karfe goma na safiyar Mayraah na waje tare da Usman da zuwan sa kenan, yana kallonta yace “Hope you are better now?” Ta gyada masa kai tace “Na ji sauki” yace “Me yasa baki kirani jiyan ba, though the ceo might not gree to that since….” Shiru Usman yayi bayan ya hango MD da ya fito daga cikin gidan, tunda Mayraah ta kallesa sau daya ta dauke kai gabanta na faduwa yake, kallonsa kawai Usman yake kamar yanda shi ma MD ke masa kallon cikin ido, har ya zo ya wucesu leaving his designer perfume scent behind, Usman ya dinga kallon jacket din da ya daura shoulders dinsa, can ya kalli Mayraah da ta juya kai taki kallonsu, a kan gado fa ta ajiye jacket din nasa ashe ya shiga ya dauka, Usman yace “Mayraah” Da sauri ta juya ta kallesa, yace “Wannan ba Jacket din da kika ce min Ceo ta baki bane?” Ta hadiye wani abu da kyar tace “Yaya shi ne, amma ai kilan shi ma ta basa ne ya sa….” Kana jin yanda take maganar kasan karya take, Calmly yace “Mayraah” Shiru tayi tana kallonsa, yace “Whose jacket is that?” Ta sunkuyar da kanta a hankali tace “Na shi ne, a airport ya bani saboda ni ban ciro nawa a akwati ba don ban san haka sanyin yake ba, shine sai ya bani nasa in saka” Kallonta kawai Usman yake, ta daga kai ta kallesa jin yayi shiru, after some seconds yace “To kin yi kokari” Tana ganin ya juya zai bar wajen ta marairaice tace “Yaya don Allah kayi hakuri, wallahi ina tsoron kar ka min fada ne shi yasa nayi maka karya” Yace “Infact karya kike still kice min babu komai tsakaninki da wannan mutumin, saurayin ki ne” Mayraah ta buda baki tana kallonsa da mamaki, juyawa yayi ya bar wajen ta bi sa da kallo, tafi minti uku tsaye wajen daga karshe ta juya a hankali ta fara tafiya zuwa cikin gidan…..
Yau ma dai kamar jiya Ceo bata bari Mayraah ta fita conference din ba tace mata tayi zamanta a gida akwai sanyi, Mayraah dai ta rasa gane amfanin zuwan ta kasar ga expenses na flight, tana zaune parlor ita kadai wajen karfe biyar saura tana karatun wani littafi da ta gani saman Centre table, the parlor was so warm hakan yasa bata jin sanyi duk da ta sa jacket dinta, not long ago mai aikin Ceo ta bar gidan bayan ta gama aikin da ta saba yi, bude kofar parlon aka yi ta daga kai ganin wanda ya shigo ta sauke idonta ta ci gaba da karatun ta without looking toward his direction again, he was smartly dressed in blue suit with white shirt a ciki, ya ajiye takardun hannunsa ya nufi Study room din Ceo ya dau wasu envelopes, dai dai nan ceo ta shigo parlon da wata baturiya da alamar kawarta ce, sai a sannan Mayraah ta ajiye littafin hannunta ta mike ta masu sannu da zuwa ta gaishesu da ladabi, Ceo na kallonta with concern tace “Kin ci abinci dai ko?” Mayraah tace “Eh na ci” Ceo tace “Ohk good, za ku je da Aliyu yanzu kiyi shopping duk abinda kike so, flight din ku na dare ne, you both will be leaving today not tomorrow, don gobe da asuba i have a flight to catch to US” a hankali Mayraah tace “To nagode Ma” Ceo ta mata murmushi tana kallonta, MD ya shigo parlon Ceo ta kallesa tace “Hope you are okay now?” Yace “Sure Ma’am” Tace “Ohk pls kar ku bata lokaci wajen shopping din so that she will get to arrange her things in order before leaving for airport” Zaunawa yayi Ceo ta zauna looking directly at him tace “idan kun koma Nigeria ka dau break din sati uku, you look stressed out… Ya kamata ka huta, Dr Ajay will take over till then” Yace “Ohk Ma’am, Thank you” Ta kalli Mayraah tace “Get ready….” Juyawa Mayraah tayi ta nufi dakin da take, karamin mayafi kawai ta dauka ta daura saman jacket din jikinta sai karamin handbag dinta sannan ta fito parlon, Ceo tace “Ki samesa a waje” sai a sannan Mayraah ta lura ya fita, tace “Ok Ma” daga haka ta fita parlorn, Mayraah wish she could tell her bata son shopping din saboda MD da tace zai kai ta amma bazata iya ce mata Aa ba, babban fargabanta ma kar su je shopping din su hadu da Ya Usman, da ya zata yi kenan? MD din da take avoiding bata son any type of encounter da shi ta yaya za su wanye lafiya wajen shoppin, tasan dole sai yayi displaying halinsa a can, tana isa gun motarsa ta bude front seat fuskarta babu walwala ta shiga ta zauna ta kulle motar, bayan few minutes ta ga ya gyada kai ya ja motar suka bar wajen, ta ɗan masa kallon gefen ido, a ranta ta riga tasan ko ta gaishesa ma ba lallai ya amsa ba shi yasa ta adana gaisuwarta kawai, suna isa mall din bayan yayi parking ya sauka, ganin haka ita ma ta sauka, tana biye da shi suka shiga ciki, cart ya dauka, ita ma ta dau daya tana kallonsa, ya nufi wajen turarruka ta bi sa da ido, sai kuma ta tabe baki ta juya ta fara duba inda zata ga chocolates da zata zabar ma Maheer, yawanci duk kayan ciye ciye ta deba a mall din, daga karshe ta dau ma Maheer, Ammi da Abba turare uku, har zata bar wajen turarrukan sai kuma ta turo baki ta koma ta daukar ma Usman ma, iyakar abinda ta dauka kenan a mall din, basu wuce minti ashirin ba suka fito bayan yayi payment, mamaki ta dinga yi ganin he didn’t create a scene with her in the mall, don ko bin ta kanta bai yi ba, ta zata nan ma sai yayi showcasing halinsa amma sai ta ga akasin haka, ta bude back seat ganin bai da alamar bude booth din motarsa ta ajiye ledojin siyayyan da tayi, bayan ta ajiye ta dawo gaban motar ta zauna keeping a straight face just as she saw him keep, driving kawai yake lokaci lokaci yana kallon agogon wrist dinsa…. Gaban wani apartment taga yayi parking daga karshe, ta juya tana kallonsa da mamaki, duk gidajen wajen iri daya kuma ko wanne da parking space dinsa a gaba sai garden ta baya, sauka yayi daga motar ita dai bata bude motar ba, yana kallonta da kyau yace “Ko ni zan sauko da ke?” Ta sake kallon gidan da ma anguwan gaba daya tace “Where is this?” Yace “Ni kike tambaya? Ki bari in kin shiga ciki sai ki tambayi warce tace a kawo ki, ai tana ciki she will explain” Mayraah dai kallonsa take ta kasa cewa komai, ya wani hade rai yace “Malama kina bata min lokaci” Bude motar tayi a hankali ta sauka tana kallonsa, ganin ya kulle motarsa da lock ya fara tafiya ta wani hade rai tace “To ban ciro ledan kayan da zan nuna mata ba ai” Banza yayi mata ya nufi entrance din gidan, ta wani hararesa sannan ta bi bayansa, yana bude kofar ya shiga, leaving the door open for her, ganin ta tsaya bakin kofa ya hade rai yace “Are you okay?” Ta sauke idonta sannan ta shiga parlon tana bin ko ina da kallo, kulle kofar yayi ta juya tana kallonsa, ya karasa cikin parlon ya zauna without looking at her, babu yabo babu fallasa ya nuna kofar wani daki yace “Go in there and meet her” Mayraah couldn’t stop looking at him, ya mike yana mata wani kallo yace “Baki ji na ne? Ko bata gaya maki airport za mu tafi daga nan ba?” Ta sauke idonta ta nufi kofar dakin da ya nuna mata tana tafiya a hankali lokaci daya kuma tana waigosa, shi ko ya ciro wayarsa yana dannawa, a hankali tayi knocking kofar ya daga kai ya kalleta, yace “Bude Ki shiga” Bata san sanda ta girgiza kai ba gabanta na faduwa tace “Wallahi ba kowa a gidan nan ka kawo ni” Mikewa yayi ya saka wayar aljihunsa yace “Ashe kin san babu kowa, to yau sai kin min bayanin dalilin da ya sa kika raina ni kika zama kece Boss din ni kuma kika maida ni staff….” Ta marairaice masa tace “Don girman Allah kayi hakuri wallahi bazan sake ba kaji har na rantse” Tana ganin ya nufota ta bude kofar dakin da gudu ta shige zata kulle sai ta ga babu makulli jikin kofar, kasa kakkwaran motsi tayi gabanta na bugawa, ganin ya shigo dakin ta durkusa tana kallonsa ta kara marairaice masa tace “Sir plss i am sorry ka yafe min wallahi sharrin shaidan ne, i promise i will be obedient from henceforth” Ya kulle kofar dakin yace “Ohk shaidan ne yasa kika raina ni kike zagina ko?” hankalinta yayi mugun tashi amma taki nuna hakan a fuskarta ta mike ta koma can jikin bango tana kallonsa tace “Wallahi ban taɓa zagin ka ba, me yasa zan zage ka bayan ka girmeni kuma kai boss dina ne” har wani zufa ke keto mata a goshi duk da sanyin da ake, tana ganin ya nufota ta wani hade rai tace “Wallahi zan maka ihu fa” Ya wara ido yace “Oh Haba? To yi ihun mana ki ga ko yana da amfani” Ta wani turo baki ta rungume hannu tace “To oya yi hakuri, wallahi na daina abinda nake har abada….” Tana fadin haka ta tafi gefen gado ta zauna ta nuna masa dan nesa da ita tace “Ka zauna let settle this amicably now….” Kallonta kawai yake, bata jira me zai ce ba, using her fingers to count tace “Kaga na farko daga yau zan dinga gaisheka duk inda na ganka, kai ma kuma dole ka amsa baza kayi ignoring ba, sannan zaka dinga treating dina yanda kake treating sauran staffs don naga su baka masu masifa ni kadai kake ma, sannan baza ka sake ce in maka gyara a office dinka ba tunda ba aikina bane na cleaners ne, and u should apologize for calling my first class a botany first class, and i will also apologize for calling a whole qualified Medical Doctor a Quack….” Confidently take maganarta looking at him straight in the eyes, sai kuma ta tallabi chin dinta da hannayenta biyu tana juya idonta tace “I am waiting for ur feedback now” Kasa ci gaba da kallonta yayi ya dauke kai…. Ta mike tace “If you’ve finish deciding ina parlor ina jiran feedback” Daga haka ta nufi kofa gabanta na mugun faduwa don kawai karfin hali tayi take maganar nan da take, ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin, zaunawa yayi gefen gadon yana shafa kansa, sai kuma ya mike da sauri ya ciro wayarsa dake ring yaga ceo ce, zaro ido yayi ya fita daga dakin da sauri, ga mamakinsa bai ganta parlon ba, yana fita waje ya ganta can jikin mota a tsaye, dauke kai tayi bata sake kallon direction din ba, ita dai ba ta samu ta fito daga gidan lafiya ba, rufe gidan yayi ya karaso parking space din yana kallonta yace “Kin zata kina da wayo ko? Zaki gane” Ta marairaice tace “But i was waiting for ur feedback” Bude motar yayi ya shiga, ita ma ta bude front seat, sai da ya tada motar sannan yayi dialing number Ceo yace mata suna hanya, cikin yan mintuna suka isa gidan, Ceo ta dinga kallon ledan hannun Mayraah tace “Shopping nace kiyi what’s this little thing u bought?” Mayraah tayi murmushi tace “Wannan ya isheni Ma” Ta kalli MD tace “Meye wannan din ta siya?” Yace “Na mata magana tace she doesn’t need anything just chocolate” Mayraah ta kallesa da sauri, Ceo tace “Ohk then, je ki shirya a daki” Mayraah ta wuce dakin rike da ledojin. Karfe bakwai da rabi na dare suka bar gidan Ceo zuwa airport, ita da kanta tayi driving dinsu zuwa airport, Bayan Mayraah ta sauka, MD ya fiddo akwatinta a booth, Ceo ta mata side hug tace “Take care of ur self dear, my regards to ur parent” Jikin Mayraah yayi sanyi ta daga kai tana kallonta a hankali tace “Ma yaushe zaki zo Nigeria?” Ceo ta mata murmushi tace “Sai bayan wata biyu in sha Allah” MD dai na tsaye sai kallonsu yake, Mayraah tace “To Allah ya kai mu, thank you so much Ma, i appreciate” Ceo tace “You are welcome” Daga haka ta daga ma MD hannu, ta shiga motarta ta bar airport din, Mayraah ta bi motarta da ido babu ko kiftawa, lokaci daya ta juya taga MD har yayi shigewarsa cikin airport din ya bar ta wajen a tsaye, Business class Ceo ta sa MD yayi masu booking, but because he wants to rest kasancewar he wasn’t too fine a conference ranan kawai sai ya biya masu ticket din first class. Sune farkon boarding plane din, Mayraah bata taɓa shiga first class ba iyakarta business class, wajen karfe takwas da rabi jirginsu ya tashi, ya kira flight attendants telling them he is taking nothing don bai ma son a zo a tambayesa, bayan Flight attendants din ta bar wajen, after few minutes Mayraah ta juya ta kallesa taga ya kwanta ya lullebe da duvet, two hours into the flight Mayraah tayi bacci. Bayan awa daya ta farka, ta mike zaune tana kallonsa, har sannan a kwance yake idonsa a lumshe sae karamin towel dake forehead dinsa, ta mike tana tafiya a hankali ta nufi inda yake, bude ido yayi da sauri jin motsi kusa da shi, ta ɗan koma baya kamar munafuka tace “Are you okay?” Flight attendant ce ta iso wajen with pain reliever, Mayraah ta bi ta da ido har ta basa maganin sannan ta zuba masa ruwa a daya daga cikin glass cups da aka ajiye masa da goran ruwa uku, bai amshi glass cup din ba ya dau bottle water instead ya kurbi ruwan ya sha maganin, bayan Flight attendants din ta ajiye glass cup din hannunta ta kalli Mayraah don tana son sake masa labulen wajen for his privacy, kafin tace komai Mayraah tace “We are together” Flight attendants din ta mata murmushi tace “Okay Ma” juyawa tayi ta bar wajen, Mayraah ta kai hannu kan karamin towel din forehead dinsa taji a jike yake da ruwa, cire towel din tayi don har a sannan he is running temperature, ta tafi toilet ta kara jika towel din sannan ta dawo, ta duka kusa da shi zata daura a goshinsa ya fixge towel din yace “Don’t worry, je ki ci gaba da baccin ki” Ta wani hade rai tace “But i am a nurse” Daga sama har kasa ya kalleta yace “Nurse with no license and working experience, pls go back to ur seat Madam and sleep” Kwace towel din tayi tace “I don’t mind what ever u will say, but i am sticking to the ethical obligations of a Nurse to a patient” Daga haka ta fara goge masa forehead dinsa that is hot with the towel din, kallonta kawai yake, sai kuma ta cire duvet din jikinsa tace “You are running temperature so there is no point in covering ur body with a Duvet” Ko minti goma ba ayi ba ya sake komawa bacci. Kafin su isa Nigeria he felt much better saboda painkillers da ya sha a jirgin, karfe biyu da rabi na dare suka sauka airport din Abuja. Bayan ta dauko akwatinta ta kalli inda yake zaune ya jingina da kujera idonsa a lumshe, shi dama bai taho da komai ba, ta karasa wajen da yake zaune tace “Zan kira yayana ya daukeni, u can leave me here” Ya bude ido da sauri yana kallonta yace “Karya kike ba yayanki bane” Tace “To naji ba yayana bane” Ya mata wani shegen kallo ya mike ya fara tafiya, he is just acting he is fine whereas he is sick, ta bi bayansa suka fito haraban Airport din, taxi suka shiga…. Bayan sun fita daga airport din yace “Ni zan gaya masa address din gidanku da kika yi shiru?” Tace “To ai naga kasan gidan tunda ka taɓa bin Dr Khalil” Juyawa yayi ya kalleta da sauri, ta maida hankalinta kan driver tana gaya masa address din gidan da zai kai ta, MD yace “Shi Khalil din ne yace maki ni na bi sa?” Without looking at him tace “Ai ba sai ya gaya min ba i saw it with my eyes” Bai sake tanka ta ba cause ba shi da strength din hakan, 10 mintues into the journey ya fara bacci, ta ɗan juya ta kallesa, da zata matsa ta koma edge din kujeran kuma dai kawai ta basa access to her shoulder, har suka isa gida yana bacci, Mayraah ta juya ta kallesa, after few seconds calmly tace “I am home” A hankali ya bude ido, sai kuma ya gyara zamansa da sauri, ta ɗan kyabe baki ta bude motar tace “Sai da safe” Daga haka ta sauka ya bi ta da kallo, drivern taxi din ya sauka ya dauko mata akwatinta a booth, bayan ta amsa ta kalli MD dake kallonta, sauke ido tayi ta daga masa hannu sannan ta juya da sauri ta nufi gate din gidan ya bi ta da kallo, Kwankwasa gate din tayi taji security na tambayarta waye, bayan ta basa amsa ya bude gate din ta shiga cikin gidan ya kulle gate din, sai a sannan MD ya sa taxi driver din ya ja motar suka bar unguwan. Mayraah ta zauna saman kujeran dake compound ta ciro wayarta tayi dialing number Maheer, sai da ya kusa katsewa ya daga a hankali yace “Mimi” Ta wara ido tace “Sorry i woke u up” Yace “Ya aka yi? Hope ba ciwon cikin bane?” Tana murmushi tace “Aa ba shi bane, ai tun ranan da aka min allura bai kara ciwo ba, yaya na dawo” Maheer ya mike zaune yace “Da gaske?” Tace “Eh” Yace “Yaushe?” Tace “Just now” Yace “In taho airport inyi picking dinki ne?” Tayi dariya tace “Eh ka taho” Yace “Right away” Daga haka ya katse wayar, mayar da wayar tayi cikin handbag dinta, ta daura handbag din kan akwatin sannan ta karasa chalet da sauri ta tsaya bakin stairs yanda bazai ganta ba har sai ya sauka kasa, bayan kusan minti bakwai sai gashi ya fito sanye da jallabiya, yana sauka stairs din tayi er kara saitin fuskarsa, ya juya da sauri yana kallonta da mamaki, ta kyalkyale da dariya tace “Wallahi nasan ka ji tsoro Yaya” Tun da Haseenah taji ya bude kofar dakinsa dama ta farka daga baccin da take a nata dakin, sai ta fito parlor, bai bi ta kanta ba as usual, tana ganin ya fita compound ta taho window tana leka waje, kawai kuma sai taji muryar Mayraah, Maheer dake kallon Mayraah daga sama har kasa yace “Wa yayi dropping din ki?” Mayraah na murmushi tace “MD dinmu, taxi muka shiga a airport din” Yace “Har kin kara haske daga zuwa Uk, are you sure we are not relocating there?” Tayi dariya tace “Wani haske? Bayan sanyi ake a can sosai, har fa mura sai da nayi, ni dai bana son kasar saboda sanyi” Yana murmushi yace “To ina akwatin?” Ta nuna masa inda ta bar akwatin tace “Yaya i bring you so many chocolates irin wanda kake so” Yace “Really” Tace “Wallahi” Gun akwatin ya nufa ta bi bayansa, Haseenah dake jikin window tana jin duk abinda suke cewa ta bi su da ido.
Mayraah na biye da Maheer dake dauke da akwatin ta suka shiga main building din gidan, ya kunna wutan parlon cause everywhere was dark, ya juya yana kallonta yace “Nasan dai kinyi bacci a jirgi” Tana cire jacket din jikinta tace “Eh nayi bacci amma ai ba da yawa ba, though i am not sleepy now” Ya kalli agogo dake nuna karfe uku da kusan rabi yace “Yunwa fa?” Ta wara ido tace “First class fa muka shiga yayana, kasan me da me na ci?” Da mamaki yace “First class? Ke da wa? Hospital din ne ya biya maku first class?” Tayi murmushi ta zauna tace “Wa enda muka je conference din mana, tare muka dawo da su ai” Ya zauna yana facing dinta yace “So how was the conference like?” Ta langwabar da kai tace “Duk fa ban je ba Yaya” Yace “Baki je conference din ba?” Ta gyada masa kai tace “Kawai a gidanta na tsaya duk 2 days din nan” Shiru Maheer yayi bai ce komai ba amma deep down him yana mamakin amfanin zuwa da ita kasar da aka yi, can yace “Ku nawa ku ka je?” Tace “I think 4, yaya Abba yana nan?” Maheer ya girgiza kai yace “Yana kano” tace “Ohk…. yaya har bana son in tuna cold din kasar” Yayi murmushi yana kallonta, Hira ta dinga yi masa a parlon yana biye ta duk da baccin da yake ji don dama wajen karfe biyu ya kwanta, ya fara bacci ba dadewa ta kirasa, har kusan lokacin da za a tada sallan asuba suna zaune parlon, suka ji ana saukowa downstairs, Maheer ya kalli agogo yaga nan da minti goma za a tada sallah a masallaci, tuni Mayraah taji kamshin turarensa ta gane shi ne, yana saukowa parlor tun da ta kallesa sau daya ta dauke kai tana ci gaba da yi ma Maheer maganar da take masa, kallo daya shi ma ya mata ya nufi kofa ta bi sa da kallon gefen ido har taga ya bude kofa, tayi kasa da murya tana kallon Maheer tace “Yaya yaushe ya dawo?” Maheer yace “Jiya da rana” Ganin ya ja kofar parlon bayan ya fita ta wani taɓe baki tace “Yaya kasan abinda yayi min ne a UK?” Maheer yace “Me ya ma ki?” Tace “Ai babu ruwana da shi daga yanxu, kawai fa daga….” Mikewa tayi da sauri ganin Usman ya dawo Parlon ashe yana jikin kofar bai tafi ba, tana ganin ya nufota ta ruga sama da gudu tayi bangaren Ammi, ya juya ya fice daga parlon, Maheer dai ya bi sa da kallo, Mayraah na shiga parlon Ammi ta kulle kofar tana turo baki, Ammi da ta fito daga bandaki ta taho parlon jin alamar an shigo, buda baki tayi tana kallonta tace “Mayraah” Dariya Mayraah tayi ta tafi da sauri ta rungumeta tace “Ammi na dawo” Ammi tace “Ikon Allah, yaushe kika dawo?” Mayraah tace “Dazun nan wajen karfe uku” Da mamaki Ammi tace “To wa ya dawo dake gida?” Mayraah tace “MD din mu” Ammi tace “Maa sha Allah, welcome daughter” Mayraab bata yarda ta bar bangaren Ammi ba don tsoron tafiya dakinta take ta hadu da Usman, wajen karfe shidda Ammi ta sauka downstairs don hado mata shayi ta kawo mata da bread, Ammi na ajiye shayin ta tadda ta ta jinginar da kanta da kujera ta fara bacci, Ammi ta dafata tace “Tashi ki sha shayin sai kiyi wanka ki kwanta” Mayraah ta buda ido a hankali tace “Ammi akwatina na downstairs” Ammi tace “Aa babu akwati downstairs, ko Maheer din ya kai maki daki” Mayraah tace “Zanyi brush in fara wanka kafin in sha shayin” Ammi tace “To je kiyi, in kin gama sai ki hado wani shayin bari in sha wannan” Mikewa Mayraah tayi ta fita daga bangaren Ammi da sauri ta tafi dakinta, tana shiga ta kulle da makulli. Wajen karfe takwas tana parlon Ammi ta gama breakfast kenan Usman ya shigo parlon, tun da ta kallesa sau daya taki dago kai Ammi ta amsa gaisuwar da yake mata, yace “Zan je kaduna Ammi” Ammi tace “Kayi breakfast din?” Yace “Nayi” tace “Toh Allah ya tsare hanya, Allah ya kiyaye, yau din zaka dawo?” Yace “Aa sai Monday in sha Allah” tace “Toh Allah ya kai mu lafiya, ya tsare hanya, drive safely pls” Yace “In sha Allah” Daga haka ya mike ya nufi kofa, Ammi ta kalli Mayraah tace “Kun gaisa ne da shi?” Mayraah ta gyada kai tace “Tun daxu da na dawo” Mikewa tayi ta dau wasu chocolates da turare daya ta fita daga parlon, dakinsa ta nufa gabanta na faduwa, ta ɗan yi knocking kofar a hankali sannan ta bude, yana rufe karamin box dinsa, taki bari su hada ido ta kulle kofar, a hankali tace “Yaya don Allah kayi hakuri, i am so sorry about what happened” Jin yayi shiru ta daga kai ta kallesa, calmly yace “Wani abu ya faru ne?” Ta ɗan yi murmushi tace “Bayan nasan fushi kake da ni har yanzu, ni dai plss i am sorry yaya, ga tsaraba nan nayi maka” Bata jira cewarsa ba ta tafi ta bude jakar da ya ke rufewa ta zuba masa chocolate din a ciki ta kulle, sannan ta karasa inda turarrukansa suke a dakin ta ajiye turaren hannunta, sauke idonsa yayi daga kallonta, ta karaso kusa da shi tace “Pls ka hakura yaya?” Yace “I will think about it” Murmushi tayi tana kallonsa. Da yamma Maheer na zaune parlon Ammi, Mayraah ma na parlon, Ammi ta girgiza kai not convinced with what Maheer is telling her tace “Ni manufar tafiya da ita nake son sani tun da ba a bar ta taje conference din a kasar ba, why will they insist on going with her? This doesn’t sound right Maheer, wallahi ni fa hankalina yaki kwanciya da aikin nan har yanzu” Maheer ya kalli Mayraah dake kallon Ammi, Ammi ta girgiza kai tace “Ni bazan boye maku ba kawai naji ban ma yarda da ceo din ba, ta yaya daga fara aikin yarinya ko wata biyu ba ayi ba ta dage sai anje wata kasar da ita bayan ga tsofaffin ma’aikata a asibitin, kuma tun da Usman ya dawo yace min gidanta ta sauke ta na kasa nutsuwa, a ina aka taɓa yin haka?” A hankali Mayraah tace “But Ammi she is so kind….” Ammi ta mike tace “Ban yarda da kindness din nan nata a kan ki ba, ai ba ke kadai bace worker a asibitin, why is she just being kind to you?” Daga haka ta yi wucewarta daki Mayraah ta bi ta da kallo, can ta daga kai ta kalli Maheer dake kallonta a hankali tace “Ammi zata ce kar in kara aikin ko?” Maheer ya kwantar da murya yace “Bazata ce ba, do not worry i will talk to her” Mikewa Mayraah tayi ta nufi kofa ta fita daga parlon ta koma dakinta. Da yammacin Washegari da ya kasance Saturday Mayraah ta gama jera kayanta da aka goge mata a press ta fito daga dakin zata sauka downstairs ta hango Maheer zaune Parlon shi kadai yana danna wayarsa, makalewa jikin karfen stairs din tayi tana kallonsa kamar ta samu TV, ta fi minti shidda tsaye a gurin kawai taga ya dago kai, da sauri ta manne da bango yanda bazai ganta ba tana zaro ido, amma tuni ya ganta, mikewa yayi ya nufo stairs din, tana ganin haka ta juya da gudu ta wuce bangaren Ammi, ganin wajen wayam ba kowa kawai ya sauka downstairs ya ci gaba da zaman sa. Da daddare Mayraah ta fito parlon Ammi zata tafi dakinta ta kwanta don har ta fara bacci ta hadu da Maheer a hanya zai je gun Ammi, yana kallonta ganin taki kallonsa zata wuce bayan ta gaishesa yace “Mayraah” Juyowa tayi tana murza idonta a hankali tace “Yaya bacci nake ji” Ya kama hannunta yace “I know… is there anything u are wanting to say?” Bata yarda ta kallesa ba still tace “Something? Like what?” Sai a sannan ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, ta ɗan yi murmushi murya can kasa tace “Not at all yaya, dazu kawai naga kana ta gyangyadi shine nake kallon ka fa” Ya wara ido kafin yace komai ta marairaice tace “Zan fara baccin fa a tsaye a nan Yaya” A hankali yace “To fara” Jingina tayi da bango ta lumshe ido slowly, kallonta kawai yake babu ko kiftawa, bayan few seconds ita ma ta bude ido tana kallonsa, bude kofa da taji anyi ya sa ta kifta ido da sauri ta janye hannunta daga nasa, juyawa yayi ya nufi downstairs ta bi sa da kallo har ya sauka, Ammi ta karaso tana kallonta da mamaki tace “Me kike a nan? Baki tafi kin kwantan bane?” Kame kame ta fara yi sai kuma ta wuce dakinta da sauri, Ammi ta bi ta da kallo har ta shiga dakin ta kulle. Mayraah na isa daki kwanciya tayi ta lumshe ido, gaba daya ta nemi baccin ta rasa, tayi ta juye juye har daga karshe baccin ya dauketa wajen karfe sha daya da rabi. Da safe tana kitchen tana dafa ma Ammi shayi Maheer ya shigo kitchen din, tana gane shi ne taki dago kanta tana ci gaba da abinda take, Calmly yace “Good morning Mimi” Still not looking at him tace “Good morning yaya” Ya ajiye cup din hannunsa ya juya ya fita, sai a sannan ta bi sa da kallo sannan ta ci gaba da abinda take. Tana daki wajen karfe sha daya wayarta ya fara vibrate ta jawo ganin Dr Khalil ne tayi picking don tun da ta dawo sau daya ya kirata ya mata sannu da zuwa, bayan sun gaisa yace “Hope kin huta enough?” Tana murmushi tace “Sure” Yace “MD yace a gaya maki ki kawo account details dinki today, za kuma ki amshi ID card….” Mayraah tace “But i wrote down my account details the other day, ID card kuma ai gobe monday ba sai in amsa ba goben” Dr Khalil ya ɗan yi murmushi yace “To dai hakuri za kiyi ki zo tunda yace ki zo yau din, shi ma kin ga baya shigowa sundays infact baya ma da lafiya tun da ku ka dawo har drip sai da na sa mashi, but he is around today, ko zuwa karfe daya ne sai driver ya kawo ki, nasan duka duka baza ki wuce minti talatin ba a asibitin, kin ga driver din ma zai iya jiranki” Mayraah da gaba daya mood dinta ya canza don bata son fitan, a hankali tace “Ohk” Bayan ta katse wayar ta mike ta je ta samu Ammi a parlorn ta, bayan ta sanar mata abinda Dr Khalil ya kirata ya gaya mata, a hankali Ammi tace “Mimi, ina ga fa hakura za kiyi da aikin nan” Mayraah ta daga kai tana kallon Ammi babu ko kiftawa, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace “Wallahi hankalina yaki kwanciya har yanzu, i am so disturb this past days na rasa dalili, ina ji a jikina kamar akwai abinda zai faru” Mayraah da jikinta yayi sanyi tayi shiru tana kallon Ammi, can ta sunkuyar da kai, Ammi ta mike ta koma kusa da ita ta jawota jikinta, nan da nan hawaye ya kawo idonta amma bata bari Mayraah taga hakan ba ta goge idon da sauri tace “I don’t know why i am afraid Daughter, duk kwanan nan wasu irin mafarkai nake da ban gane kansu ba” Mayraah tayi karfin halin cewa “In sha Allah Ammi na bar aikin since you are not comfortable with it” Ammi dai tayi shiru tana rungume da ita wasu hawayen na taruwa idonta. Bayan azahar Mayraah na kwance dakinta taji wayarta na vibrate, mikewa zaune tayi sanin bazai wuce Dr Khalil ba, to me ma zata ce masa, kai tsaye dai bazata ce masa Ammi tace ta bar aikin ba, a hankali ta jawo wayar bayan ta gama tunanin abinda zata ce masa, amma sai taga wani layi with special digits ne ke kiranta, ta dinga kallon screen din babu ko kiftawa, babu wanda ya fado mata sai Musharraf, lkci daya taji jikinta yayi sanyi and she just believe shine ke kiran nata tunda babu wanda ke da layin bayan yan gidan da Dr Khalil, picking call din tayi kafin ya katse ta sa hands free gabanta na faduwa tana jiran jin muryarsa, “Didn’t Khalil pass my message to you?” Mayraah tayi shiru, ko kadan bata yi wani mamakin inda ya samu numberta ba bayan da ta ji muryarsa, after some seconds ta langwabar da kai tace “A gidanmu ance sai gobe zan je tunda kowa yasan yau ai bana zuwa aiki” Jin yayi shiru tace “Hello” Yace “No bari nayi ki gama rashin kunyan” Ta dan tabe baki tace “Abinda aka ce a gidanmu fa nake gaya maka ai ba rashin kunya bane” Yace “Za ki sani” Daga haka ta ji ya katse wayar, ta ajiye a hankali ta koma ta kwanta maganganun Ammi na dawowa kanta, lkci daya hawaye ya cika idonta. Bayan la’asar Mayraah ta je kai bowl din da tayi ma Ammi fruit salad a ciki taga Maheer zaune parlor yana kallo, throughout yau bata gansa ba, bayan ta gaishesa ta tafi kitchen da bowl din ya bi ta da kallo, ba a dau lokaci ba ta fito ta xauna kujeran dake facing dinsa tace “In maka girki yaya?” Ya dan buda ido yace “In baxan takura Mimi ba” Murmushi tayi ta mike ta wuce kitchen…. Kafin karfe shidda Mayraah ta gama girka masa favorite dinsa, bayan magrib ganin bai shigo gidan ba ta dau wayarta tayi dialing numbersa yana fara ring ya daga a hankali yace “Mimi” Tace “Yaya na gama kuma naga baka shigo ba” Yace “I am having headache Mimi ki kawo min nan” Da damuwa tace “To bari in kawo maka yaya, Allah ya sauwake” Daga haka ta katse wayar ta dau hijab din da tayi sallah ta mayar jikinta sannan ta fita, downstairs ta sauka zuwa kitchen bayan ta dau abincin iya wanda zai iya ci ta fita ta kai masa chalet, dukawa gabansa tayi ta ajiye masa abincin tace “Idan ka ci sai ka sha magani” Yace “Yes dear” Mikewa tayi ta fita daga parlon, Haseenah da ta shigo kitchen take tsaye tun farkon da Mayraah ta kirasa yace mata ta kawo abincin, tana jin alamar Mayraah ta fita ta kwala wani kara me karfi, Maheer dake kwance ya mike zaune yana kallon kitchen din, banda zuciyar musulunci babu abinda zai kai sa kusa da kitchen din nan, but because of the kind of heart he have haka nan ya tashi ya tafi kitchen din, ƙasa ya ganta a kitchen din tana sauke numfashi, ya karasa yana kallonta ta dinga nuna masa kirjinta, tun dawowarsu gidan sai ranan yayi mata magana yace “Me ya faru” Da kyar tace “It’s paining me” Nan da nan hawaye ya fara sauka idonta tana girgiza kai, sai da ya kai zuciyarsa nesa ya daga ta yana jin wani mugun tsanar ta har cikin zuciyarsa, suka fito daga kitchen din da kyar tana numfarfashi taki zama parlor tace “Daki zan je” Haka nan suka tafi dakin nata, hawaye na sauka idonta ta dinga juye juye tace “Wallahi mutuwa zan yi ciwo yake min sosai” Shi dai yana tsaye yana kallonta as if trying to diagnose what she said is wrong with her, muryarta na rawa tace “Kilan Ulcer ne ranan na bar maganin a kitchen din Ammi da ya tasar min” After few minutes ya juya ya fita daga dakin tana jin ya bude kofar parlor sannan ya rufe ta taso da gudu ta leka parlon ganin ya fita ta koma dakinta da sauri ta jawo karamin ledan dake karkashin gadonta ta fito parlor a guje ta nufi inda Mayraah ta ajiye masa abinci hannunta na rawa ta bude warmer din miyan ta juye abinda ke cikin kwalban gaba daya a miyan, ko ina na jikinta rawa yake, da yatsanta ta jujjuya miyan sannan ta kulle da gudu ta koma daki ta tura ledan da kwalban karkashin gado ta shiga bandaki ta wanke hannunta da handwash ta fito ta kulle kofar bayan ta goggoge hannunta ta koma inda ya bar ta ta kwanta ta kulle ido, bayan few seconds ta ji ya bude kofar parlon ta dinga sauke numfashi a wahale idonta a kulle har ya shigo dakin…..
78….
Haseenah na makale jikin window taki fitowa sai zare ido take tun bayan da Bilkisu ta zo tana kuka ta kira Maheer, she doesn’t even know weda she should be happy or otherwise, duk da ba haka ta so ba, har kasan ranta tayi bakin ciki da ba Maheer bane ya ci abincin nan, amma Mayraan ma dai da ta ci Allah Ubangiji ya sa ta mutu kawai, addu’ar da ta dinga yi kenan feeling no epitome of remorse akan abinda ta aikata, tana cikin wannan tunanin taga Ambulance ya shigo gidan, duk iya leken da take bata ga wanda ya saka Mayraah a Ambulance din ba, amma tana ta jiyo kukan Ammi, sai kuma ta juya da sauri ta koma dakinta tana tunanin inda zata yi discarding kwalban poison din don tasan ko hauka take bazata saka a bola ba…. MD har zai shiga Ambulance din bayan paramedic da suke ciki sun saka ma Mayraah oxygen with Maheer by her side, sai kuma ya juya ya kalli
Ammi dake biye da shi a gigice tana kuka kamar ranta zai fita ita ma tana kokarin shiga Ambulance din, speaking calmly yace “In sha Allah she will be fine, bazai yiwu ki shiga Ambulance ba…” Bai jira cewarta ba ya shiga Ambulance din suka bar gidan, Ammi na kara rusa kuka, Sai da Haseenah ta ji fitar Ambulance din ta fito compound a rikice ta nufo Ammi da gudu tace “Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, me ke faruwa Ammi, na fara bacci naji kamar siren, meye ke faruwa?” Hankali tashe take tambayar tana zaro ido, Ammi ko kallonta bata yi ba ta bi bayan Ambulance da sauri ko takalmi babu, Haseenah ta koma gun Bilkisu da ke kuka tace “Wai me ke faruwa Bilkisu? Me 78…..
RA
ke faruwa a gidan nan” Cikin kuka Bilkisu tace
“Wallahi Mayraah ce babu lafiya har kumfa na fitowa bakin ta” Haseenah ta dafe kirji tana gwalo ido tace
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, kuma ta mutu?”
Bilkisu bata tsaya bata amsa ba ta shiga cikin gida da sauri don dauko ma Ammi takalmanta da Hijab ganin har ta fita gate, dama kuma har ta haddace sunan asibitin da ta gani jikin Ambulance din. Maheer na zaune babban reception din asibitin ya dafe kansa da yayi masa nauyi, lokaci lokaci yake dagowa ya kalli Ammi dake reception din ita ma tare da Bilkisu dake ta kokarin kwantar mata da hankali take bata hakuri amma kamar tana kara tunzurata don Ammi tayi kuka har taji ba dadi, gaba daya ta dawo bata da wani kuzari, sun kusa awa biyu reception din a zaune amma babu likitan da suka ga ya fito har sannan, wannan ya kara daga ma Ammi hankali sosai ba kadan ba, wajen karfe sha biyu da rabi Dr Hamid ya fara fitowa, Maheer ya mike da sauri yana kallonsa don yayi recognizing dinsa as one of the doctors that went inside the emergency room with Mayraah, karasawa yayi gun sa, Ammi ma ta mike da sauri ta nufesa gabanta na mugun faduwa, Dr Hamid na kallon Maheer yace “She is been transferred to ICU….” Yana fadin haka ya bar wajen, Maheer ya bi sa da kallo, Ammi ta fashe da matsanancin kuka ta riko Maheer tace “Maheer me hakan ke nufi? ICU naji fa yace” Maheer yayi kokarin calmly dinta yace “Dama za a kai ta can ai, saboda pulse dinta da ya dauke na wani lokaci, in sha Allah she will be fine Ammi” Karfin 78…..
hali kawai shi ma yake yana kokarin kwantar mata da nata hankalin. Karfe biyu saura na dare Dr Khalil ya shigo reception din daga ICU, Ammi ta mike da sauri tana goge hawayen idonta ta nufesa don taga kamar kusan duk likitocin asibitin sai da suka shiga Emergency room din, muryarta na rawa ta kamo hannunsa tace “Plss tell me how is my daughter? Kar ka boye min komai don girman Allah ka gaya min Dr, just tell me piss, is she alive?” Hawaye na sauka idonta tayi masa tambayar, Maheer da ya mike tsaye shi ma sai kallon Dr Khalil yake ganin expression din fuskarsa, Dr Khalil yayi kasa da murya amma hakan bai boye damuwarsa ba yace “Zata samu lafiya in sha Allah Mama, ki kwantar da hankalin ki” Dr Khalil ya Kalli Maheer da ya nufosa yace “Dr Maheer?” Maheer ya masa nodding, Dr Khalil yace “Mu je office Dr” Ammi ta fashe da wani sabon kuka ta rikosa tace “Ni ma zaka iya gaya min koma menene Dr, mu tafi office din” Tana fadin haka ta fara tafiya kamar tasan office din nasa, Dr Khalil ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya kalli Maheer dake tsaye gabansa yace
“How comes Maheer? Waye yayi mata haka?” Damuwa karara a fuskarsa yayi tambayar, Maheer yayi kasa da murya yace “Wani irin poison ne pls?
And how is she? Is she responding? can i see her?
PIss?” Zuciyar Maheer na bugawa yayi request din, Dr Khalil ya zauna kan kujera cause he was exhausted ya rike kansa, Maheer ya zauna kusa da shi don gaba daya hankalinsa ya gama tashi, Ammi kuwa tayi gaba ba tare da ta waigo ta ga ko Dr Khalil din na biye da 78…..
ita ba, Dr Khalil yace “Don Allah garin yaya wannan abu ya faru? Su waye da waye a gidan? Ko taje wani waje ne aka bata abincin?” Maheer yace “Yanzu baza a min alfarma in shiga in ganta ba?” Dr Khalil yace
“She is in a critical condition now, we’ve tried our best, her body is failing, she is on life support” Maheer yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Dr Khalil bai iya ya dago kansa ba har bayan kusan minti daya, a hankali yace “We are trying our very best, akwai manyan likitoci biyu ma from another hospital da suka ZO” Yana fadin haka ya mike ya bar wajen Maheer ya bi sa da kallo. Maheer bai taba shiga kalan tashin hankalin da ya shiga a lokacin ba, he felt like the world is coming to an end, ji yake kamar komai ya tsaya masa cak a duniyar, he wish mafarki yake, he wish shi ne ya ci abincin nan ba Mimi ba, yasan don shi aka yi poisoning abincin not Mimi, fita yayi daga reception din yana ganin building din na juya masa a kai ya jingina jikin bangon asibitin ya runtse ido zuciyarsa na bugawa da karfi, lokaci daya ya bude ido ya nufi outside of the hospital. Wajen karfe hudu Dr Khalil ya shiga ICU for the countless time, tun karfe uku likitocin ciki suka fita MD kadai ya rage a ciki, Dr Khalil na kallonsa don tun dazu yake tsaye a position din da yake, Dr Khalil ya karasa yayi kasa da murya yace “Kana bukatan ka huta MD, I will stay, go get some rest….” MD dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, Dr Khalil could see how confused and disappointed he is, ya juya a hankali yana kallon Mayraah dake kwance on life support feeling so 78…..
heartbroken, Sunkuyar da kai MD yayi a hankali yace
“I wish we could do more than this, i wish…” Sai kuma yayi shiru, Dr Khalil yace “It’s not our fault MD, we tried our best, kawai mu ci gaba da addu’a ba mu cire hope ba in sha Allah” Zaunawa MD yayi ya jinginar da kansa jikin wajen ya rufe ido. Karfe hudu na asuba Abba ya shigo asibitin hankali tashe after driving all the way from kano. Kallonsa kawai Ammi dake zaune reception take yi hawaye na sauka idonta, yanda taga rana haka taga daren nan tare da Bilkisu dake gefenta, Abba ya karasa hankali tashe yace
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, ina likitocin suke.. where is the Drs office, suyi transferring dinmu outside of the country kawai” Kuka kawai Ammi take kamar ranta zai fita ta kasa cewa komai, Abba ya nufi Nurse dake zaune reception din da sauri yace “I want to speak with any of the doctor in here pls” Nurse din ta zagayo tace “Ohk sir” Office din Dr Khalil ta tafi don ko minti biyu ba ayi ba ya tafi sama bayan ya fito ICU. Bayan Dr Khalil yaji bukatan Abba yayi kasa da murya yace “Sir our hospital is among the best here in Nigeria, kwararrun likitoci gare mu a nan, ko an fita da ita iyakar abinda muke yi a nan din za ayi mata, likitoci turawa biyu where among us today, so kawai addu’a za mu mata Allah ya tashi kafadunta, in sha Allah she will be fine….” Cikin rashin gamsuwa Abba yace “Na fi gane kuyi referring dinmu any best hospital in the world za mu je piss, ku min haka” Shiru Dr Khalil yayi yana kallonsa. ICU Dr Khalil ya samu MD ya sanar masa abinda Abba ke cewa, MD dake ta kallonsa yace Ceo tana hanya with 2 Dr’s
Tablet ya ciro a pack din hannunsa ya mika mata da goran ruwan, ta mike zaune da kyar tana yarfe hannu hawaye na sauka idonta ta amshi maganin da ruwa, ya ajiye sauran maganin sannan ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo, yana fita ta tura maganin karkashin carpet ta ajiye ruwan ta mike ta koma gefen gado ta zauna tana murmushi duk da yanda gabanta ke faduwa, alas gwara duk kowa ya rasa shi, da dai tayi witnessing ya auri Mayraah ko kuma wata mace a doron kasa bayan ita to gwara duk a rasa shi gaba daya, ta goge hawayen idonta tana murmushi. Maheer na komawa parlon ya zauna ya bude abincin da Mayraah ta ajiye masa, rufewa yayi ya koma ya kwanta don gaba daya bai jin appetite din cin abinci, throughout ranan haka ya yini da fever, yana ta kwance har bacci ya daukesa, Haseenah dai na gefen gado a dakinta har sannan ta ma kasa fitowa parlon, ta san wani lokacin sai ya bari abinci ya huce yake ci, tasan yanzun ma jira yake abincin ya huce kafin ya ci. Bude ido Maheer yayi ta dalilin wayarsa dake ring, ganin Mayraah ce ke kiransa ya daga a hankali yace “Mimi” Tace “Yaya ka sha maganin?” Yace “Zan sha” jin yanayin muryarsa da damuwa tace “To sai yaushe?” A hankali yace “Zan sha Mimi, am not too fine, ko zaki kawo min tea?” Ta sauka daga kan gado tace “To bari in kawo maka” Duk Haseenah na jin wayar da yake don kofar dakinta a bude yake, ta yi wani murmushi ta mike a hankali ta kulle kofar dakinta wato baya jin dadi alamar har ya ji a jikinsa yau ne ranarsa na karshe a duniya, tasan dai babu ta yanda Mayraah zata yi girki ko kadan ne ace bai ci ba, dole zai ci abincin, bayan kusan minti sha biyar Mayraah ta shigo parlon da sallama, ta ajiye shayin hannunta ta duba abincin ganin bai ci ba da damuwa ta koma gefensa ta zauna tana taɓa forehead dinsa, jin he is running temperature tace “Yaya ka ci abincin ko kadan ne sai in maka allura” Yace “Bari in fara shan shayin” Daga haka ya mike zaune, ta dau shayin ta mika masa ya amsa, kadan ya iya sha, tayi tayi da shi ya kara yace ya ishesa, ta ajiye shayin yace “Pls go to my bedroom zaki ga maganin da na sha dazu a bedside drawer ki dauko min” Tace “Wanne ne Bedroom din naka?” Ya nuna mata direction din ta mike ta tafi cikin dakin, ta dauko ledan maganin ta dawo parlon ta bude masa su ta basa ya sha ya koma ya kwanta, tana kallonsa tace “Dama baka da lafiya ne yaya?” Yace “I was feeling feverish tun da safe” Tace “Toh Allah ya sauwake, in zuba maka abincin ko kadan ne ka ci?” Ya girgiza mata kai yace “Bazan iya ci ba Mimi” Tayi shiru tana kallonsa, dama in har yana rashin lafiya komin kankantarsa baya iya cin abinci sai tea, a hankali tace “Toh shikenan bari in tafi da shi” Yace “Hope u are not angry?” Tayi murmushi tace “Aa yaya, ai nasan baza ka iya ci ba ko na bar sa nan, but plss ka kara shan shayin ko kadan ne” Ya mike ta dau shayin ta mika masa ya sha kusan rabi sannan ya ajiye ya kwanta yace “Thank you” Tace “Ko zaka shiga daki ka kwanta?” Yace “Aa nan nake kwanciya wani lokacin” Da damuwa tace “Kilan ma sauro ne ya cijeka ka samu malaria” Murmushi kawai yayi ya lumshe ido, tace “Anjima zan kira inji if u are better, in kuma baka ji sauki ba sai in sa driver ya kai ni pharmacy in siyo alluran da zan maka, yace “Ohk Mimi” Mikewa tayi ta dau abincin da cup din shayin ta fita ya bi ta da kallo sannan ya lumshe ido. Mayraah na komawa can cikin gida ta kai abincin kitchen, bayan ta wanke cup din da ya sha shayi, ta dau plate ta bude abincin ta debi shinkafa kadan ta sa miya, ko naman bata saka ba, ta bar sauran abincin a nan kitchen ta wuce sama zuwa dakinta, ajiye abincin tayi ta cire hijab dinta sannan ta dau wayarta zata jona a charge taga tana da miss call daya, dubawa tayi taga number da ya kirata dazu, mamaki ne ya cikata ta zauna gefen gado tana kallon number, to me yasa ya sake kiranta? Ko dai mistake yayi? Kawai a ranta ta sa mistake ne ma ba ita zai kira ba, kallon agogon wayar tayi taga karfe tara har da minti biyar, ta ajiye wayar gefenta sannan ta dau bowl din abincin da ta zuba ta dau cokalin ta fara cin abincin…. Cokali uku Mayraah tayi ta ajiye spoon din a hankali jin wani abu tun daga throat har zuwa cikinta, lokaci daya taji cikinta ya ƙulle, makogwaronta taji kamar ana yanka mata, ta fara jan numfashi da kyar tana zaro ido, ihu take son bude baki tayi amma ta kasa, hannunta na rawa ta jawo wayarta dake gefenta da last strength dinta ta iya danna call log dinta tayi sending call din number da hannunta ya taɓa, ko fitowa maganarta bai yi sosai ta dinga cewa zata mutu not knowing ko kiran ya shiga ko bai shiga ba, an daga ko ba a daga ba, mikewa MD yayi after hearing her almost inaudible voice kamar warce ake strangling tana cewa zata mutu, yace “Hello… Hello” amma kalmar da take ta maimaitawa kenan, Katse wayar yayi da sauri ya sake dialing amma har ya gama ringing ba a daga ba, ya sake kira no response, sau hudu yana kiran layin nata, zan mutu da ta dinga cewa ne kawai ke rotating a kansa, and she sounds as if they are strangling her, wannan yasa ya fara dialing number Dr Khalil da sauri, har ya gama ringing bai daga ba, Kallon agogo dake nuna karfe tara da minti sha biyar yayi, ya koma ya zauna yana kallon textbook din gabansa, kasa kwanciya hankalinsa yayi ya mike tsaye, in few minutes ya canza daga pajamas din jikinsa zuwa sweat pant with shirt, makullin motarsa ya dauka ya fita daga gidan, har bayan da mai gadi ya bude masa gate ya fita daga gidan kiran layin Mayraah yake but no response, ya sake kiran number Dr Khalil don yasan bazai rasa number kowa a gidan ba amma shi ma no response, though yasan yana asibiti suna operation as at that time, cikin minti sha biyar MD ya isa gidansu Mayraah after driving with speed, parking yayi kofar gida ya nufi gate din gidan sai a sannan ya fara tunanin me zai ce ya ma kai sa gidan, bai ko kalli fuskar security guy din da ya bude masa gate din ba zai shiga cikin gidan security din ya ki basa hanya yace wa yake nema, MD ya kallesa yace “Baka taɓa ganin motata kofar gidan bane?” Daga haka ya bi gefensa ya shiga ciki walking in a haste, Babban Chalet din building din ya fara kalla, sai kuma ya karasa main building din gidan, standing at the main entrance yayi knocking kofar, komawa baya yayi thinking if he isn’t going to look stupid? Bude kofar aka yi, mai aikin Ammi na kallonsa daga sama har kasa ta gaishesa da ladabi, sai da ya fara tunanin sunan Mayraah sannan yace “Mayraah… Ita za ki kira min” Da ladabi tace “Yallabai ai ta hau sama ta kwanta” Yace “Tafi saman ki kirata yanzu” Juyawa tayi ta bar wajen ta wuce sama, kwankwasa kofar dakin Mayraah tayi taji shiru, sai da ta kwankwasa ya kai sau biyar bata ji an amsa ba, hakan yasa ta juya ta sauka kasa don komawa tace masa bata bude mata kofar ba, Ammi ta fito daga bangarenta jin ana knocking kofa, bata ga kowa corridor din ba, kawai ta karasa dakin Mayraah don bata ga ta zo yi mata sai da safe ba gashi har goma ya kusa, murda kofar dakin tayi ta bude, ganinta kwance a kasa Ammi ta karasa cikin dakin tace “Meye haka kika kwanta kasa Mimi?” Wani ƙara Ammi ta kwala da karfi ba tare da ta san tayi hakan ba, lokaci daya ta zube gabanta ta fizgota ganinta kwance with foam coming out from her mouth, jijjigata ta dinga yi jikinta na rawa tana kiran sunanta, kawai ta saketa ta fito dakin da gudu ta kara kwala wani ƙaran, gaba daya tayi rikicewar da bata taɓa yi ba a rayuwarta, bilkisu dake kokarin gaya ma MD Mayraah bata bude kofar ba kilan tayi bacci, ta zaro ido jin ihun Ammi ta juya da sauri, tuni MD ya shiga parlon bayan shi ma ya ji ihun da Ammi ta kwala, har ya fara tafiya ganin girman gidan bai kuma san exactly inda zai bi ba, ya fixgo Bilkisu yace “Where is her room?” Bilkisu ta nuna masa hanyar stairs din gidan, ya nufi can da sauri yana danna emergency line dinsu na asibiti a wayarsa for Ambulance, cikin few seconds aka daga kiran, Bilkisu dai sai bin sa take a baya jiki na rawa don duk ta tsorata, har sannan Ammi bata daina ihun da take ba don she was soo shocked, daga karshe taji kamar an zare mata duk kuzarinta ta fara ganin jiri ta dafe karfen stairs din ta durkusa inda take tsaye tana maida numfashi, dai dai nan MD ya hauro saman Bilkisu da jikinta ke rawa na biye da shi da gudu, kallo daya yayi ma Ammi dake maida numfashi da kyar, kawai ya shige dakin da ya gani a bude, Bilkisu na leka dakin ita ma ta kwala kara ta koma baya tana zaro ido, Ammi na kallon Bilkisu bakinta na rawa tace “Maheer” Bilkisu na jin abinda Ammi tace ta sauka kasa a guje zuwa chalet. MD na shiga dakin ya jefar da wayarsa ya durkusa gaban Mayraah ya dagota da sauri, yana ganin yanayin da take da kuma abincin dake gefenta cikin second biyu yayi diagnosing hakan as poisoning, ganin she has no sign of pulse, ya saita kansa don da farko rikicewa yayi, ya kwantar da ita da sauri ya fara mata CPR a kirjinta with every of his strength dan bai san for how long pulse dinta ya tsaya ba, dai dai nan Maheer ya shigo dakin after running all the way from the chalet, zuciyarsa na bugawa ya karaso kusa da su ya durkusa ya dafe kansa yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” MD was doing all his possible best to revive her pulse…. Haseenah na makale jikin window taki fitowa sai zare ido take tun bayan da Bilkisu ta zo tana kuka ta kira Maheer, she doesn’t even know weda she should be happy or otherwise, duk da ba haka ta so ba, har kasan ranta tayi bakin ciki da ba Maheer bane ya ci abincin nan, amma Mayraan ma dai da ta ci Allah Ubangiji ya sa ta mutu kawai, addu’ar da ta dinga yi kenan feeling no epitome of remorse akan abinda ta aikata, tana cikin wannan tunanin taga Ambulance ya shigo gidan, duk iya leken da take bata ga wanda ya saka Mayraah a Ambulance din ba, amma tana ta jiyo kukan Ammi, sai kuma ta juya da sauri ta koma dakinta tana tunanin inda zata yi discarding kwalban poison din don tasan ko hauka take bazata saka a bola ba…. MD har zai shiga Ambulance din bayan paramedic da suke ciki sun saka ma Mayraah oxygen with Maheer by her side, sai kuma ya juya ya kalli Ammi dake biye da shi a gigice tana kuka kamar ranta zai fita ita ma tana kokarin shiga Ambulance din, speaking calmly yace “In sha Allah she will be fine, bazai yiwu ki shiga Ambulance ba…” Bai jira cewarta ba ya shiga Ambulance din suka bar gidan, Ammi na kara rusa kuka, Sai da Haseenah ta ji fitar Ambulance din ta fito compound a rikice ta nufo Ammi da gudu tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, me ke faruwa Ammi, na fara bacci naji kamar siren, meye ke faruwa?” Hankali tashe take tambayar tana zaro ido, Ammi ko kallonta bata yi ba ta bi bayan Ambulance da sauri ko takalmi babu, Haseenah ta koma gun Bilkisu da ke kuka tace “Wai me ke faruwa Bilkisu? Me ke faruwa a gidan nan” Cikin kuka Bilkisu tace “Wallahi Mayraah ce babu lafiya har kumfa na fitowa bakin ta” Haseenah ta dafe kirji tana gwalo ido tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, kuma ta mutu?” Bilkisu bata tsaya bata amsa ba ta shiga cikin gida da sauri don dauko ma Ammi takalmanta da Hijab ganin har ta fita gate, dama kuma har ta haddace sunan asibitin da ta gani jikin Ambulance din. Maheer na zaune babban reception din asibitin ya dafe kansa da yayi masa nauyi, lokaci lokaci yake dagowa ya kalli Ammi dake reception din ita ma tare da Bilkisu dake ta kokarin kwantar mata da hankali take bata hakuri amma kamar tana kara tunzurata don Ammi tayi kuka har taji ba dadi, gaba daya ta dawo bata da wani kuzari, sun kusa awa biyu reception din a zaune amma babu likitan da suka ga ya fito har sannan, wannan ya kara daga ma Ammi hankali sosai ba kadan ba, wajen karfe sha biyu da rabi Dr Hamid ya fara fitowa, Maheer ya mike da sauri yana kallonsa don yayi recognizing dinsa as one of the doctors that went inside the emergency room with Mayraah, karasawa yayi gun sa, Ammi ma ta mike da sauri ta nufesa gabanta na mugun faduwa, Dr Hamid na kallon Maheer yace “She is been transferred to ICU….” Yana fadin haka ya bar wajen, Maheer ya bi sa da kallo, Ammi ta fashe da matsanancin kuka ta riko Maheer tace “Maheer me hakan ke nufi? ICU naji fa yace” Maheer yayi kokarin calmly dinta yace “Dama za a kai ta can ai, saboda pulse dinta da ya dauke na wani lokaci, in sha Allah she will be fine Ammi” Karfin hali kawai shi ma yake yana kokarin kwantar mata da nata hankalin. Karfe biyu saura na dare Dr Khalil ya shigo reception din daga ICU, Ammi ta mike da sauri tana goge hawayen idonta ta nufesa don taga kamar kusan duk likitocin asibitin sai da suka shiga Emergency room din, muryarta na rawa ta kamo hannunsa tace “Plss tell me how is my daughter? Kar ka boye min komai don girman Allah ka gaya min Dr, just tell me plss, is she alive?” Hawaye na sauka idonta tayi masa tambayar, Maheer da ya mike tsaye shi ma sai kallon Dr Khalil yake ganin expression din fuskarsa, Dr Khalil yayi kasa da murya amma hakan bai boye damuwarsa ba yace “Zata samu lafiya in sha Allah Mama, ki kwantar da hankalin ki” Dr Khalil ya Kalli Maheer da ya nufosa yace “Dr Maheer?” Maheer ya masa nodding, Dr Khalil yace “Mu je office Dr” Ammi ta fashe da wani sabon kuka ta rikosa tace “Ni ma zaka iya gaya min koma menene Dr, mu tafi office din” Tana fadin haka ta fara tafiya kamar tasan office din nasa, Dr Khalil ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya kalli Maheer dake tsaye gabansa yace “How comes Maheer? Waye yayi mata haka?” Damuwa karara a fuskarsa yayi tambayar, Maheer yayi kasa da murya yace “Wani irin poison ne pls? And how is she? Is she responding? can i see her? Plss?” Zuciyar Maheer na bugawa yayi request din, Dr Khalil ya zauna kan kujera cause he was exhausted ya rike kansa, Maheer ya zauna kusa da shi don gaba daya hankalinsa ya gama tashi, Ammi kuwa tayi gaba ba tare da ta waigo ta ga ko Dr Khalil din na biye da ita ba, Dr Khalil yace “Don Allah garin yaya wannan abu ya faru? Su waye da waye a gidan? Ko taje wani waje ne aka bata abincin?” Maheer yace “Yanzu baza a min alfarma in shiga in ganta ba?” Dr Khalil yace “She is in a critical condition now, we’ve tried our best, her body is failing, she is on life support” Maheer yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Dr Khalil bai iya ya dago kansa ba har bayan kusan minti daya, a hankali yace “We are trying our very best, akwai manyan likitoci biyu ma from another hospital da suka zo” Yana fadin haka ya mike ya bar wajen Maheer ya bi sa da kallo. Maheer bai taɓa shiga kalan tashin hankalin da ya shiga a lokacin ba, he felt like the world is coming to an end, ji yake kamar komai ya tsaya masa cak a duniyar, he wish mafarki yake, he wish shi ne ya ci abincin nan ba Mimi ba, yasan don shi aka yi poisoning abincin not Mimi, fita yayi daga reception din yana ganin building din na juya masa a kai ya jingina jikin bangon asibitin ya runtse ido zuciyarsa na bugawa da karfi, lokaci daya ya bude ido ya nufi outside of the hospital. Wajen karfe hudu Dr Khalil ya shiga ICU for the countless time, tun karfe uku likitocin ciki suka fita MD kadai ya rage a ciki, Dr Khalil na kallonsa don tun dazu yake tsaye a position din da yake, Dr Khalil ya karasa yayi kasa da murya yace “Kana bukatan ka huta MD, I will stay, go get some rest….” MD dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, Dr Khalil could see how confused and disappointed he is, ya juya a hankali yana kallon Mayraah dake kwance on life support feeling so heartbroken, Sunkuyar da kai MD yayi a hankali yace “I wish we could do more than this, i wish…” Sai kuma yayi shiru, Dr Khalil yace “It’s not our fault MD, we tried our best, kawai mu ci gaba da addu’a ba mu cire hope ba in sha Allah” Zaunawa MD yayi ya jinginar da kansa jikin wajen ya rufe ido. Karfe hudu na asuba Abba ya shigo asibitin hankali tashe after driving all the way from kano. Kallonsa kawai Ammi dake zaune reception take yi hawaye na sauka idonta, yanda taga rana haka taga daren nan tare da Bilkisu dake gefenta, Abba ya karasa hankali tashe yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, ina likitocin suke.. where is the Drs office, suyi transferring dinmu outside of the country kawai” Kuka kawai Ammi take kamar ranta zai fita ta kasa cewa komai, Abba ya nufi Nurse dake zaune reception din da sauri yace “I want to speak with any of the doctor in here pls” Nurse din ta zagayo tace “Ohk sir” Office din Dr Khalil ta tafi don ko minti biyu ba ayi ba ya tafi sama bayan ya fito ICU. Bayan Dr Khalil yaji bukatan Abba yayi kasa da murya yace “Sir our hospital is among the best here in Nigeria, kwararrun likitoci gare mu a nan, ko an fita da ita iyakar abinda muke yi a nan din za ayi mata, likitoci turawa biyu where among us today, so kawai addu’a za mu mata Allah ya tashi kafadunta, in sha Allah she will be fine….” Cikin rashin gamsuwa Abba yace “Na fi gane kuyi referring dinmu any best hospital in the world za mu je plss, ku min haka” Shiru Dr Khalil yayi yana kallonsa. ICU Dr Khalil ya samu MD ya sanar masa abinda Abba ke cewa, MD dake ta kallonsa yace “Ceo tana hanya with 2 Dr’s”
Maheer ya dau wayarsa dake ta vibrate ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren Mama Ladi tace “Na shiga uku Mashir gani gaban asibitin cikin rana tun dazu, anya za su bari in shiga kuwa? naga masu gadin wasu gaddawa ba fara’a ba annurin musulunci a tattare da su, ko dai ba asibitin bane ɗan sahun ya ajiye ni” A hankali yace “Ki shigo za su bar ki” Mama Ladi ta zuge karamin Ghana must go dinta ta jefa wayar ciki sannan ta dau abunta ta rataya a kafada, bata sake kallon masu gadin ba ta nufi karamin gate zata shiga security din yace “Mama yau ba ranan kawo ziyara bane, sai gobe da yamma….” Mama Ladi ta tsaya tana kallonsa baki bude, can ta fashe da kuka tace “Dama asibiti wajen ziyara ne? daga karaye fa nake an ba jikata guba ta ci a abinci, in kawo ziyara asibiti sai kace wajen yawon bude ido in ba kaddara ba ma me zai kawo ni nan, tun karfe biyar fa na fito gida daga karaye” Komawa yayi ya zauna bai sake ce mata komai ba kuma bai bude gate ba, Mama Ladi ta ajiye Ghana must go dinta tace “Ikon Allah, To asibitin yan iska aka kawo Meran dama? Wallahi idan har ran jikata yayi halinsa bamu gana ba bazan yafe maka ba har karshen duniya” Ganin Security din bai sake kallon direction dinta ba kuma ya kulle gate, ta ciro wayarta ta sake kiran Maheer, bai daga ba kawai ya mike ya fita waje, after persuading the securities suka bar Mama Ladi ta shiga da Ghana must go dinta tana hararansu tace “Kattin banza kawai, ko me asibitin dai bazai ce kar in shiga ba balle ku masu gadi” Mama Ladi ta kalli Maheer cikin tashin hankali tace “Mashir garin yaya haka ya faru? Me ya kai guba sabon gidan har aka ci ni Ladiyo?” Shi dai bai ce mata komai ba yana tafiya yaje parking space ya bude mata Booth ta saka Ghana must go dinta suka shiga cikin asibitin, zaunawa tayi gefen Hajja ta rike kai ta fashe da kuka tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’una, mu kuma da bala’in da muka wayi gari da shi kenan a pamily yau, duk wata fitina da tashin hankali da abun kunya a pamilyn mu yake karewa, anya ba lefi muka tafka ma ubangijinmu bamu sani ba kuwa? Daga wannan sai wannan kamar masu shan jinin mutane, To ni dai na yanke shawaran yin azumin kwana uku in nema ma Pamilyn nan namu gafara ko za mu dinga ganin dai dai, don gaskiya ban yarda da wannan iftila’in dake fado mana ba kullum, to ita kuma ina taje ta samu guba ta ci kamar dai ana yunwa a sabon gidan, mu fa zamaninmu dabbobi ne ke cin guba garin ciye ciyensu a titi” Daga Aunty Mariya har Hajja babu wanda ya kalli Mama Ladi, Usman ya mike ya bar wajen gaba daya, Maheer dama ya tafi can gaban ICU ya zauna, Mama Ladi tace “Ai shikenan” Dr Khalil na tsaye office din MD dake zaune after taking his bath yana juya rabin cup din shayin gabansa da teaspoon, Dr Khalil na kallonsa yace “Idan ka sha shayin sai in maka allura don ka warware daga stress din nan so it won’t weigh you down” MD yace “No, just pain reliever” Juyawa Dr Khalil yayi ya bar gaban table din yace “Injection zai fi sir” Fita yayi daga office din ba a dau lokaci ba ya dawo rike da allura bayan ya hada masa har da na bacci amma dosage ba me yawa ba, bai yarda MD ya lura da kalan alluran ba yayi masa sannan ya fita daga office din. Da yamma Ceo na tsaye tare da Abba da Usman a bakin ICU with 3 Doctors dake bayanta, bayan ta gama yi ma Abba bayani a takaice a kan yanda suke bakin kokarin su, ta kuma kwantar masa da hankali giving him assurance, Abba da ko kadan yaji bai gamsu da bayaninta ba yace “I just want to know if she is responding, is there any improvement? shine kawai damuwata yanzu” Ceo ta sauke idonta tace “She will respond, sure she will, and they will be improvement soon… She is still being monitored for now” Daga haka ta juya zata bar wajen Abba yace “Ina son shiga in ganta, i want to see my daughter” Ceo ta juya ta kallesa tace “Ka bari idan Allah ya kai mu gobe sir, kaga ko 24 hours bai cika ba da kawo ta ai…” Shiru Abba yayi yana kallonta tashin hankali karara a fuskarsa, tuni ta bar wajen likitocin suka bi bayanta, Usman ya zauna a kujeran wajen looking so disordered, Abba na kallonsa yace “Pls Barrister ka kai su Mariya gida, sun yi yawa a asibitin and the staffs are complaining tunda ba visiting day bane” Usman na kallon Abba a hankali yace “But Abba why not a fita da ita waje? Won’t that be better?” Abba yace “Haka nima na so, amma kaga ceo din tasu ai daga waje ta zo da wasu likitocin….” Usman ya jinginar da kansa da bango ya rufe ido…. Maheer na zaune ward din da aka kwantar da Ammi, holding on to her hands yace “Ko minti sha biyar ban yi da fitowa daga can ba Ammi, she is getting better pls ki kwantar da hankalin ki” Ammi ta goge hawayen idonta tace “Toh ni me yasa baza su bar ni in shiga in ganta ba?” Maheer ya kwantar da murya yace “Drip ne fa a hannunki Ammi” Ammi tace “To a cire min mana idan na dawo sai a mayar” Maheer yace “Jininki bai sauka ba har yanzu, ki bari idan ruwan ya kare za ki shiga ki ganta, i promise u she is getting better Ammi” Ammi dai kallonsa kawai take hawaye na sauka idonta, duk da shi ma mugun karfin hali yake mata pretending Mayraah is getting better, ya sauke idonsa yace “Bari in je in amso abinci a gida, Aunty Mariya ta gama” Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga ward din, bayan ya kulle kofar ya jingina da bango ya rufe ido, bayan kusan minti biyu ya bar wajen yana tafiya a hankali, ICU ya koma kamar yanda yace ma Ammi 20 mins ago he was allowed inside amma still no progression as at then, Usman na zaune gaban IC unit din, Maheer ya zauna gefensa yana kallonsa yace “Ka shiga?” Usman ya ta gyada masa kai, shiru Maheer yayi bai sake cewa komai ba, bayan kusan minti goma Dr Khalil ya fito daga Unit din, yana kallonsu calmly yace “In sha Allah muna sa ran za a samu advancement nan ba da dadewa ba, her system is gradually trying to respond” Maheer ya mike da sauri yace “Did she make any movement Dr?” Dr Khalil ya girgiza kai yace “Not yet, but muna sa rai” Maheer yace “Pls can i go in?” Dr Khalil ya dan masa murmushi yace “Ceo dinmu tana ciki ka bari sai ta fita” Maheer ya koma a hankali ya zauna yace “Ohk nagode” Juyawa Dr Khalil yayi ya bar wajen, dai dai second floor ya hadu da MD that was coming down the stairs as if counting each and every step he is making, he was walking very slowly, tun da Dr Khalil yayi masa allura sai yanzu karfe shidda saura ya tashi, yana ganin Dr Khalil ya tsaya, amma sai ya kasa ce masa komai as if he was expecting a news that might ruin him in seconds, kallon Dr Khalil kawai yake babu kiftawa, Dr Khalil ya nufesa yace “How are you feeling Sir?” Wani boyayyen ajiyar zuciya ya sauke, Dr Khalil ya kai hannu forehead dinsa wanting to feel his temperature, MD ya kauda kansa yana masa wani kallo yace “Na ce maka ka min alluran bacci Khalil? Me yasa zaka min alluran bacci?” Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace “Kai da kayi baccin yanzu baka samu relieve ba Sir?” MD bai ce masa komai ba ya ci gaba da tafiyarsa zai sauka downstairs, Dr Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi don yasan in da zai je, da sauri MD ya juyo, Dr Khalil yayi keeping straight face yana kallonsa, MD ya dawo sai kuma ya fasa masa tambayar da zai masa kawai ya juya ya sauka kasa, Dr Khalil ya san tambayarsa zai yi ko akwai progression but probably bai son ya ji otherwise shi yasa ya gwammace ya je da kansa, MD na sauka downstairs ya nufi ICU ba tare da ya ma san Nurses dake reception suna gaishesa ba balle ya amsa, Maheer ne kadai zaune gaban ICU din idonsa a lumshe, Usman ya tafi gida dauko ma Ammi abinci don Maheer yace masa bazai iya driving din ba, MD ya wuce sa ya shiga cikin Unit din, Wata registered nurse ce kadai zaune at the far end of the Unit tana monitoring Machines din, Tana ganin MD ta mike ta gaishesa da ladabi, shi dai idonsa na kan Mayraah baya ko kiftawa, nurse din ta koma ta zauna, bayan few seconds ya juya ya kalleta yace “You can leave” Mikewa tayi tace “Ohk sir” Daga haka ta fita daga Unit din, walking slowly ya karasa kusa da gadon…. Dukawa yayi looking at her face ya kamo hannunta a hankali giving it a gentle Massage, murya can kasa yace “Mayraah… Can you hear me? I know u can….” Though he wasn’t expecting an answer, amma haka ya ci gaba da kiran sunanta in a very low voice without stopping, Kamar me rada yace “Hello! sleeping Beau…” Sai kuma yayi shiru bai karasa ba ya sauke idonsa daga kallonta yana ci gaba da murza palm dinta gently, bayan minti biyar ya daga idanuwansa ya kalleta, a hankali yaga ta juya kai, ya mike tsaye da sauri yana kallonta, sake kiran sunanta yayi this time around bata yi making any movement ba, within few seconds yayi placing mata pulse oximeter probe a finger da sauri yana kallon Machine din, dai dai nan Ceo ta shigo Unit din, Ya mike tsaye yana kallonta, Ceo ta karaso kusa da gadon tana kallon Mayraah tace “Akwai advancement Aliyu?” MD ya gyada kai da sauri yace “She just moved her head now, shine nake duba oxygen saturation level….” Ceo ta ɗan yi murmushi tace “Glory be to God, this is what we’ve been waiting for, ka je office dina ka sanar ma Dr George….” MD yace “Ohk Ma’am” Juyawa yayi da sauri ya fita daga Unit din, Ceo ta dinga kallon Mayraah babu ko kiftawa, bayan few seconds ta sauke ajiyar zuciya ta juya ta kalli kofar ICU din sannan ta karasa kusa da ita ta kamo hannunta a hankali tace “Mary Ann, can you hear me?” Pecking hannunta dake ta kamshin turaren MD tayi tace “Quickest recovery dear” MD na fitowa Unit din Maheer ya mike yana kallonsa yace “Doctor is there any progress now? Zuwa yanzu ya kamata a samu wani progress” MD na kallonsa yace “Sure there is, in sha Allah” Daga haka ya bar wajen Maheer ya bi sa da kallo. Ceo na tsaye kan Mayraah har MD ya dawo tare da Dr George, sannan ta juya ta fita daga Unit din. Bayan isha Dr George yayi decreasing degree na ventilator support din so as she won’t be depending fully on the machine, MD da Dr Khalil dai na tsaye suna kallon baturen, har ya gama ya fita after checking her for the last time, Dr Khalil ya kalli MD yace “Kai baka jin yunwa ne tun jiya bawan Allah?” MD ya shafa kansa a hankali yace “I took tea da safe ko ka manta” Bai jira cewar Dr Khalil ba ya karasa kusa da Mayraah yana kallonta, can ya juya ya kalli Dr Khalil dake kallonsu, yace “I think da safe relatives dinta can come in one at a time to check on her…” Dr Khalil ya gyada kai yace “Haka ne, Allah ya kai mu goben, Allah kuma yasa kafin goben improvement din yafi haka….” Daga haka ya juya ya fita, MD ya bi sa da kallo, a hankali ya juya ya kalleta, sai kuma ya duka ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace “Can you hear me Mayraah?” A hankali ta bude lumsassun idonta, he was astonished seeing her open her eyes, Bai san sanda yayi mata murmushi ba, murya can kasa yana massaging hannunta yace “You will get well sooner, you are already doing great, be strong….” Rufe ido ta sake yi, tun kafin magrib ta ke making different movement of discomfort as a result of the breathing tube and that’s a very good sign of recovering slowly, amma duk bata bude ido ba sai a yanzu, murza hannunta ya sake yi therapeutically, ta bude ido a hankali, yayi kasa da murya yace “Can you hear me….” Kallonsa kawai take looking so pale and weak, ya sauke idonsa daga kallonta, bai sake ce mata komai ba ya mike ya nufi kofa, har a sannan Maheer na zaune bakin ICU, MD na kallonsa yace “You can check on her, speak to her” Mikewa Maheer yayi yace “Thank you Dr” MD ya bar wajen, Maheer ya shiga unit din, yana isa bakin gadon ya duka ya kamo hannunta a hankali yace “Mimi…” Bude ido tayi, Maheer couldn’t believe that, ya kalli Ventilator Machine din da sauri ya ga an ma rage karfinsa, ya matsa dab da ita yace “Get well pls Mimi, we all miss you, i know you to be a strong baby gal, stay calm and relax… You will get better very soon, we love you Mimi” sweet words haka is also a sedative therapy dake improving mental and psychological well being na patient in ICU, it really helps patient to be relaxed and comforted, bin sa kawai Mayraah take da ido, yana massaging mata hannu gently yana kallonta giving her a warm smile yace “Be strong for me, ur Ammi, Abba and barrister…” Lumshe ido tayi, ya sauke ajiyar zuciya feeling so much relieve now. Karfe tara Usman ya shigo IC unit din tare da Dr Khalil, Dr Khalil na kallonsa yace “Speak calmly to her” daga haka ya juya ya fita, nurse daya ce zaune tana monitoring din Mayraah, Usman ya karasa kusa da gadon, idonta na lumshe, ya zauna kan kujeran dake kusa yana kallonta, kasa ce mata komai yayi ya sunkuyar da kansa, bayan few seconds ya riko hannunta ta bude ido, still bai iya yace mata komai ba yana rike da hannunta for almost 10 mins, sake dago kai yayi ya kalleta, yayi pecking hannunta ya lumshe ido da kyar ya iya cewa “Come back soon Mimi” Daga haka ya mike ya fita waje. Sha daya saura Dr Hamid ya shigo Unit din, da mamaki yake kallon nurse din dake kokarin canza ma Mayraah hospital gown dinta da blanket yace “Madam sau nawa za a canza gown din nan ne?” Nurse din zata basa amsa sai ga MD ya shigo, Dr Hamid ya duba abinda zai duba sannan ya juya ya fita, MD ya kalli nurse din yace “What are you waiting for?” Nurse din tace “Dr Hamid just came in to check on her, yanzu zan canza” Juyawa MD yayi ya fita. Washegari da safe Abba ya shiga ICU din tare da Maheer, sosai hankalin Abba ya kwanta ganin state din Mayraah, don yanzun ma ta bude ido duk tana kallonsu, Maheer dai ya duka gabanta yana rike da hannunta yayi mata murmushi yayi kasa da murya yace “Good morning Mimi” Kallonsa kawai take, mintinsu sha biyar suka fita, Abba ba kallon Maheer yace “To yaushe za su yi disconnecting abubuwan nan da suka sa mata?” Maheer yace “Ana jiran aga ko zata iya numfashi da kanta babu matsala sai a cire in sha Allah, nasan zuwa anjima kilan a cire tunda an rage karfin machine din sosai” Abba yace “Toh Alhamdulillah, mun gode ma Allah, nayi farin ciki da abinda wannan asibitin suka mana na nuna concern dinsu, ko nawa suka bukata a biya nasan they deserve it” Maheer yayi kasa da murya yace “Ammi zata iya shiga ta dubata ita ma?” Abba yace “A dai bari a cire abubuwan nan da aka sa mata tukunna” Maheer yace “Haka ne” Ceo ce ta shigo asibitin leaving her securities outside, MD da ya fita dauko mata laptop dinta da wasu abubuwa yana biye da ita a baya, tana ganin Abba maimakon ta wuce sama sai ta tsaya suka gaisa tace “Ka shiga ka dubata ko Alhaji….” Abba yace “Eh bamu dade da fitowa ba, na kuma ji dadin yanda muka sameta, jiki kam Alhamdulillah” Ceo tayi murmushi tace “Mun gode Allah” Daga haka ta wuce sama MD na biye da ita har zuwa office dinta, ya bude mata ta shiga sannan shi ma ya shiga ya kulle kofar ya kunna AC, ajiye handbag dinta tayi ta zauna tace “I left early yesterday, wani family issue ne ya taso shi ne naje nayi intervening, tun daga gidansu nayi niyyar kiran ka in baka samples din nan….” Tana fadin haka ta warware karamin towel din hannunta ta ajiye kananun bottles biyu dauke da blood samples kan table dinta, sai kananun ziploc nylon biyu each dauke da strand of hair tace “I need genetic testings on this, commence it immediately” MD ya dauka yace “Ohk Ma’am” zai fita tace “Yauwa ya jikin Mary Ann? Zuwa yaushe za ayi disconnecting dinta daga Machine din?” Da ladabi yace “Har yanzu numfashin isn’t steady so we are still watching over it” Ceo ta sauke ajiyar zuciya tace “Idan na sha coffee zan sauko in duba ta yanzu” Yace “Ok Ma’am” Daga haka ya juya ya fita, duk da Abba bai so Ammi ta ga Mayraah ba sai an cire mata Ventilator Machine, amma saboda yanda ta mugun daga hankali haka likitocin suka saka a barta ta shiga kawai ta ganta, ai ko ranan kwana Ammi tayi kuka har da karin drip, don ita yanda taga an jojona mata wayoyi a jiki duk da idonta biyu tana kallon kowa gani take kamar fa babu sauki kwata kwata, in da sauki ai baza a makala mata wayoyi ba, haka nan aka ci gaba da kula da Mayraah a asibitin, a duk sanda Maheer ko Usman or Abba wani zai shiga wajen ta ya ganta babu hinderance, tunda Incident din nan ya faru MD ke zaman asibiti 24/7 don dama Bedroom babba garesa a office dinsa, Surkar Dr Khalil da inna da ita kanta Zainab duk sun zo asibitin duba Mayraah, duk da basu shiga ICU ba iyakarsu wajen Ammi. Aunty Mariya na kitchen yau ma kamar kullum tana dafa abincin da za a kai ma Ammi asibiti, kwanansu na shidda kenan a Abuja amma Abba yace ba sai sun je asibitin ba tukunna, hakan na damun Aunty Mariya amma bata masa musu ba duk suna gida sai dai tayi girki ita da Bilkisu Usman ko Maheer ya zo ya dauka ya kai asibiti, Mama Ladi ce ta shigo kitchen din tana yafa gyale tace “Sai na dawo Mariya” Aunty Mariya na kallonta tace “Ina kuma zaki Mama?” A fusace Mama Ladi tace “Ina kuwa zan je banda asibiti? Ko a kasashen waje ban taɓa jin inda aka ce baza a shiga asibiti a duba marasa lafiya ba in ba a tsinannen asibitin can ba, in haka ne meye amfanin zuwana? yau fa kusan kwana shidda mun tare a katon gidan nan sai dai mu ci abinci mu kwanta kamar wasu mayunwata” Aunty Mariya tace “Amma dai Alhajin da kansa yace ba sai mun je ba ka’idar asibitin kenan ko, kuma dazu da muka yi magana da shi yace ko zuwa jibi sai mu je” Mama Ladi tace “Amma ai katuwar matarsa Amina ita dai taje kuma an bar ta har ta shiga, tun da har nan ta zo ta mana jaje, naga ma ta kara narka wani uban kiba matar, kuma kwanan ta uku a garin nan yau, Shi kansa Umar da ya dawo shekaranjiya yayi sintirin zuwa asibitin ya fi a kirga kuma duk ana barin sa ya shiga, to sai mu ne za a raina ma wayo ace baza mu je asibiti ba? Ko dai wari muke ne?” Hajja dai ta tabe baki don ita ma hakan sam bai mata ba, to meye amfanin zuwan su Abujan kenan har yau basu ga marasu lafiyan ba, Mama Ladi tace “Ko ya zata cin abinci ya kawo mu Habujan, ni wallahi ban da yanda Hajja ta kirani tana kuka, da nayi ma kaina alkawarin ko gwal ake rabawa gidan Mamuda bazan sake tako kafata ba, don ba shi da mutunci mutumin, amma wannan ya zama dole ne kawai babu yanda na iya, don haka kin ga tafiyata asibitin idan kuwa ba haka ba idan zuciya ta debeni wallahi sai in dau jakata in koma karaye, iyaka duk wanda ya mutu in bugo waya ince Allah ya ji kansa ya gafarta masa” Tana kai wa nan ta fice daga parlon tana sakale da wani jaka a hammata, Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace “Ae gaskiya ne Mariya, mu muna nan sai dai ayi ta ce mana jiki da sauki an ki barinmu muje mu duba su, a ina aka taba haka?” Aunty Mariya dai bata ce komai ba ta ci gaba da girkinta a ranta kuwa tasan Abba gudun su bar abun fade a asibitin yake ne, barin ma Mama Ladi… Mayraah na kwance bayan an maida ta ward jiya, sai da tayi kwana biyar da Ventilator Machine kafin aka cire, kuma duk da haka wani lokacin sai taji numfashin ta na mata gardama, gaba daya ta rame sosai, sai haske da ta kara ba kadan ba, har a sannan she is having difficulty in saying anything sai dai tayi ta bin mutane da ido, kana ganinta kasan tana jin jiki, Ammi na zaune gefenta tana rike da hannunta trying to comfort her kamar yanda take yi tun da suka fito ICU, wani lokacin kuma Usman ne ke zama by her side, Maheer dai sai dai ya tsaya jikin window yana kallonta, yana jin kamar ya maida pains dinta gaba daya jikinsa ta samu relieve, ganin tana son mikewa zaune Ammi ta zaunar da ita tana mata sannu cike da damuwa, da kyar Mayraah ta bude baki a karo na farko tun da suka fito ICU tana kokarin yi ma Ammi magana, Ammi ta kasa kunne don jin abinda take cewa, Maheer ya karaso kusa da su, Ammi ta kallesa bayan ta fahimci abinda Mayraah ke cewa, dukawa yayi yace “What did she want Ammi?” Kasa cewa komai Ammi tayi, ta kara kallon Mayraah dake sauke numfashi a hankali, Maheer yace “Pls me tace Ammi?” Ammi dai tayi shiru.
Maheer ya karasa kusa da su ya duka yana kallon Mayraah ya kwantar da murya yace “Me kike so Mimi?” Shiru Mayraah tayi tana kallonsa tana sauke numfashi a hankali, Mikewa Ammi tayi ta bar wajen ta koma jikin window ta tsaya tana kallonsu, gaba daya damuwa yasa ita ma duk ta rame ba kadan ba don ko abincin kirki bata iya ci ganin halin da Mayraah take ciki, jin Mayraah tayi shiru Maheer ya rike hannunta yace “Talk to me Mimi, what is it? Me kike so?” Hawaye na sauka idonta cikin rawan murya tace
“Yaya i just…. want to ask Musharraf for forgiveness, kilan mutuwa zan yi wallahi…” sai da Maheer ya sa kunne sosai sannan yaji abinda take cewa, ya dinga kallonta ya ma kasa cewa komai, da damuwa ya girgiza kai yace “No Mimi, baza ki mutu ba, ki daina kira ma kanki mutuwa pls, you will heal completely nan ba da dadewa ba in sha Allah, i know u are strong” Ta daura kanta a shoulder dinsa tana kuka a hankali tace “I am always finding it difficult to breathe, I can’t do anything my self, my body is getting weaker everyday, bana iya tsayawa da kaina… ina jin kamar mutuwa zan yi, ina son kowa ya yafe min…” Nan da nan hawaye ya cika idon Ammi tana kallonsu daga inda take tsaye, Maheer dai ya kasa cewa komai yana rungume da ita maganganunta na yawo a kansa, bata san he is just acting strong because of her ba, don a yanda yake ji kullum da yanzu an kwantar da shi shima amma bai bari abinda yake ji yayi weighing dinsa down ba cause he wants to be by her side always, kuka kawai Mayraah take 81…..
tana jin kirjinta ya mata nauyi, shi kam he was trying all possible means to control him self yana patting bayanta a hankali, after many seconds da kyar ya dake yace “Za ki samu sauki Mimi, in sha Allah…” Ta girgiza kai da kyar tace “Amma ina son in masa magana pis Yaya, even Hamidah” Maheer bai sake cewa komai ba, ya kasa ci gaba da sauraronta yayi karfin halin kwantar da ita ya mike ya fita daga ward din, Ammi dai sai kallon Mayraah take ta kasa karasawa kusa da ita, ji take ina ma zata iya dauke duk wani ciwo da take ji a jikinta, hawaye ya kasa tsaya mata, tasan duk za su cinye wannan jarabawar ma kamar yanda suka cinye na baya, Bude kofar ward din aka yi MD ya shigo da sallama, ya kalli Ammi dake share idonta, ya kalli Mayraah dake kuka ita ma saman gadon, yayi kasa da murya yana kallon Ammi yace “Ma’am za mu dan yi magana a waje” Ba musu Ammi ta bi sa tana share hawayen da yaki daina zuba idonta, suna fita waje MD na kallonta da damuwa yace “Kukan nan da kike a ko da yaushe isn’t helping her, you need to be strong, she will recover fully in sha Allah nan ba da dadewa ba” Ammi ta fashe da kuka tace “Dr dole inyi kuka, ko da yaushe sai tayi ta ce mana zata mutu, ta yaya hankalina zai kwanta, wallahi she is all i got, ita kadae ce macen da Allah ya bani” Tana kai wa nan ta kara fashewa da kuka sosai, MD ya jingina jikin bango yana kallonta bai iya yace komai ba, bayan few seconds a hankali yace “Bazata mutu ba in sha Allah, she will heal completely, i know it’s not going to be easy, she is experiencing all this 81…..
RA
because she stayed too long in ICU, gradually jikinta zai dawo dai dai in sha Allah…. Abinda ya kamata yanzu idan akwai ko aunt dinta sai ta dawo nan ke ki koma gida, you need rest too, kema ba lafiya gare ki ba” Da sauri Ammi tace “Aa zan iya, i will be with my daughter” MD ya dan yi shiru, sai kuma yace “Toh shikenan, let me speak with her now….” A hankali Ammi tace “Toh” Kujeran dake corridor din ta tafi ta zauna tayi tagumi, shi kuma ya shiga ward din ya kulle kofar, karasawa yayi gaban gadon yana kallonta, ta sauke idonta daga kallonsa tana sauke numfashi a hankali, ya dafa gadon cikin kwantar da murya yace
“Akwai inda yake maki ciwo ne bayan chest dinki da kuma weakness da kike ji?” Girgiza kai tayi ba tare da ta kallesa ba, yayi kasa da murya yace “To ina za ki mutu ki je?” Sai a sannan ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, Ya sauke idonsa yace “Yea, mutum baya mutuwa sai lokacinsa yayi, tun da baki mutu a ICU ba, a nan ma in sha Allah baza ki mutu ba, you won’t die until ur creator is pleased with your soul, you are going no where in sha Allah, think about ur parent, brothers, relatives, friends, And…” Shiru yayi, ita dal kallonsa take, ya mike a hankali yace “And ur new pesky….” ita dai share hawayen dake makale idonta kawai take, yayi kasa da murya yace “You will get married, make babies… And fulfill all ur beautiful dreams in sha Allah” Ta daga kai ta kallesa, sunkuyar da kai yayi ya juya ya fita daga ward din, Ammi na ganin ya fito ta mike, ya karasa kusa da ita yace “Pls Ma’am ki rage kukan da kike a gabanta, always say
81…..
encouraging words to her, it will really help” a hankali Ammi tace “Toh Doctor Nagode” Ya dan yi murmushi ya juya ya bar wajen, Ammi ta shiga ward din. Da yammacin ranan wajen karfe biyar Mayraah na zaune Usman dake gefenta yana bata shayin dake cikin cup din hannunsa, Ammi na zaune kan kujera tana azkar dinta, Umar da Mama Ladi suka shigo ward din, Mama Ladi ta cire gyalenta ta jefar kan kujera ta karasa kusa da Mayraah da sauri tana kallonta tace
“Sannu Mera, wallahi yau satina daya a garin nan an ki bari in zo in duba halin da kike ciki yanzun ma zagawa nayi na biyo Umar babu wanda ya sani” Tana kai wa nan ta fashe da kuka ta rike kai tace “Allah ya isa tsakaninmu da Sanisa, Allah ya saka mana cikin gaggawa, Allah yayi mata abinda tayi mana, kuma naji dadi da Mashir yayi dubaran mikata hannun hukuma bakinsa alekum, da wa’e ne kilan kasheta da duka zai yi kinga sai laifin ya koma kansa dumu-dumu” Ita dai Mayraah bata dago kanta ba don hayaniyar Mama Ladi har cikin brain dinta take jin sa, yanzu gaba daya bata son hayaniya ko wani iri ne nan da nan sai kanta ya fara mata matsanancin ciwo ta fara ganin jiri, Ammi ta mike tana son ce mata ta rage murya amma ta rasa ta yanda zata fara gaya mata hakan, Umar dai tun da suka shigo da ita ya tafi far end of the ward ya zauna yana kallonta don tada masa bala’i tayi sai ya kawo ta, ko su Aunty Mariya basu san ya taho da ita ba,
Usman na kallon Mayraah da taki amsan shayin yace
“Ya isheki?” Ta gyada masa kai, ya ajiye sauran shayin ya gyara mata pillow din bayanta ta kwanta, can dai ya kalli Mama Ladi da taki yin shiru ga kukan da ta cika kunnensu da shi yace “Don Allah Mama ki yi kasa da muryarki asibiti ne nan akwai marasa lafiya, shi yasa ba a barin mutane su shigo anyhow” Ta juya da sauri tayi facing dinsa ta wani tsuke fuska kafin tace komai aka bude kofar ward din, Maheer ne ya shigo da sallama duk suka juya suna kallonsa har ya karaso ciki, da mamaki Ammi ke kallon warce ke bayansa da hijab dinta har kasa, Mama Ladi har da kifta ido don ita ma ta tabbatar da warce take gani a bayansa,
Mayraah ma ta dinga kallonta har ta karaso cikin ward din, gun Ammi ta fara zuwa kanta a kasa ta gaisheta a hankali, Ammi ta amsa tana kallonta, daga haka ta karasa kusa da gadon ta kalli Usman tace “Ina yini Yaya” Yace “Lafiya lau” ta maida dubanta kan Mayraah, Mayraah ta sunkuyar da kanta, a hankali tace “Ya jikin Mayraah?” Mayraah ta gyada mata kai kawai, Mama Ladi da abun duniya ya isheta ta ja Kujera ta zauna tace “To yanzu fisabilillahi ke kuma uban wa ya maki kwatancen nan? Salon a ganki cikinmu a gano baki da aure mu bar abun fadi a asibitin nan ayi ta nuna mu da hanci in muka zo wucewa, me yasa baki yi zamanki a inda kike Badiyya, yanzu domin Allah meye amfanin zuwanki nan ki bar mana abun fade” Badiyyah dai kallon Mama Ladi kawai take bata ko kiftawa, Mama Ladi ta kyabe baki tace “Ni yanzu ban ma san yanda zan bi in fita asibitin nan ba gashi ban sa Shijabi ba, tunda nasan duk yan asibitin sun san nan dakin kika shigo, wannan ai sai ayl tunanin kema pamilynmu ce bayan ba haka ba” 81…..
Badiyyah da har hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kai, a hankali ta fashe da kuka ta durkusa gaban Mayraah tana kallonta cikin kuka tace “Nasan ni ce silan duk wani abu da ya sameki saboda son zuciya na, i wish i never did all what i did to you Mayraah, nasan ban yi deserving yafiyarki ba kuma bazan ce ki yafe min ba, amma ina maki fatan Allah ya baki lafiya, Allah ya ci gaba da daukaka ki a rayuwar ki, i wholeheartedly regret all what I did Mayraah, nayi ruining happiness dinki for my selfish interest…”
Mayraah dai kanta na kasa hawaye na sauka idonta, Mama Ladi ta fashe da matsanancin kuka tace
“Wayyoo Allahnaa, wayyoo” Badiyyah dake kuka sosai ta mike da sauri ta fita daga ward din, sai a sannan Mayraah ta daga kai hawaye na sauka idonta, Ammi dai ta rike kanta daga inda take zaune, a hankali Mayraah ta jinginar da kanta jikin kafadar Usman dake gefenta tana kuka a hankali, shi dai idonsa na kofar ward din baya ko kiftawa, jin yanda take kuka ya juya ya kalleta, sauke idonsa yayi ya mata side hug trying to comfort her without saying anything, da sauri ta fada jikinsa tana kuka sosai, Maheer ya sauke idonsa ya juya ya fita daga ward din yana jin kukan nata har cikin ransa….. Dr Hamid ne ya shigo ward din, yana kallonsu yace “Plss plss bata bukatar duk wannan hayaniyar a kanta duba da condition dinta, mutum daya ya isa ya zauna tare da ita ba sai an cika daki haka ba, ka’idar asibitin nan kenan kuma lokacin visting ya wuce tun dazu” Mama Ladi ta share hawayenta tana kallonsa tace “Amma 81…..
RA
dai asibitin yan iska ne asibitin nan, yau naga bala’i da neman fitina, ta yaya za a dinga mana walakanci ana hantaran mu kamar wasu en banza, ko basu san waye Mamudan bane a garin nan, ba fa a banza muke ba don ka ganmu bama cikin hayyacinmu mun yi wujiga wujiga sbda tashin hankali, wallahi ba yan banza bane, meye haka kamar in an mutu a nan din aljanna za aje? Ni tunda uwata ta haifeni ban taba jin wannan ka’ida ba sai a shegen asibitin nan, yau kwanana takwas a garin nan anki bari in shigo nan ana ta mana iya shege, na samu da kyar an kawo ni yau kuma kace daga ina na fito? To wallahi ka fita idona in rufe” Dr Hamid dake ta kallonta ya juya ya fita, tuni Ammi ta mike ta kasa tsaye ta kasa zaune taji kamar ta nutse wajen don kunya, Usman dama kauda kai yayi, Mama Ladi ta ja tsaki tana huci tace “Yau ga figaggen likita kawai zai kawo min filili, ko dai asibitin na ubansa ne ne” Dr Hamid na fita office din MD ya tafi, bakin office dinsa ya samesa ya fito kenan, MD yace “Pls karfe nawa ne injection din nata?” Dr Hamid yace “MD pls talk to her family su bar yarinyar nan ta yi recovering yanda ya kamata kar su yi traumatizing kwakwalwarta, me yasa ma security za su dinga barin suna shigowa haka, ina ce tun karfe uku aka gama visting, noise din wata tsohuwa naji har corridor fa kamar ana cin kasuwa, what if Ceo ta shigo yau…”
MD dake ta kallonsa yace “I will talk to the mother, no more visitation till she recovers completely, Ceo din ma na hanya yanzu haka….” Dr Hamid yace “Gaskiya hakan zai fi Sir, talk to the mother” Daga haka ya juya 81…..
RA
ya bar wajen, MD ya sauka downstairs zai je duba wani patient da suka yi ma aiki dazu da safe kafin ya je ya samu Ammi a ward din da Mayraan take, tun daga nesa yake kallonsa babu ko kiftawa kamar yanda shi ma yake kallonsa har ya karaso cikin reception din, ya cire face cap dinsa zai wucesa without looking at him yace “Good evening” MD ya bi sa da kallo yace “Daga ina kake?” Bai tsaya ba yana ci gaba da tafiya yace “Kano” MD ya bude ido sosai ganin matar da ta shigo Reception din, ya karasa wajenta da sauri, cike da mamaki yace “Mami, daga ina ku ke haka?” Mami na kallonsa daga sama har kasa tace “Daddy you told me u are in Adamawa da na kira ka dazu….” Yana shafa kansa yace “Eh na dawo ne Mami, me ku ke yi a nan?”
💖💖 MAYRAAH 💖💖
83
Mami ta sauke ajiyar zuciya tace “Dubiya muka zo Daddy, i was surprise da naji asibitin nan ne ma, shi yasa na kira ka dazu nake tambayar ko kana Abuja kace kaje Adamawa” MD ya shafa kansa yace “Mu je office ki sha ruwa Mami” Mami dake kallon Musharraf da ya zauna reception yana dialing number Maheer tace “Aa bari mu fara duba ta tukunna Daddy” MD yace “Ohk wani ward number suka ce maku suke?” Mami tace “Shi zai kira yayan nata mu ji, da kyar ma aka bari muka shigo wai visting sai nan da kwana biyu, sai da Musharraf yace masu za mu ga likita ne sannan suka bari, ya kira wayar ka kuma baka daga ba” MD ya ɗan kalli Musharraf Yace “Ohh wayar na office ne Mami, ashe dai yana da numberta har yanzu” Mami tace “Wani irin magana ne wannan Daddy” MD yace “To yaushe rabon da ya kirani? Duk ya kullaceni tun akan aurensa da aka fasa kamar ni na hana auren, me ya hanasa fara bincike kafin ya nemi yarinyar? Kinga we are not to be blamed ai” Mami tace “Kaga ba a nan ya kamata mu yi wannan maganar ba, kuma koma dai meye ɗan uwanka ne you can’t change that fact, and you were suppose to sympathize with him during that period, amma yace min baka taɓa kiran sa ba tun bayan faruwan abun which is very bad of you, yana da wani ɗan uwan ne da zai tsaya masa bayan kai?” MD zai yi magana sai ga Maheer ya karaso Reception din, tafiya Maheer yayi gun Musharraf dake zaune yayi kamar baya jin discussion din Mami da yayan nasa, ya mike yana kallon Maheer ya basa hannu, Mami tace “Ina jin yayan nata ne wannan” MD dai ya dinga kallon Maheer a bit confused, Maheer ya karasa gun su bayan Musharraf yace masa tare suke da Mamin sa, Gaisheta yayi da ladabi Mami ta amsa masa, da damuwa ta kara da cewa “Ya me jikin?” Maheer yace “Alhamdulillah da sauki, mu karasa ciki” Mami ta kalli MD da gaba daya kansa ya ƙulle sai bin su yake da kallo with confusion, tace “Bari mu je….” Daga haka Maheer yayi leading dinsu zuwa ward din da Mayraah take, MD ya bi su da kallo still confuse, can dai ya bi bayansu shi ma da sauri, Maheer na shigowa ward din Mayraah ta dinga kallon Musharraf dake bayansa bata ko kiftawa, a hankali ta mike zaune har sannan kuma bata daina kallonsa ba kamar yanda shi ma yake kallon ta, MD dai na tsaye bakin kofar bai karasa ciki ba, anya ma ya taɓa zama confuse haka a rayuwarsa banda ranan da ya kawo Mayraah asibiti, Mikewa Ammi tayi ganin Mami ta fara welcoming dinta da fara’a, Mami ta karaso cikin dakin Ammi ta ajiye mata kujera tana mata sannu da zuwa, Mami sai da ta fara gaida Mama Ladi da tayi bake bake kan kujera, Mama Ladi na kallonta daga sama har kasa tace “Sannun ku da zuwa… Ai kun ma ci sa’a da aka barku ku ka shigo don lokacin ziyaran marasa lafiya ya wuce, duk da dai sun san wa enda suke raina ma hankali” Mami na murmushi tace “Ai kam da kyar suka bar mu Mama, ya me jiki?” Mama Ladi tace “Aa Alhamdulillah jiki yayi sauki, gashi har tana tashi zaune da kanta duk da maganar tata har yanzu sai an kasa kunne ake ji, da yake asibitin me tsada ne sun san kan aikinsu da karamin asibiti ne da yanzu gaisuwa ku ka zo ba dubiya ba” Mami tace “Gaskiya kam, Allah Ubangiji ya kara mata lafiya ya sa kaffara ne, Allah ya tsare gaba” Daga haka Mami ta karasa gun Ammi dake kallonta, da fara’a suka kara gaisawa Ammi na nuna mata kujera tace “Ki zauna Hajiya” Mami na murmushi tace “To nagode” Sai da ta fara karasawa kusa da gadon dakin tana kallon Mayraah cike da tausayinta tace “Sannu kin ji Mayraah, ya jikin?” A hankali Mayraah ta gaisheta, Mami ta amsa tace “Ya karfin jikin?” Mayraah ta gyada mata kai tace “Da sauki” Kallonta kawai Mami da ta dafa gadon take, don bata taɓa ganinta ba sai yau, ita dai Mayraah kanta na kasa, Mami kam bata fasa kallonta ba, Ammi ta amsa gaisuwar Musharraf da murmushi fuskarta tace “Ya hanya Musharraf?” Da ladabi yace “Alhamdulillah Ammi, ya me jiki?” Ammi tace “Jiki Alhamdulillah da sauki” Usman ya mike ya gaida Mami, sannan suka gaisa da Musharraf ya fita ward din, Umar ma ya gaishesu daga inda yake zaune, Musharraf ya karasa kusa da gadon yana kallon Mayraah dake kallonsa ita ma, Mami ta zauna kujeran da Ammi ta ajiye mata, Musharraf ya sauke wani ajiyar zuciya yayi kasa da murya yace “Ya jikin?” Ta sunkuyar da idonta ta kasa cewa komai, nan da nan hawaye ya kawo mata, shi ma ya sauke idonsa kasa, Ammi ta nufi MD da ta gani tsaye bakin kofa ya kasa shigowa, tayi kasa da murya tace “Don Allah ku yi hakuri Dr nasan ba haka ka’idar asibitin yake ba, amma su daga kano suke ne, in dubata zaka yi ka shigo kawai sai mu mu fita tunda su baki ne” MD ya sauke idonsa ƙasa ya kasa ce mata komai, Ammi ta koma cikin dakin zata ce ma Mama Ladi da Umar su ɗan fita su je reception, Sai a sannan Mami ta lura da MD a bakin kofa, tace “Oh ashe ka biyo mu Daddy” Bai ce komai ba ya karasa ciki, Mami na kallon Ammi tace “He is my son, he is working here” Da sauri Mayraah ta daga kai tana kallon MD kamar yanda Maheer har ma da Ammi ke kallonsa da mugun mamaki, MD ya sauke idonsa, Sai a sannan Ammi ta lura da mugun kaman da suke, ta ja kujera ta zauna da mamaki tana kallon Mami tace “Don Allah fa?” Murmushi kawai Mami tayi, Ammi na jinjina kai tace “Ji wani ikon Allah kuma” Mayraah dai ta kasa daina kallon MD babu ko kiftawa zuciyarta na wani irin bugawa, MD ya daga kai ya kalleta, da sauri ta sunkuyar da kai, ya juya ya fita daga ward din, Musharraf ya bi sa da kallo, Ammi da ta kasa daina mamaki tace “Allah me iko, ai kam ya mana kirki sosai, tun da aka kwantar da mu yake tsaye kan mu, always making sure she is better….” Musharraf ya maida dubansa kan Mayraah da jikinta yayi sanyi sosai ga tunani kala kala dake yawo a ranta infact ta ma rasa wani irin tunani zata yi, yayi kasa da murya yace “Ya jikin?” Ta gyada masa kai amma ta kasa cewa komai don duk a daburce take, a hankali Musharraf yace “Pls say something” Tayi karfin halin cewa “Alhamdulillah” Bai iya ya sake ce mata komai ba saboda yasan duk kallonsu ake a dakin barin Mama Ladi dake ta kallonsa tana kokarin tuna inda ta taɓa ganinsa. MD na komawa office dinsa ya zauna kan office chair dinsa ya tallabi chin dinsa looking so confuse zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri, at the same time he was trying so hard to understand something, to a ina su Mami suka san Mayraah da family dinta kenan? Or are they family frnds? Kawai sai yayi convincing kansa da hakan wato they are just family frnds shine dai bai san da haka ba, ya kai minti sha biyar a yanda yake wayarsa da ke kan table ya fara vibrate ya sauke idonsa kan screen din a hankali ya ga Mami ce ke kiransa, dagawa yayi ya kai kunne murya can kasa yace “Mami” Tace “Na fito ward din yanzu, kana ina?” Ya sauke idonsa yace “Ina office, ai kin san office din Mami” Tace “Ohk gani nan zuwa” Mami ta kalli Musharraf da ya zauna reception don allura za ayi ma Mayraah shine yasa suka fito daga ward din har Mama Ladi da tace kora da hali kawai ake masu meye kuma za a ce su fita don za ayi mata allura kamar wasu bare, Mami tayi kasa da murya tace “Mu je office din Daddy Musharraf” Musharraf ya kalleta yace “Ki je ni zan jira a nan Mami” Mami tace “Saboda me? Wai kana da wani ɗan uwa da yafi Daddy ne a duniyar nan, me yasa ku ke haka Musharraf?” Shiru yayi bai ce komai ba, ganin yanda take kallonsa sai kuma ya mike, ta fara tafiya yana biye da ita har suka haura sama zuwa office din MD, Mami ta ɗan yi knocking kofar sannan ta bude ta shiga ciki Musharraf ma ya shiga, kallonsu kawai MD yake har suka karaso ciki sannan ya mike, Mami ta zauna kan kujera tace “Ka rage Ac din nan don Allah” Musharraf ya zauna ya dau remote din AC din dake kan karamin table dake gaban sofa din da suka zauna ya rage karfin AC din ya mayar da remote ya ajiye, MD ya nufi fridge dinsa ya bude ya dauko masu can drink biyu da goran ruwa biyu ya karasa ya ajiye kan table din, Mami tace “Kwanansu nawa kenan a asibitin yau?” MD ya tafi ya jingina da table din office din ya rungume hannunsa yana kallon Mami yace “Sati daya, amma a ina kika san su Mami? Ko family friends?” Mami tace “Wani family friends kuma? Ita ce fa yarinyar da Musharraf ya nema da aure aka fasa” Sai da MD ya dafa table din bayansa da sauri tsabar yanda zuciyarsa ya buga, Mami na kallonsa da mamaki tace “Are you okay?” Shi dai Musharraf idonsa na kan TV dake kunne a office din duk da yana sauraron conversation dinsu, MD ya dago da sauri yana girgiza kai ganin Mami ta mike yace “I’m fine Mami, just that tun safe muke wani aiki ne, i am exhausted…” Mami da ta tsaya tana kallonsa tace “To ko dai kwanciya zaka yi” Ya girgiza kai da sauri ya zauna kan kujeran dake kusa da shi ya jinginar da kansa jikin kujeran yace “I will be fine, it’s just stress” Mami ta koma ta zauna tace “Sannu….” Sai a sannan Musharraf ya juya ya kallesa, Mami na kallon MD tace “I heard she was poisoned?” Gyada kai kawai MD yayi bai iya yace komai ba, Mami tace “Allah sarki, yarinyar nan na ganin jarabawa iri iri” Sai kuma da mamaki Mami tace “Wait… Amma ai da kai aka kai kudin auren nata Daddy ko ka manta ne? Ai zaka gane yayyinta maza da ma Abban nata….” Girgiza kai kawai MD that was speechless and confuse yayi yana kallon Mami amma ya ma kasa magana, Mami bata sake ce masa komai ba cause she can see he is tired don taga hakan a idonsa, bayan few seconds ya lumshe ido kansa na jingine da kujera zuciyarsa na ci gaba da bugawa, Musharraf ya dau can drink din gabansa ya bude ya fara sha, Mami kuma ta dau bottle water ta bude, Lkci daya MD ya bude ido bayan kusan minti biyu jin wayarsa na vibrate, yana dubawa ya ga Ceo ce ke kiransa, gaba daya yaji kamar an zare masa laka ne a jikinsa, Musharraf ya mike bayan ya kusa shanye drink din Mami na kallonsa tace “Zaka koma ward din ne?” Yace “I want to get something for her outside first” Mami tace “Ohk, amma kasan Flight dina na komawa Kano bayan magrib ne zaka yi using motar Daddy kayi dropping dina airport nan da minti talatin” Musharraf yace “Toh” Kallon MD da ke ta kallon kiran ceo yayi, gaba daya he is absentminded don hankalinsa ma baya kan kiran kawai kallon screen din yake babu ko kiftawa tunaninsa na wani wajen daban, Musharraf ya karasa kusa da shi yace “Zan yi amfani da motar ka” Sae a nan MD ya dawo duniyar tunanin da ya tafi ya daga kai da sauri ya kallesa, sai kuma ya daga kiran Ceo kafin ya katse, sanar masa tayi ta shigo asibitin tana office he should meet her, bayan sun gama magana MD ya katse wayar ya dauko makullin motarsa ya mika ma Musharraf ba tare da ya kallesa ba, Musharraf ya amsa ya nufi kofa, Mami dake ta kallon MD tace “Daddy are you sure you’re okay?” Ya mike da sauri yana feigning smile yace “Mami na gaji ne fa, bari in je our Ceo is around ita ta kirani yanzu” Mami tace “Ohk” Yana tafiya a hankali ya fita daga office din. Har ya isa Office din Ceo hankalinsa baya jikinsa, ya sameta tana waya, ya sunkuyar da kai ya jira har ta gama, sannan yayi mata sannu da zuwa da ladabi, ta ajiye wayar hannunta tana kallonsa daga sama har kasa tace “Are you okay?” Ya gyada kai yana kirkiran murmushi yace “Sure Ma’am” Takarda ta dauka kan table dinta tayi rubuce rubuce sannan ta mika amsa tace “Magunguna da alluran da za a canza ma Mary Ann kenan, it should start from tomorrow morning pls” Ya amsa yace “Ok Ma’am” Tana kallonsa, bayan few seconds tace “You said the result will be ready today Aliyu” Yace “Sure Ma’am it’s out, yana office dina ma…” Shiru tayi tana kallonsa, shi dai yana tsaye yana jiran next instruction da zata bada, Ajiye pen din hannunta tayi a hankali tace “Bring it to me” Yace “Alright Ma” Daga haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita. MD na komawa office dinsa ya zauna with confusion yana kallon Mami, calmly yace “But Mami ita wannan ai da iyayenta fa, har ma da yayyinta maza, warcen kuma ba cewa aka yi bata da iyaye bata da asali ba? Sannan ita wannan a nan Abuja suke zama….” Mami da ta ma rasa abinda zata ce masa tayi shiru tana kallonsa as if wanting to figure out something, ya girgiza kai yace “Gaskiya ina jin ko kamanni ne, ko kuma, kawai dai ba yarinyar bace…..” He just realized he sounds stupid and he is not making any sense, ya kara girgiza kai ya mike ya dau envelope din result din genetic testing din da Ceo ta bada ayi, kofa ya nufa Mami ta bi sa da kallon mamaki har ya fita, yana komawa office din Ceo ya ajiye mata envelope din saman table yace “Here is it Ma’am” Kallon envelope din kawai Ceo take, yace “Is there anything again Ma’am?” A hankali tace “Just wait” Yace “Ohk Ma” Gefe ya koma ya tsaya, ta dau envelope din tayi unsealing dinsa gently ta ciro result din ciki, Shi dai MD kallonta kawai yake, Glasses dinta ta dauka ta saka sannan ta warware takardun tana dubawa, MD wondered why she was this nervous checking the result, ko da yake tace family issue ne, mikewa yaga tayi da sauri ta dafe table dinta, MD ya karaso da sauri kusa da table din yace “Is everything okay Ma’am?” Sai kuma yaga hawaye na sauka idonta ta cire glasses din idonta da sauri tace “I need privacy pls Aliyu” Yana kallonta yace “Alright Ma, take care pls” Daga haka ya nufi kofa yana waigota ya ga ta nufi dakin dake office din, shi dai ya fita ya kulle kofar, jingina yayi da bango ya lumshe ido zuciyarsa na wani irin bugawa, da kyar ya iya jan kafa ya bar wajen ya koma office dinsa, yana shiga office din Mami ta mike tace “Kar nayi missing Flight dina Daddy” a hankali yace “Okay Mami, Musharraf din ya dawo ne” Tace “Eh yana waje, mu je in fara masu sallama tukunna” Bai iya yace mata komai ba, suka koma ward din da Mayraah take, Mami ta karasa kusa da gadon Mayraah tace “Allah ya sauke Mayraah” Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, kallonta MD yake babu ko kiftawa, Mami ta ciro 50k a jakarta ta ajiye gefen Mayraah tace “A siya maki fruits” Ammi tace “Har da dawainiya Hajiya, zuwan kadai ma ai ya wadatar wallahi” Mama Ladi ta kalli Ammi da sauri tace “Kul, ba a maida hannun kyauta baya, godiya kawai za kiyi mata kice Allah ya kara arziki haka ake yi” Murmushi kawai Mami ke yi tace “Lallai kam Mama gwara dai da kika gaya mata” Cikin sanyin murya Ammi tace “To Allah ya saka da alkhairi Hajiya, mun gode kwarai da gaske, Allah ya bar zumunci” Mami tace “Ameen ya Allah, ita kuma Allah ya bata lafiya ya tsare gaba” Ammi tace “Ameen” Mayraah ta ɗan daga kai ta kalli MD da bai fasa kallonta ba suka hada ido, kauda kanta tayi da sauri, Ammi da Mama Ladi suka fita raka Mami, Usman dai sai kallon MD dake kallon Mayraah yake.
Masha allah , allah yakara basira